Sunday 9 April 2017

KHALEEL Page 81&82

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥

        PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
                  (P.M.L)

               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com



              PAGE


✍🏻✍🏻81&82✍🏻✍🏻


Last ChapterπŸ™ŒπŸ» In dedication to each and every readerπŸ‘„πŸ’…πŸ»


Two years later!


Hanifah ta kammala karatunta lafiya ta fito da first class upper! Hakan yasa Khaleel ya bata surprise na zuwa L'A (Los Angeles) murna a wurin Hanifah ba'a magana.
Gaba d'aya suka shirya harda Adnan suka tafi, sunyi enjoying rayuwansu sosai sai da sukayi sati biyu suka dawo gida.
Bayan sati ukku kuma Khaleel ya shirya musu zuwa Saudia gaba d'aya harda Ammi dasu Saif. Haka kuma suka d'unguma suka tafi Makka.


Bayan sun dawo life moved on yanzu Adnan har ya shekara biyu yana gudunsa ba inda baya zuwa, ga rashin ji sai dai Hanifah bata wasa da tarbiyansa ko kad'an, zuwa yanzu har karatun qur'ani take koya masa kuma yana yi sosai, don ko hakanan zasuji yana karantowa idan yana hidimansa cikin gida ko yana wasa, hakan ba k'aramin dad'i yake musu ba.
Yana shekara uku aka sanya sa school kuma ba laifi yana k'okari.


*****

Hanifah na kwance bata da lafiya sosai Khaleel ya matsa mata suka je asibiti harda Adnan, bayan sun ga doctor aka tabbatar mata tana daga ciki na wata biyu. Murna a wajen Khaleel ba'a magana, d'aukarta yayi yana juyi da ita cikin asibitin tana ta dariya. Haka suka fito suna ta murna a bakin k'ofa suka kusa cin karo da mutum, Hanifah ta d'ago da mamaki tana kallonta, idanu ta ware tana son gano inda ta santa, matar ta fara magana tace
"Hanifah ce?"
Hanifah ta kalle ta tana d'auke da wata yarinya y'ar wata bakwai, Hanifah tace
"Eh."
Matar tace
"Humaira ce."
Da mamaki Hanifah tace
"Humaira kece?"
Humaira tayi murmushin yak'e tace
"Nice Hanifah! Na zo kwanaki gidanki bakya nan dama gafaranki nazo nema naga rayuwa, kuma dama ance duk wanda baibi duniya a sannu ba zata koya masa hankali, nidai na tuba, ki yafe min abinda nayi miki, nayi nadama ki yafe min."
Hanifah ta dafa ta.
"Kar ki damu Humaira ni dama na dad'e da yafe miki Allah ya yafe mana gaba d'aya."
Humaira ta rungumo ta tana kukan farin ciki. Tace
"Allah ya kaddara min aure bayan abinda ya faru ga mijina nan ku gaisa."
Cike razana Hanifah tayi baya baki bud'e tace
"Wannan ne mijinki? Kinsan ko waye kuwa? Deen ne fa! Khaleel kalli Deen!"
Khaleel ya rik'o ta yana fad'in
"Calm down my princess, kibi a sannu kinga bake kad'ai bace."
Ta samu ta nutsu inda Deen ya fara k'ok'arin durk'usawa k'asa yace
"Nasan ban kyauta maku ba, bani da bakin da zan rok'e ku gafara, just find it somewhere in your heart to forgive me, na rok'e ku."
Khaleel ya d'ago sa a hankali had'e da dafa sa yace
"Allah ma muna masa laifi ya yafe mana bare mu mutane? Ay indai mutum yayi kuskure kuma ya gane kuskurensa meyasa baza'ayi masa uzuri ba? Wallahi kar ka damu na dad'e da yafe maka Allah ya yafe mana gaba d'aya."
Harda d'an guntun k'wallansa yace
"Nagode muku! Allah ya saka da khairan."
Ya fad'a yana kallon Adnan yace
"Little man meye sunanka?."
Adnan yace
"Ma ismuka ake cewa."
Deen yayi murmushi yace
"Sorry ma ismuka?"
Adnan yace
"Ismi Abdul'aziz."
Deen yace
"Nice name Allah ya maka albarka."
Yace
"Amin."
Nan sukayi musabaha da exchanging numbers Khaleel yace
"Mu zamu wuce sai anjimanku, sai munyi magana."
Deen yace
"Mun gode k'warai Allah ya saka da khairan."
Adnan ya kwasa a guje yace
"Daddy kamo ni."
Khaleel ya k'yalk'yale da dariya yace
"Ok."
Take ya bishi a guje a yayinda Adnan ya ruga yana dariya, Hanifah tasa dariya sosai inda ta bisu da sauri tana dariyar itama.
Can ta hango Khaleel ya d'aga Adnan sama suna k'yalk'yatar dariya, Hanifah na zuwa ta rungumo su ta baya Khaleel ya kamo ta yace
"Come here Maman biyu."
Ta zum6uro baki.
"Ni ba Maman Biyu bace d'aya dai."
Khaleel yace
"Kin ma isa? Ay biyun nan zaki haifa insha Allah."
Tace
"Ni a'a."
Ya jawo karan hancinta yace
"Zamu gani ay."
Adnan ya shige mota da gudu inda Khaleel ya kamo Hanifah tana bisa kafad'arsa, haka suka tako har bakin k'ofa kafin Khaleel yaja ya tsaya yana kallonta cike da so! Yace
"Allah ya barmu tare har aljanna my princess."
Tayi murmushin jin dad'i tare da hugging d'insa sosai tace.
"Amin my only I love you."
Yace
"Love you more and more."
Tace
"More and more and more."
Dariyar Adnan suka ji suna juyawa suka ga yana lek'ensu ta window yana ganin sun kalleshi ya rufe fuskanshi yana dariya, yace da k'arfi
"I love you Mummy and Daddy!"
Da k'arfi suka ce
"We love you too Adnan.!"
Suka sa dariya gaba d'aya cike da farin ciki....



           

               Alhamdulillah!


Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah (S.W.A) da ya bani ikon kammala littafina mai suna Khaleel lafiya!
Alhamdulillah....

Toh nidai a nan na kawo k'arshen book d'ina mai suna KHALEEL! Kuskuren da  ke ciki Allah ya yafe min, darasin da ke ciki Allah ya bamu ikon d'auka.
Ina mik'a sak'on godiya ta ga dukkan masoyana Nagode da k'aunarku a gareni.😊

Ina mik'a sak'on ta'azziyata ga friend d'ina Asma'u data rasa d'anta jariri Allah ya jik'ansa yasa mai ceto ne Amin!πŸ˜’

Godiya ta mussaman ga....

*Pure moment of life writers
*Hausa Novels na (Fatima Mansur), (Raff) and my (Chuchu)
*Lovely fans
*Rash kardam novels
*Dandalin Meesha lurv
*Talented writers group
*Khaleesat Haiydar novels
*Mu Sha Karatu

Kuna raina dukkan masoyana da wanda na sani da wanda bansani ba kuna raina! ❤️

Litattafan marubuciyar~~

1) Komin nisan dare
2)HAIFAH
3) TAGWAYE NE?
4)KHALEEL

Don Allah ina cigiyar book d'ina KOMIN NISAN DARE daga farko har k'arshe mai shi ta taimaka ta turo min shi. 😘

ALLAH ya sadamu da alkhairi! Taku har kullum mai kaunarku

MARYAM S BELLO (MSB)πŸ‘„πŸ’…πŸ»❤️

No comments: