Thursday 5 September 2019

RAYUWAR HOSTEL PAGE 32 {END}

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

*we don't just entertain and educate,we touch d hearts of d readers*

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*page 32 by*
*mmn khadijahπŸ’…*

πŸ”š

Haka dr Maheer ya fito a gidan cikin farin ciki,be tsaya wani b'ata lokaciba yana isa mota ya kira sanyin idonshi zulaihat ya fad'a mata duk yadda sukayi da hajiyarshi,ita hakan yayi mata dad'i matuk'a ahaka sukayi sallama ya kashe waya.ita kuwa taci gaba da shiri
dan zata fita karatu saboda lokacin exams ya gabato.

*AFTER 3 DAYS*
Daga wanka ta fito tana shafa,wayarta ce ta fara ringing,da sauri ta d'aga "hello k'awata please kiyi sauri ki shigo ya kusa isowa,kuma kinsan babyn nawa bayason jira.shiru tayi na d'an lokaci da alamun tana sauraron maganar wancan b'agaren ne,"owk toh sai kin k'araso".

Ba'a fi five minute ba sai ga Halima ta iso tare da dr,da alamun a hanya ya ganta suka taho tare.

Ba wata kwalliya tayi sosai ba,light makeup tayi,amma ba k'aramin kyau tayiba,swiss lace tasa orange da kwalliyar sky blue,d'inkin riga da skirt,hijabi tasa sky blue, takalminta orange da dan blue a jiki,ta rataya jaka suwaga sky blue,wash gaskiya ba k'aramin kyau zulaihat tayiba,suna fita dr Maheer yayi tozali da sahibarsa baisan sanda kalman "fatabarakallahu ahsanul khaliqeen"ta fito a bakinshiba,kallanta ya dingayi har suka k'araso,cike da soyayya da kaunar juna suke aikawa junansu sak'o.

______________
Ba k'aramin karb'a gidansu dr Maheer sukayima su zulaihat ba,kowa a gidan yana haba-haba dasu,abinci da drinks ba'a magana,sun dan jima a gidan ba laifi,sannan suka tafi,wata babban leda hajiyar dr Maheer ta bata,Wanda kayan kwalliyane da tiramen atanfa masu tsada guda uku,babansuma ba'a barshi a bayaba kud'i ya basu 10k,yanayin tarbiyyan gidansu dr ba k'aramin birge zulaihat yayi ba,dan haka taji ta k'ara kaunarshi sosai a ranta.

Ad'aki suke zaune banda hirar gidansu dr Maheer ba abinda sukeyi,wayar zulaihat ce ta fara ringing,ras taji gabanta ya yanke ganin sunan dake d'auke ajikin screen d'in wayar,d'agawa tayi tare da yin sallama.
"ke zulaihat duk abinda kikeyi ki bari gobe kizo gida,ana gama fad'in haka aka kashe wayar batare da an bari tayi magana ba.

"Innalillahi wa innailaihi rajiun ta fad'a tare da cire wayar a kunnenta"
"k'awata lapiya naga yanayinki ya canza?.
Ajiyar numfashi zulaihat tayi sannan tace."yayana ne ya kirani wai inje gida,daga yanayin furucinshi nasan babu lapiya.
"insha Allahu ba wata matsala k'awata,ki kwantar da hankalinki.

Da tunani iri-iri a ranta ta kwanta,dan haka da sassafe tayi shiri sai gida.

Tana isa tayi arba da Ruky zaune tayi baja-baja,tunda ta ganta jikinta yayi sanyi tasan tabbas ba alkhairi bane ya kawo ta,zama tayi ta gaida mutan gidan kowa da kyar ya amsa mata,itako Ruky sai yatsina takeyi tana wani babbasarwa.

Yayan zulaihat ne ya fara magana cikin fushi,duk abinda Ruky ta fad'a musu ya zayyanowa zulaaihat tabd'i lallai Ruky  ba k'aramar shedaniya bace had'ata tayi sosai da iyayenta dan kusan duk maganganun karyane,haka yacigaba da fad'a kamar zai ari baki,itadai zulaihat banda kuka ba abinda takeyi dan gaba d'aya bata da tacewa.

Saida ya gama tsaf sannan yace nagama yanke hukunci akanki daga rana mai kamar tayau kin gama makarantan,na dakatar dake kamar yadda aka kori wannan baiwar Allah,wani dadi Ruky taji a ranta dama kuma muradinta kenan yanzu burinta ya cika.

Harya tashi zai fita zulaihat tace "yayana inada magana"komawa yayi ya zauna yace "fad'i maganarki ina sauraro".

"banzanyi gardama ko jayayya akan duk hukuncin daka yanke akainaba,saboda kai kamar mahaifine a gurina,kuma nasan bazaka yi duk abinda zaka cutar daniba.akan duk abinda Rukayya ta fad'a wannan ba halinabane kuna wallahi ba gaskiya bane, dan tabbatar da maganata gaskiyane ga numbern dr Maheer ka kira nasan zai fad'a maka komai akaina.

Ruky ce tayi caraf"eh abokin munafurcin nakiba,yaya karka yarda da wannan zancen nata,wallahi duk k'anzan kuregene".
Yaya be kula zancen Ruky ba ya karb'i numbern dr atake ya kira yayi masa bayani,dr "yace su jira yana zuwa.

Ba'a dauki lokaci mai yawaba dr Maheer ya iso gidan, nan ya fayyace ma yayanta komai akan su Ruky da sauran yan k'ungiyarsu,sannan yayi masa bayani akan yanason zulaihat da aure anan suka tsara komai.
Bayan tafiyar dr yaya yayima Ruky ta tas,sannan ya mata korar kare wanda saida ta gwammace da batazobama.

Haka alamari yaci gaba da tafiya maganar auren dr da Zulaihat tayi karfi inda aka sa ranar aurensu,nan shirye- shirye ya keta kankama.

Rana bata k'arya saidai uwar d'iya taji kunya,ayau aka daura auren dr Maheer da amaryarsa Zulaihat inda akasha hidima,an kece raini,amarya tayi matuk'ar kyau kamar ka saceta ka gudu😜,dare nayi aka kai amarya d'akinta.toh sai muce dr Maheer da Zulaihat Allah ya kawo kazantar d'aki amma bata dattiba.

*Tammat bi hamdullah*
Saimun had'u a littafinmu na gaba.

*Tsokaci*
_wannan labari na rayuwar hostel akwai abin lura aciki,munga dai yadda rayuwar zulaihat ta kasance,tafito daga gidan tarbiyya karshe ta hadu da frirnds wanda suka lalata mata rayuwa,kunga inda daga baya ta tsinci kanta cikin tashin haknkali,akwai mata da yawa wanda hakan take faruwa dasu ko kuma makamancin hakan,toh mu sani kasancewarki a hostel bashi ke baki freedom nayin duk abinda kikaga damaba,hausawa sunce kowani tsuntsu kukan gidansu yakeyi,duk yadda kike haka zaa dauki tarbiyyar gidanku dan haka yan mata da matan aure ya kamata mu fad'aka mu gane,Allah yasa mu dace amin_

Godiya ta musamman ga

Rayuwar hostel fans
Pure moment of life
Mmn khady fans nvl 1and 2
Sarauniyar mace
Mmn humaira novels
Ummyn yusra novrls 1and 2

UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀

Wednesday 4 September 2019

RAYUWAR HOSTEL PAGE 31

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
  {We don't just entertain and educate we touch the heart of readers}

      P.M.L

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page 31 by
  Jannart lameed'o
  {Babyn garkuwa}

      It's too droop b'cos true love happens once in life my FANSπŸ˜»πŸ‘Œ

     *w*ashagari Zulaihat ta had'a koman tah, karfe 8 na safe ta gama shirin tah Dr Maheer kawai take ji yazo,
      Karfe 8:15 yah iso k'ofar gidan, kiranta yayi awaya tare da sheda mata yah iso, batawani b'ata lokaci ba ta fito,
    Sanye take da pink d'in riga dogo  tare da pink d'in hajibi shima Amman mai hannu tayi kyau sosai,
   Yayi da Dr Maheer ke sanye da pink d'in shadda mai aiki fari a jikin sah, kansa yasha farin hula hatta agogon hannun sa fari ce yayi kyau sosai,
     Kana ganinsa kaga d'an matashi maiji da kyau, ilimi, da nasaba, sai sheki yake,
      Tafiya take kaman tana tsoran kasa , cike da yanga, harta iso wajan Dr Maheer baisan ta iso bah saida ta isa kusa dashi tare da hure masa ido, cikin ajiyan xuciya ya dawo hankalin sah,.

    "Lafiya my soul ka wani kafeni da ido sai kace baka sanni bah?"

   Murmushi yayi, yana kare mata kallo yadda tayi wani kyau yau kaman ba itah bah.

     "My baby kece kullum cikin rud'ani kaman bake ba, kinga wani irin kyau da kikayi yau kuwa? Kaman in gudu dake nayi ta kallon ki"

    Fari tayi da idanun ta , tare da rausayar da kanta gefe,

     "My soul kenan ae duk kyau na ban kaika bah,ni har tsoro nike kar wata ta kwace mun kai muddin kana fita cikin wannan kwalliya"

    Ta karashe maganan cikin shagwa6a, da kuma kishi ganin yadda yayi wani kyau yau, she kawai ta ji gaban ta na fad'uwa,

    "Haba my sweetheart ke kanki kinsan Zulaihat ta Maheer ce haka Maheer na Zulaihat ce komin wuya komain tsanani muna tare dake,  babu abunda zai raba Zulaihat da Maheer d'in ta sai mutuwa,

      Dariya suka sake tare dukkan su kowa najin son d'aya cikin ransa.
   Sun juma suna hira kafin ya bud'e mata motan tashiga,
    Tasha ya kaita kaman karsu rabu haka suke ji, saida ya tabbatar motan tasu ya tashi kafin ya tafi cike da kewar sahibarsa,

   Zulaihat na isa gida, gida ya kaure da murnah kowa sai murnan ganin ta yake, bayan taci abinci ta huta ne , take sanar da Ummah tata abunda ya kawo to,
  Ummah ta nuna jin dad'in ta sosai tare da saka musu  albarka, yayun ta suna dawowa Ummah ta sheda Musu ,suma sunnu na jin dad'in su sosai,

******************
Bangaran su Rukky kuwa suna kulle cikin makaranta ko bari aje wajan su ba ayi,
   Tunda aka kulle su babu mai cewa komai kowa da tunanin da yake cikin ransa,
    Rukky ce ta fara magana cikin tashin hankali,

   "Wallahi KB kei ne ka jefamu cikin wannan rayuwa, kei ne ka lalata min rayuwa na, ka mai dani tamkar akuya, Allah ya isa KB, yanzo idan Dady d'ina yazo wajan nan nagama kad'ewa"
   Tsawa KB ya daka mata yana huci kaman zakin da ya kwana bai ci bah,
   
      "Ke malama saurara, nine na kawo ki yadda nake? Ko kuma na miki dole ne? Daman can da gutun iskanci ki, kikazo cikin school d'in nan dan haka karki d'aga mana hankali"
   Dubansu Eysha tayi d'aya bayan d'aya, idon ta ya kad'a yayi jah kaman garwashi sai huci take,

     "KB ,Jibson, kun cuce rayuwa ta wallahi kun barmun abun fad'i cikin al'umma, tun farko naki harkan nan , Amman saida kukasan yadda kukayi nashiga cikin ku ,Allah sai ya sakamin wallahi"
 
     Sai yanzo Jibson yasamu daman magana,

    "Da Allah Ku fura wa mutane baki, zamuji da Wanda muke ciki ne ko kuma da mitan Ku, banzaye ja kuna kawai"

     Haba nan da nan Rukky ta haure sarkin rashin hakuri,

     "Malam waye banzaye? kaji d'an akuwa mai cin duk dusan da ya gani batare da tsaya tattacewa bah"

    "Ke Dan ubanki nine Dan akuyan?"

     "A nafadi maka ko kanada abunda zakayi ne?"
 
    Ae bata gama magana ba ya d'auke ta da wani mari Wanda hakan ya tilassa mata dafe wajan,
   Daga ido tayi batare da wani tsoro bah ta tsinke Jibson da wani mariiiiiiii,

    "An fad'i d'an akuya"

Zuciya ne ta taso ma Jibson nan take ya fara dukan Rukky baji ba gani yana kuma takata da kafarsa, itama Rukky ramawa take,
   Ganin haka yasaka Eysha fara zagin KB akan yara basu, shuru ya mata shima ganin yaki kulata yasa ta cire takalmin kafarta ta kwad'a mishi,
     Cikin zuciya yayi kanta da duka,
     Fad'a ne ya kaure tsakanin su babu abunda ke tashi sai karan duka,
     Kowah na  zagi d'aya cike da jin haushin junan, kafin zuwa wani lokaci sunyi wa junan su jina_jina kaman Wanda aka saura musu halitta lokaci d'aya,

    Ganin haka yasa muka kulle musu kofar mukayo waje.........................

UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 30

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

-We don't just entertain and educate, we touch the heart of readers_

      P.M.L

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page 30 by
Maryam Sbello

Da k'yar su KB suka lalla6a suka mik'e daga wurin ko ina a jikinsu ciwo yake, Ruky in banda gunjin kuka ba abinda takeyi, shi kuwa KB ba zafin dukan kad'ai ya 6ata masa rai ba harda yanda mutane ke kallonsu wai harda Allah k'ara ake musu. Banda kunya data ishe su wai ace kamar su big boys da ake  ji da su a makaranta wai yau su aka ma haka?

A inda suka saba zama meeting nan suka wuce kansu tsaye, kallo d'aya zakayi masu ka tabbatar da suna cikin 6acin rai ba kad'an ba, KB ya dafe gefen bakinsa inda ke zubar da jini ga azabar zafi ya bugi table d'in da ke gabansa cike da 6acin rai.

"Lallai gayen nan ya nuna mana iyakar mu yau, ace kamar mu, *Untouchables* wai yau mu aka ma haka a makarantar nan? Lallai da sake."
Ya k'arasa yana nuna kansa gami da fuzar da iskan huci daga bakinsa.

Jibson ya d'ago ya kalleshi yace
"Ay gaskiya mutumin nan ashe haka yake? Duk warning d'in da muka buga masa da tsoratar dashi da mukayi duk bai gani ba ashe? Bamu ta6a zama defeated ba a school sai yau, duk abinda muka sa gaba sai mun same shi, amma ace wai saboda Zooly kad'ai mun gagara cimma burinmu? Nooo!"

Ya fad'a yana huci sosai, ga 6acin rai da yake ciki marar misaltuwa.

Shi kuwa Big boy bai ma iya magana saboda kansa zubar da jini kawai yakeyi.

Ruky ce ta daka musu tsawa tace

"Kai da Allah ya isa haka! Kun bani kunya sai cika baki amma baku iya ta6uka komai! Kalle ku da Allah rai d'aya ya maku wannan abin, amma kuma kunzo kuna mana ihu aka, to tunda kun kasa aikata komai sai kuyi mana shiru aikin banza kawai."

KB ya mik'e cike da 6acin rai yana nuna Ruky
"Ke yarinya! Kar ki nemi ki raina mana hankali fa a nan, in ba haka ba sai na miki abinda bazaki manta ba, ki barni naji da abinda ya dameni."

Ruky tayi shewa
"Idan nak'i fa me zaka iya yi? Besides Dr ma ya maka d'an banza duka..."

Rai a 6ace KB ke mata wani irin kallo yace
"Me zan iya yi kika ce? To ki jira ki gani mana!"

Nan sukayi ta chachar baki inda har KB ya wanke Ruky da mari cikin zafin nama, itama kuwa ta rama, daga nan fad'a ya kaure tsakaninsu, da sauri Jibson ya shigo don ganin ya raba su amma memakon haka sai aka had'a dashi. Cikin wannan hali Easha ta shigo, tayi tayi ta raba su amma abu ya ci tura.
Sai da suka gaji don kansu suka bari.

Ba'a fi minti biyar ba wani malami ya shigo inda suke sunyi lik'is!
Cike da 6acin rai yace duk su tashi su zo HOD na nemansu gaba d'ayansu, duk iskancinsu kuwa yau sai da suka ji tsoro.

Office d'insa suka shiga inda suka tarar da manyan malamai sunfi su biyar, gefe kuma Dr Maheer ne da Dr Khaleed, ko wanensu fuskarsa a d'aure kamar hadarin kaji.
Nan fa su *Untouchables* ido ya raina fata, HOD ne ya kallesu sannan kuma ya daka masu tsawa yace
"Don kun raina mutane baza ku duk'a ba kun mana tsaye aka! Get down on your knees now!"

Da sauri suka duk'a jiki a sanyaye, HOD ya cigaba da magana yace
"Daman abinda yake faruwa a cikin makarantar nan kenan bamuda masaniya, Saboda Allah a turo yara karatu amma su tsaya suna irin wannan? Malam Aminu? Malam Ibrahim? Malam Musa? Kuna sane wannan abin ke faruwa a cikin makaranta?"

"Muna sane kayi hak'uri, abin ne yafi k'arfin mu sheyasa, amma kayi hak'uri."

HOD yace
"Yafi k'arfinku? Har sun isa? Su waye su? Ba'a haife su ba wallahi. Inda Dr Maheer bai sanar da mu ba da shikenan sai abubuwa suyi ta faruwa bamu sani ba? Amma bakomai tunda yanzu an sani."

Ya kalle su cike da 6acin rai
"Kai! Naji labarin baku shiga lectures sai kunga dama? Ga lalata da iskanci da kuka sa a gaba, da zuwa club, baku aje komai ba sai lalata yaran mutane ko? Ga raini da isgilanci bakuda respect ko kad'an, yanzu har Dr Maheer kuka kama zaku daka, kuka farfasa masa mota saboda raini ko? Abinda kuka ga dama kukeyi ku ga tantairai masu ji da kansu? To baku isa ba wallahi, nace baku isa ba kunyi kad'an! Bazamu d'auki irin wannan ba, kuma bashi muke koyawa ba, don haka dole zamu d'auki mataki a kanku."

Ya kalli Malam Aminu yace
"A d'auko file d'insu ko wane a kira lambar iyayensa suzo makaranta, inaso a sanar masu bad'alar da sukeyi sannan mu sallame su su tafi can su k'arata! Bama buk'atar irinku a makantar nan."

Nan fa suka hau bada hak'uri HOD ya daka musu tsawa
"Ashe ma cikin 'yan iskan ku k'anana ne?
Ay kad'an kuka gani, duk abinda kuka aikata sai an sanar da iyayenku wallahi."

Don tsorata sun tsorata don kuwa sunsan muddin aka sako iyayensu a ciki to da matsala. Don haka suka soma bada hak'uri, amma ina HOD ma ko saurarensu baiyi ba ya fara k'ok'arin kiran layin iyayensu.

****

Tsaye yake ya hard'e hannayensa yana jiran fitowar Zulaihat don suyi sallama gobe zata je gida weekend. Sanye yake da jar riga mai ratsin fari da bak'i mai dogon hannu, sai bak'in wando, ba k'aramin kyau yayi ba, fuskarsa mak'ale cikin siririn farin glass wanda ya k'ara fiddo da cikar kamalarsa. Ba'a juma ba sahibarsa ta fito tana sanye da atamfa mai ja da bak'i sai ta d'ora doguwar bak'ar hijabi da ta kusa kai mata k'asa. Dad'i had'e da farin ciki suka dirar masa a zuciya, ba k'aramin burgesa tayi ba ganin yadda a kullum take saka hijabi sai yaji ya k'ara sonta sosai.

Tana k'arasowa ta sakar masa sansassanyar murmushi mai saurin sace zuciya take ya mayar mata.
"My soul..."
Ta fad'a cikin jin kunya ganin yadda ya tsare ta da manyan idanunsa, tayi murmushi. yace
"Ya kike?"
Tace
"Lafiya lau."
Yayi murmushi yace
"Yau dai nazo miki da albishir mai dad'in gaske?"
Tace
"Allah? Meyafaru?"
Nan ya kwashe labarin komai ya fad'a mata, ya d'ora da cewa
"Yanzu dai suna hannun makaranta, insha Allah k'arshen iskancinsu yazo kenan, you can live freely babu mai takura min ke."

Tace
"Alhamdululillah, gaskiya naji dad'i sosai, Allah ya biyaka, su kuma Allah ya shiryesu."
Yace
"Amin amin."
Tace
"Gobe ma zan je weekend gida insha Allah."
Yace
"Eyyah zanyi missing d'inki sosai, amma yana da kyau kije ki gaida iyayenki ay."

Tace
"Hakane."
Ya duba agogo tara saura yace
"Bari na barki ki shirya ki kuma kwanta da wuri, gobe zan zo na kaiki tasha."
Tace
"Da wace motar my soul? Kaida taka na wurin gyara."
Yace
"Dr Khaleed zai bani tasa kar ki damu."

Sun d'an juma suna fira kafin suyi sallama ji suke kamar kar su rabu da junansu...

UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 29




*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

*we dont just entertain and educate,we touch d hearts of readers*

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART Lameed'o*
*RUFAIDA YUSUF*

*Page 29*
      *By*
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ*

     Ba a fi 10 mins da yi mishi waya ba ya sake kiranta yace ta fito su tafi

      Haka suka dinga fito da kayan bakin hostel shi Kuma yana kaiwa mota har suka gama sai ta ce ya raka ta su karb'i phone d'inta a wajen Masu chaji Da yake a wayar Halima suka dinga communicating, ba musu suka tafi karb'i waya suna tafe suna hira abin su gwanin ban sha'awa

      Suna tafiya su Untouchables suka fito daga mab'oyar su don duka abinda ya faru akan idon su ne,suna zuwa suka yi raga-raga da glasses d'in motar gaba d'aya sannan suka sace masa tayoyi duka,suka d'ebo Datti mai yawa suka tura a cikin motar, sai kuma kit d'in Zulaiha suka FASA shi shima suka zazzage kayan da ke ciki,akwai wata jakar undies d'inta itama haka suka zazzage ta a wajen suka yi mata baja-baja da kaya,suka kuma tsaya a wajen suna jiran suga ta inda za a bi a fitar da ita daga school d'in

      Suna nan tsaye Big boy da Katon kulki a hannun sa inda k.b ke rik'e da katakon hockey sai kuma Eeshat da ke gefe tana tauna chewing gum kowanne daga cikin su ya rufe ido da bak'in Google.

      Tunda su Zulaihat suka doso wajen taga abinda ya faru zuciyar ta ta fara bugawa da k'arfi, tsoro ne sosai ya shige ta don ta San wannan tsayuwar tasu ba ta alkhairi bace.

     Shiko Dr ganin hakan da yayi ba k'aramin b'acin rai ya shiga ba,domin kuwa wannan B'arnar da suka yi masa ba k'aramin kud'i zai jaa ba,gashi kuma shima yana tsoron tunkarar su.

     Juyawa yayi yaga yanda zulaihat gaba d'aya ta gama tsorata jikinta sai rasa yake yi. tsoron ta d'aya kada su tab'a lafiyar masoyinta

     Kallon ta yayi suka had'a ido ya mata alama da ido na "be strong" sai dai hakan da yayi maimakon ya bata k'warin guiwa sai ka karya mata zuciya sai ta fashe da wani sabon kukan

     Ganin haka ya sa ya ce mata tayi hak'uri su koma clinic ya karb'i key D'in motar Dr khaleed sai ya kaisu da ita

      Shi kuma ya juya ya nufi wajen motar zuciyar shi na matuk'ar bugawa don bai San me zasu yi masa ba,sai dai bai bari hakan ya nuna a face d'in shi ba

     Yana zuwa ko kallon inda suke bai yi ba ya sunkuya ya kwashe kayan zulaihat d'in da suka watsar,su kuwa suka dinga mishi dariya suna tsokanar shi Wanda hakan ba k'aramin bata masa rai yayi ba

      Ya gama had'e kayan tsaf ya juya zai tafi sai kawai ji yayi an jefe shi wani abu mai matuk'ar wari ta bayan shi

      Cak ya tsaya yana tunanin menene Wannan suka jefa masa? Sai dai bai juya ya tanka su ba ya ci gaba da tafiya,Ai kamar daga sama sai ji yayi ana ta jefa masa wannan abun mai warin masifa har ji yake tamkar zai yi amai

      Cike da zafin zuciya ya waiga idanun sa sun jawur kamar gauta ya yi wani kukan kura ya kauwa big boy raruma Wanda shi bai expecting haka ba. Kafin kace meye wannan ya had'a masa jini da majina Domin idon Shi a rufe yake ko ganin abin yake baya yi,daga baya yaji an cafko shi ana k'ok'arin daga shi sai ya kuma cakumar Wanda ke rik'o shi ta bayan ya kwantar da shi a kasa ya d'auki wani dutse a gefen shi ya buga masa akai,dai-dai nan kuma Zulaihat ta k'araso wajen don ganin abinda ke faruwa ga mutane sun taru mak'il a wajen ana kallo an rasa mai shiga tsakani

      Da yawa mutanen Wajen Allah shi kara suke yI wa untouchables ana cewa yau sun tab'o Wanda ya fisu masifa, Eeshat kuwa ganin ana dukan su big boy ai tuni ta sampe daga wajen ta karawa wabdon ta iska, bata tsaya koina ba sai d'akin da Ruky ke jinya ta labarta mata abin da ya faru

     Zulaihat kuwa ganin Dr na Neman yin kisa ya sa ta taho da gudu ta na rik'e shi amma ina bai ma saurate ba ba ya hankad'a ta ta fad'i gefe guda, duk da haka bata hak'ura ba ta sake zuwa ta rik'e shi tana janshi,sai a sannan ya gane meke faruwa ya tashi suka bar wajen inda aka bar su k.b a wahale kowa ya Watse Ana musu Allah shi k'ara

UntouchablesπŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 28

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

*we dont just entertain and educate,we touch d hearts of readers*

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*Page 28*
      *By*
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ*

       Bayan zulaihat ta fito daga lectures a bakin lecture hall d'in ta ga sahibin nata,kai tsaye wajen Shi ta zarce, ita kuma Halima ta wuce hostel

        Bayan sun D'an zauna ya bata meatpie da drink d'in da ya siya musu, suna ci suna hira, ya yi gyaran murya ya ce "my zee akwai abubuwa biyu da nake son na sanar dake masu mahimmanci"

     Ta tattara hankalin ta waje guda ta ce "ina jin ka my soul" ya ce "yawwa daga farko dai yau nake so ki yi parking ki koma wancan gidan don an gama gyaran shi kuma gaskiya as I can see
You are not safe  here any more"

      Godiya tayi masa mai yawa tare da yi masa addu'o'i Wanda suka sanyaya masa zuciya,yaji dad'i sosai

     Yace "ba godiya tsakanin mu my soul ke dai ki ta mana addu'a Allah ya zab'ar mana abinda yafi alkhairi ya kuma cika mana burin mu".

      Ta ce "Ameen"

Ya ce "to sai abu na biyu, ina ga its high time iyaye su shiga cikin maganar auren mu,don haka idan kin koma wancan gidan sai ki fara istibra'i daga nan sai mu yi proceeding"

      *ISTIBRA'I* ta mai-maita Kalmar a cikin ranta, nan da nan idanunta suka kawo k'walla,wani irin malolo taji ya tokare ta a mak'oshi,ga wani d'aci da yake taso mata a cikin bakin ta, sai yau ta sake yin regretting abun da ta aikata, sai dai bata ce komai ba ta ci gaba da sauraron bayanin da yake mata, waton yanzu Maheer kallon karuwa yake mata kenan? A tunanin shi lalacewar ta har ta kai yanda zata dinga bin maza da yake mata zancen istibra'i? Amma babu komai Allah ne shahidi akan bata tab'a aikata zina ba sai dai ta San tana yawan kusantar ta,Kuma bata da wata hanya da zata wanke kanta daga zargin da ake mata don haka ta ja bakin ta tayi shiru.

      Sun gama magana akan zata je ta kwaso kayanta su koma gidan da ya kama mata d'in

       Sam bai kula da yanda yanayin ta ya canja ba don shi amincewar da tayi zata yi istibra'i ayi maganar auren su ya sa shi farinciki sosai

      Tace masa zataje ta hado kayan ta sai ta zo su wuce ya ce "to my luv, bara na lek'a clinic kafin ki gama",ta ce "to"

       Tana barin wajen Shi hawayen da take b'oyewa suka fara bin Kumatun ta,har bata ganin hanya sosai don yanda idanun ta ke kwaranya,a haka ta isa hostel ta samu Halima tayi musu girki ta gyara d'akin, bata bi ta kanta ba ta fad'a kan katifa ta fara gunshek'en kuka tamkar ranta zai fita,ji take kamar zuciyarta zata Faso k'irjinta ta fito saboda tsananin b'acin rai da kuma Dana sanin da take ciki.

      Hankalin Halima ba k'aramin tashi yayi ba ganin halin da kawar tata take ciki, a rikice ta iso wajen ta ta dafa kafad'arta tace "Zulaihat lafiya? Me ya faru? Fad'a kuka yi da Dr. d'in? Ko kuma untouchables d'in ne suka sake k'ullo muku wani abun?"

        A hankali zulaihat ta d'ago daga ruf da cikin da tayi ta kalli Halima da jajayen idanun ta tace "Halima na Dad'e ina regretting biyewa su Ruky da nayi na b'ata rayuwata a banza, amma ban tab'a yin Dana sani mai ciwo kamar wadda nake ji a yanzu ba,kaico na Halima nayi asara mai yawa,na Riga na zubar da mutunci na gaba d'aya a idanun duniya hatta a idon wanda nake matuk'ar k'auna,n abarwq 'yaya na abin fad'a" ta sake rushewa da wani kuka mai tsuma zuciya

     Halima tace "me ya faru zulaihat? Me maheer ya miki?"

      Nan zulaihat ta kwashe duk yanda suka yi da Dr. maheer ta gaya mata sannan ta k'ara da cewa wallahi Halima ban Tab'a sanin d'a namiji ba a rayuwata,na San nayi runs sosai da maza da mata amma ban tab'a bari wani ya keta min haddi ba,sai dai na San ko zan had'iye kur'ani ba Wanda zai tab'a yarda da hakan"

    Dafa kafad'ar ta Halima tayi ta ce "I trust you my friend,na yarda dake 100% amma kuma da kin sani kin sanar da shi gaskiya"

      Zulaihat ta sa tissue ta share majina a hancin ta sannan tayi murmushin takaici ta ce "ba shi da wani amfani In Sanar masa tunda ya Riga ya yanke min hukunci,ita gaskiya Ai dole wata rana zata bayyana,idan har da rabon za mu yi aure to da kanshi zai gane gaskiya ba sai na gaya mishi ba"

      Halima ta ce 'to Allah ya tabbatar da alkhairi, zulaihat tace "Ameen"

    Nan suka tashi suka fara parking d'in kayan, cikin lokaci kad'an suka gama had'a kayan tayi masa waya ta sanar da shi sun Gama

UntouchablesπŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 27

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

*we dont just entertain and educate,we touch d hearts of readers*

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*Page 27*
      *By*
*Mmn khadijah*πŸ’…
          &
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ*

Fitowa dr yayi rai a b'ace,kallo d'aya zaka masa ka gabe yana cikin b'acin rai,dan gaba d'aya fuskarshi ta sauya,muma muna gefe muna mamakin yadda cikin kankanin lokaci dr ya canxa,dana ya iya b'acin rai haka.

     Cikin kakkausar murya yake magana,"Kai wannan wani irin iskancine haka?,na lurafa kuna nema ku wuce gona da iri,toh ku sani bafa tsoranku nake ji ba,kuma ba na rasa hanyar da zanbi bane wajen ganin nayi maganinku,ku da kuke 'yan iskan k'arshen zamani,kafin kuyi iskanci mutum nawa sukayi? kuma wacce riba suka samu? In baku saniba yau ku sani a iskancin ma ku burbud'i kuka samu,in har baku fasa mana wani abu nida zulaihat ba kun raina iyayenku 'yan iska kawai marasa mutunci,wallahi3,duk shege ko shegiyar da bai bani hanya na wuceba sai na taka shi,kuma inga uban da zaimin maganar.

      Cikin zafin nama ya koma cikin mota tare da rufe k'ofar motar da k'arfi ya bata key ya nufosu gadan-gadan.

     Da sukaga da gaske yake yi zai iya taka duk wanda be matsaba,tuni suka watse a kan titin.

     Ruky da ta sanya cokalelen takalmi har tana gurd'ewa amma bata kula ba don ta tsorata da yanda taga ya fafaro motar a million.
     
      Yan zuwa saitin su ya d'an rage gudu yace "k'anaun 'yan iska Ashe ma k'aryar rashin kunya kuke yi" ya figi motar shi yayi gaba

      Yana gama parking hostel di'n ya nufa dubo Rabin ran nashi, a dai-dai lokacin kuma suka shigo school d'in ita da Halima, yayan Haliman ne ma ya kawo su tare da k'annen ta guda biyu.
 
      Halima tana ganin shi ta zunguri Zulaihat tace "k'awata duba can kiga" ta kalli inda Halima ke mata nuni sai kuwa karaf idanunsu ya had'u,wani irin tattusan murmushi suka sakar wa junan su inda shi Dr ya ji tamkar ya je ya rungume zulaihat d'in don tsabar farin cikin Ganinta cikin k'oshin lafiya.

       Sai da ta yiwa yayansu Halima sallama ta fito ya nufi wajen shi tana masa murmushi,shima d'in murmushin yake mata domin yana matuk'ar jin dad'in yanda ta d'auki shawarar shi take suturta jikinta,yanzun ma hijab d'inta k'ato ne ta sanya shi har k'asa maroon colour sai takalminta ma white da d'igon maroon a jiki tayi matuk'ar yi masa kyau, darajar ta kuma ta saja ninkuwa a zuciyar shi

      Da ta k'araso yace "waton my heart kina so ki saka min hypertension ko?"

      Sai da tayi farrr da idon ta sannan ta ce "haba my soul wace ni da wannan danyan aikin? "

      Wannan fain da tayi masa ba karamin daukar masa da kasala yayi ba,ya kara jin wani irin singa na ratsa masa zuciya,ganin yayi shiru yana kallonta ya sa tayi snapping yatasan ta a dai-dai idon shi ta ce "soulmate ya dai? Irin wannan kallo haka?"

      Dariya yayi yace "to ya Maheer ya iya da zulaihan shi? ta kashe waya kuma ta gudu a hostel ba notice duk ta tayar da hankalin Maheer d'in ta".

      a yanda yayi maganar cikin shagwab'a ya sa ta sake fad'awa shauk'in son shi,kafin tace wani abu Halima ta zo wajen tace "to love birds lokacin shiga lecture yayi"

     Dr ya ce "ni kam k'awa gaskiya fushi nake yi dake kin min fashin mata duk kun d'aga min hankali don haka sai kun answer query".

       Dariya tayi tace "tuba nake yi Angon Zulaiha ba laifina bane ruwa ne ya tare ta shi yasa bata dawo ba"

     "To kuma shine harda kashe waya?"

     Sai a lokacin zulaihat tace "Ai wayar ma fa tana wajen chaji yanzu idan na fito lectures zan karb'o"

     Yace "its Ok yanzu dai kuje lectures d'in zan jira ki gama don akwai important issue danake son nai discussing dake"

*****

     B'angaren untouchables kuwa yau sun sha mamakin yanda Dr yayi reacting a Kansu, gashi garin haka har  Ruky ta ji ciwo a k'afa sai da suka kaita asibiti aka mata d'aurin kafar.

     Eeshat tace "gaskiya guys wannan gayen fa yaga wajen kwanan mu,ka duba yanda muka Dad'e muna kafa masa tarko yana tsallakewa amma yau d'aya yayi mana muguwar b'arna haka?" Ta fad'i gana kallon k'afar Ruky da ta sha bandage

     Big big yace "gaskiya gayen nan ba k'aramin shu'umi bane,amma duk da haka ba zamu hak'ura ba sai mun d'aukar ma Babyn mu fansar wannan jinyar da ya saka ta".

UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 26

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L


2017


*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*We don't just entertain and educate,we touch the heart of the readers*

*Page 26 by*
*mmn khadijahπŸ’…*
           *And*
*Faridat musa (sweery)*

Ab'angaren zulaihat kuwa bayan tabar wajen dr wayarta ta bada caji saboda ta mutu,kuma akwai assignment Ι—in da zatayi.

AΙ—aki ta samu Halima ta baje tana ta girki,mamaki ne ya cika Zulaihat dan ita batai tunanin ganin Halima a hostel ba.

Murmushi ta sake mata tare da cewa "kaga masoyan asali,wanda tun daga  siffa, kama,hali sun dace,gaskiya fa k'awata ba k'aramin dacewa kukayi da docter d'inkiba",ta k'arasa maganar cikin zolaya.

"wallahi kedai bakya rabo da tsokana da barkwanci,ni ba wannan ba nayi mamakin ganinki a hostel a dai dai wannan lokacin"

"kinsan miye?naba su mum Ι—ina labarinki ne shine duk yan gidanmu suke kwaΙ—ayin ganinki,niko nace su kwantar da hankalinsu duk randa zanzo zamu taho tare,Ι—azu akamin waya dad ya dawo kinga sai muje ku gaisa ko?".


Ba musu zulaihat tace "toh " nan fa suka haΙ—u suka gama girkin da ganan suka shirya.

Shagon mai chaji suka je dan ta karΙ“i wayarta amma sukaga shagon a rufe,ganin a nata kiran Halima a waya daga gida yasa suka wuce da niyyar inta dawo anjima ta karΙ“i wayar.

 

Ba k'aramin karΙ“a aka ma Zulaihat ba a gidan su Halima,sun nuna mata k'auna sosai,yadda suke mata kamar dama can sun saba da juna,haka suka zauna a nata shan taΙ—i.

Ta jima sosai a gidan dan sai yamma lis sannan tai shirin tafiya,abin Allah saida ta fito ruwa ya tsinke kamar da bakin k'warya ba yadda ta iya dole ta zauna,Halima kuwa da sauran 'yan uwanta farin ciki kamar bazasu mutu ba,domin sunyi sunyi da ita akan ta kwana tak'i wai tabar wayarta a sch.
Haka aka sha ruwa har 12am.

**************
Kamar yadda suka tsara da yamma Kb zai kawo cocaine haka ko akayi,ya kawo ya dank'a a hannun Ruky ahaka sukayi sallama,idan aiki ya kammala zata kirasu a waya.

Basu da matsala da Baba mai gadi dan tuni suka rufe masa baki dafarare bugun Abuja.

Jikin Ruky har rawa yakeyi gaba Ι—aya ta kosa dare yayi ta aiwatar da nufinsu akan Zulaihat.

1:00am nayi k'afa ta Ι—auke a hostel su Ruky suka shigo kai tsaye Ι—akin Zulaihat suka nufa.turawar da zasuyi sukaji k'ofa gam,dayake sunada key Ι—in Ι—akin cikin zafin nama suka buΙ—e,abin mamki ba Zulaihat a ciki,gani suke kamar zasu ganta dan gaka suka shiga Ι—akin suka hau duba ta harda Ι—aga katifa.

Da suka tabbatar bata Ι—akin ne suka fito rai a Ι“ace,kiran su Kb sukayi suka faΙ—a mudu duk abinda ke faruwa,ba k'aramin mamaki suka yi ba,domin basu taΙ“a tunanin Zulaihat zata tsallake ma target Ι—insuba.

Suna gama waya da Ruky Kb ya danna number Dr Maheer saida ta kusa tsinkewa kafin ya Ι—aga.

"kai wato damu kake jako?,mu zamu rika tsara abu kana wargaza mana,toh ka sani a tarihinmu bamu taΙ“a neman abu mun rasaba,dan haka bazamu fara akan Zooly ba,wato kaje malaminka ya faΙ—a maka kuΙ—irinmu akan Zooly shiyasa ka Ι—auketa a hosteΖ™ ko?,toh ka sani yau nasara na wajenka gobe kuma kasa a ranka mu keda nasara.
Cikin zafin nama ya sauke wayar tare da furzar da iska daga bakinshi.
"Guys mu wuce zanu nunama gayen nan mun fishi sanin duniya."

Zunb'ur Dr ya tashi,tuni ya nemi baccin dake idon shi ya rasa,nunbern Zulaihat ya kira yaji a kashe nan fa ya kara shiga tashin hankali.

Ya kira wayan tafi a k'irga ganiyake kaman in yakira zai shiga amma bai samu ba, ji yake kaman ya tashi ya tafi Hostel d'in amma ba hali saboda yanayin tsaro idan dare yayi, tashi yayi yayi alwala ya tada sallah, ya ringa kai kukansa ga mai sama dan yasan shine kad'ai zai iya kub'utar da Zulaihat daga sharrin *untouchable*.

Bashi ya tashi daga kan sallaya ba saida yaji kiran assalatu sannan ya tafi masallaci, a daddafe yayi salkah saboda azababben baccin dake damunsa.

A b'angaren Zulaihat ma hankalinta ba'a kwance yake ba saboda tasan Dr zai kirata kuma inhar yaji a kashe hankalinsa ba k'aramin tashi zaiyi ba, haka tayi bacci a daddafe da tunanin Dr a zuciyarta.

Tun asuban fari *untouchable* suka fito gate d'in makaranta suka tsaya duk wanda ya kallesu yasan suna cikin b'acin rai ba kad'an ba shiyasa ma d'aliban suke kaucewa insun gansu dan tsira da mutuncinsu.

Dr Maher suka hango a cikin motarsa ya kwaso da gudu da ganinsa yana cikin tashin hankali, duban juna sukayi sukayi magana da ido alamar akwai abunda suka k'ulla masa a ransu, jeruwa sukayi a daidai hanyar da zaiwuce yanda dole saiya tsaya, wani wawan burki yasha ganin mutane a gabansa "Allahumma ajirni fi musibati waklifni khairan minha" abunda ya firto kenan abakinsa ya tsaya.

Ku biyo mu danjin yanda zata kaya.

*UNTOUCHABLE*πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀

*mmn khadijah*
&
*Sweerry*

RYAUWAR HOSTEL PAGE 25

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

2017

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*wannan shafin nakine yar uwa rabin jiki hajia laurat  kano mmn husnah,hakika ke masoyiyatace bani da kalaman da zanyi anfani wajen nuna godiyata a gareki sai dai a koda yaushe ina miki addua da fata na alkairi,allah yasa kifi haka ya raya miki zuria,ameen*

*Page 25*
      *By*
*Mmn khadijah*πŸ’…

Kafin takai k'asa Allah ya bata iko ta dage,dubawan da zatayi taga k'atuwar taya ce cikinta ansa xare anyi sak'a ita duk bata kula da tayan ba saboda hankalinta na can kan Dr Ι—inta.
Ganin haka yasa Dr ya matso gurinta yana jera mata sannu,
 D'aga kanda zasuyi suka hango Ruky tsaye ta zuba musu ido kwafa tayi  sannan ta wuce.

Allah ya shiryeku shine abinda Dr ya faΙ—a,suka bar wurin.waje mai kyau suka samu anan ake zuba love,hak'ik'a sun dace da juna matuk'a,bayan sun taΙ“a hira dr ya faΙ—a mata zataΙ“ar hostel dan har ya sama mata gida ya gama komai komawa kawai ya rage tayi.bataso hakan ba dan tana matukar kaunar zaman hostel amma bata nuna masa hakan da yayi be mata daΙ—iba, domin ance yaba kyauta tukuici,tayi godiya sosai amma ta sanar dashi zataje gida jibi intaje zata faΙ—ama iyayenta duk abinda sukace zaiji.yaji daΙ—in jin haka daga gareta,domin hakan ya k'ara tabbatar masa da lallai zulaihat Ι—insa mai biyyayya ce da hangen nesa,domin yasan da watace ba itaba zaiyi wahala ta faΙ—ama iyayenta,duba da yadda yasan masu zaman hostel ba zaman daΙ—i sukeba.

Sun jima suna shan love Ι—insu daga nan ya bata abinda ya kawo mata sukayi sallama ya tafi.

*****************
Bayan kwafa da Ruky tayi ta wuce motarta ta hau ta nufi wajen wani club da suke shanawa,bayan sunsha rawa da duk baΙ—alansu, kowa ya watse aka barsu,dayake haka sukeyi bayan kowa ya watse su sai su zauna zaman shan syrup su buΙ—e sabon babi na iskanci.

Eesha ce ta dauko kayan hawa sama bada jirgiba kirarin da sukeyi knan.

"Ruky ce tace baby aje wannan kayan akwai maganar da nakeso muyi,nan fa kowa ya samu guri suna sauraronta.

Duk abinda ya faru ita da zulaihat ta faΙ—a musu harda tayan data saka mata,tacigaba da cewa guys nifa ina mamakinku,anya wannan yarinyar ba wani kullin tayi muku ba?ku tuna yadda muke a baya,duk yayinyar da muka nuna muna kwaΙ—ayi ko yar gidan uban waye sai mun sameta da karfi koda lalama,saita gundiri kowa acikinmu,amma ku duba yadda kuke sanya a lamarin zooly,ai ni inaga abin kunyanema a garemu zooly ta shigo wannan kungiya tamu ta fita a raayin kanta,kuma taci gaba da rayuwa normal duk muna kallanta,toh bara kuji idan ku kun hak'ura da kwasar kayan daΙ—inta toh nidai ina nan sai inda karfina ya k'are."

"Nan suka fara kururuwa kowa na faΙ—an albarkacin bakinshi.

"Enough guys kB ya faΙ—a tare da Ι—aga hannu,munyi anfani da malam tafi da imani abu be yuyuba,akwaifa sauran method da muke dasu, yanzu kawai muyi anfani da cocaine inaga zaifi,kunga ku Ruky da Eesha tunda kuna shiga Ι—akinta ku zamuba kuje ku shak'ama shegiya ba tare da kowama ya jiba,kunga idan ta fita a hayyacinta k'afa fara Ι—aukewa a hostel sai ku fito mana da ita,bamu da matsala da baba mai gadi tunda yana karΙ“an farare,muna bashi aikinmu zai tafi yadda muka tsarashi.
Kuna fito mana da ita magana ta k'are,zooly mun gama da ke hhhhhhhhhhhh ya k'arasa maganar

Yes wannan shawara tayi haka duk kansu suke faΙ—a,nan suka aje magana akan kb zai kawo cocaine da yamma,bayan sun gama shaye shayensu suka bar wajan.

Duk abin nan da sukayi a kunnen Isa ogan masu tsaron zulaihat,dan bayan sun bar wajan Dr tsara yadda zasuyi aikin sukayi,Isa tunda shine oga yace zai rink'a bibiyar su untouchables duk wani motsinsu dole zai rik'a sani,manga da sani su zasu rik'a kula da zulaihat duk wani motsinta su rik'a sani a haka suka rabu kowa ya fara aiki.

Da Isa akasha rawa a club dan shigewa cikinsu yayi tsilif aka sha harka saboda karsu ganeshi,bayan an watse ne ya sami wani lungu ya mak'ale inda bazakayi zaton akwai mutum ba,dan ko numfashi a hankali yake ja da saukewa,saida suka gama komai suka tafi  sannan ya fito.

Wayar Dr Maheer yaita kira danya faΙ—a masa abinda yaji amma kash tak'i shiga is not recable at d moment ake faΙ—a masa,gashi bashi da numbern Dr Khaleed bare ya kira.
Haka ya tari dan acaΙ“a ya nufi gidan Dr ko zaici saa yana gida,yana isa wani k'aton kwaΙ—o yayi arba dashi a jikin kofar gidan hakan ya tabbatar masa da bakowa a gidan.jiki a sanyaye ya juya.har bayan sallan magriba yana kira numbern Dr bata shiga.

*maryam muh'd lawal*πŸ‘Œ
*UNTOUCHABLES*πŸƒπŸ»‍♀

RAYUWAR HOSTEL PAGE 24


🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

         We don't just entertain  we touch the heart of d readersπŸ‘Œ

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

_thankz yhu for my beautiful bufday wishes! I fell grateful and lucky to have so many amazing by my side, fan's bohoot/bohoot shukriayh!!!_ One love#😍
        Serious sick!!!!πŸ˜₯needed ur du'a friends

Page 24 by
*jannart lameed'o*🌝
  (Babyn garkuwa)

   Mutane 3 suka samu
 maza,  suka musu bayanin aikin da zasu musu, babban ne mai suna Isah ya fara magana,

    "Insha Allah ogah zamuyi iyakan kok'arin mu wajan bata kariya yadda ya dace"
 
   Dafa kafad'ar sa Dr Maheer yayi yana mai murmushi wanda yake k'ara masa kyau,

    "Good Isah haka nike so, mutukar kukamun aiki yadda ya dace ni kuma Zan muku dukkan abunda kuke so"

    "Insha Allah zamuyi kok'ari Oga"

   Sallaman su yayi sannan ya sheda musu gobe zasu fara aiki, bayan tafiyan su Dr Khaleed ya dube Dr Maheer,

     "Abokina da alaman nasara atare damu akan *untouchables*"

      "Sosai mah, insha Allah mune da nasara , fatana Allah ya shiga tsakanina da *untouchables*"

  "Ameen y Rabbi abokina, Amman ka dage da addu'a don zasu iyayin komai don ganin sun mallaki Zulaihat"

   "Wannan hakane, kuma insha Allah Zan k'ara akan Wanda Nikeyi"

        motan Dr Khaleed suka nufah, shi  yake jansu suna tafe sunah hirah, Dr Khaleed ne ya ajiye Dr Maheer a gidan sah sannan ya d'auki hanyan gida.
     Dr Maheer nashiga bedroom nashi toilet ya fad'a yayi wanka, tare da alola bayan ya fito ne ya tayar da sallah cikin nutsuwa ya dad'e yana kai kukasan gurin Mahaliccin sah, sannan yah shafa,
     Kan bed nashi ya komah tare da d'aukan phone nashi dake kan bed d'in number Zulaihat ya kira, bugu d'aya yayi ta d'auka,

   "Assalamu alaikum my soul, yah kake?"

      "Lafiya qalau my dear, hope kina cikin k'oshin Lafiya?"

    "Lafiya qalau my soul"

"Haka nakeson ji, yah karatu kuma? Fatan zan sameki anjima?

   " alhadulillah my soul, eh zaka same ni babu inda zanje"

        Hirah suka tab'a kad'an kafin sukayi sallamah kowa da tunanin d'aya cikin ransa,
   Bayan gama wayansu Zulaihat tashi tayi domin yau so take tayi wah Dr Maheer kwalliya mai kyau,  meckup tafarayi wanda rabonta dashi harta manta, ta nayi tana murmushi kaman Wanda Dr Maheer ke gabanta,
    Tana cikin yi kenan Rukky ta shigo d'akin, ganin yadda Zulaihat take ta faman murmushi ita d'aya, yah tabbatar mata da Dr Maheer ne zaizo, nan take taji zuciyar ta tafara matah wani irin zafi Amman ta daure, ta dubi Zulaihat,

      "Zooly yau kintuna da kwalliya ce? Koko kin dawo kan hanya ne?

   Shuru Zulaihat tayi saima ci gaba da kwalliyan ta tayi,batare da takula Rukky bah, Rukky ganin tak'i kulata ne yasa ta kuma cika, tazo har wuya sauran k'iris ta fashe,

    " Zooly ba magana nake miki bah?"

   Sai a sannan Zulaihat ta d'ago idon tah, gami da kallan Rukky wacce tayi tsaye kaman gunki,

    " Inace mungama wannan babin dake, nace miki sunana Zulaihat bah Zooly bah, muddin kinason iringa amsa miki magana to kik'irani da sunana na gaskiya bah shirme ba"
 
    Rukky sake baki tayi tana kallon Zulaihat wacce tai mungun bata mamaki ,ji take kamar ta shak'eta Amman babu halin haka,
   Juyawa kawai tayi tabar mata cikin d'akin,

Zulaihat kuwa hakan ya mata dad'i don cigaba da kwalliyan tah tayi abunta,
    Bayan ta gama kwalliyan ta, tasanya wani black d'in dogon Riga mai adon red ajiki kayan sunyi matuk'ar mata kyau sosai kaman ba ita bah, rolling d'in d'ankwalin tayi, tana cikin faisah turare phone d'in tah yah fara k'ara alaman yana naiman agaji, dasauri ta d'auka ganin Wanda ke kiran ne yasa tayin wani murmushi sannan ta d'auka tare da karawa a kunnan tah,

    "Hello my soul, harka iso ne?"

   Mudai bamuji abunda yace mata bah saidai kawai munji tace "owk gani nan fitowa"

      Takalmi ta zurah a k'afarta ta fitah, tundaga nesa ta hangoshi yayi matuk'ar mata kyau, k'ananan kaya shima yasa red and black kayan sun amsheshi sosai,sai aikin murmushi suke sakarwa junan su,

  dap zata isa wajansa ne taji ansa mata Abu ak'afa tayi yuuuiiiiiii zata..................

*tofahπŸ€”da magana anya Dr Maheer Zaiyi nasaran fitar da Zulaihat daga hostel kuwah? Danjin yadda za akayi kubiyomu*

 UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀πŸƒπŸ»‍♀

*jannart ceπŸ‘Œ*momyn Janan

RAYUWAR HOSTEL PAGE 23

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
      P.M.L

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNART LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page23 by
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ😘*
           &
*Maryam s BΙ›llΦ…*

         The next day Ruky tayi shirinta tsaf na zuwa wajen boka domin dubawa ko can ta baro maganin, sai dai to her greatest surprise ba a can ta Bari ba.


      Sai ta ce 
"To boka tunda ba a ga wancan d'in ba ina ga Ai sai ka bamu wani don a matsae muje kwarai da aikin nan."


     Boka yayi dariya ya ce "Ruky mai duniya, Ai kin makaro domin Wannan maganin shi ne na k'arshe da ya rage min, kuma kayan had'in shi ma wahala suke yi sai dai ki yi hak'uri.
Ba k'aramin tashin hankali Ruky ta shiga ba da jin bayanin boka ba.

      Haka Ruky ta mik'e  jiki a salu6e ta koma da tsabar takaicin 6atan maganin nan.

*****

    A B'angaren Doctor Maheer kuwa friend d'insa ne mai suna Dr Khaleed, Dr Maheer ya kwashe labarin komai ya fad'a masa game da Zulaihat da kuma *untouchables* 
Bayan ya gama ne Dr Khaleed ya bashi shawarwari sosai akan kada ya rabu da zulaihat domin rayuwar ta tana cikin damuwa, gwara ya zamo jajirtacce akan lamuranta tunda yana sonta, kuma idan ya aure ta ma jahadi yayi.

Tabbas Doctor Maheer nason Zulaihat so na hak'ik'a sai dai 6angare d'aya na zuciyarsa yana tsoron karawa da *untouchables* domin ya riga da ya lura wasu irin yara ne da  basa jin magana, kuma gasu 'yan duniya wanda duk wani abinda suka ce zasuyi to zasuyi d'in. Sheyasa yanzu dole sai ya bi a hankali idan yana son cimma burinsa.

Dr Khaleed yayi ajiyar zuciya ya dafa kafad'ar Dr Maheer yace
"Abokina bari na baka wani tak'aitaccen labarin abinda ya faru da wata yarinya a baya."
Dr Maheer yace 
"Ina jinka Khaleed."

Dr Khaleed yace
"Wato akwai wata yarinya a baya da suka nemi ta shiga cikin k'ungiyarsu, sai yarinyar tak'i basu had'in kai, sai suka rik'a bibiyarta ta k'arfi da kuma ta magani, suka rik'a binta, suka takura ma yarinyar sosai suka hana ta sukuni, to sai Allah ya tsare ta bata shiga k'ungiyar ba, da suka ga duk wata hanya da zasu bi su dawo da ita cikinsu abin ya ci tura sai suka haukata ta, abin takaicin kuma kowane a cikinsu sai da yayi mata fyad'e. 
To a gaskiya nidai zan baka shawara kar sake ka rabu da Zulaihat, sannan kar ka barta ta cigaba da zama a hostel, ni a ganina ka d'auke ta ka kaita can wani wuri kamar can cikin gari ka kama mata gida cikin mutane, kuma wanda daga can zata dinga shiga makaranta tana dawowa, sannan ka sanya masu tsaronta sosai, wanda ita kanta bazata san da su ba, saboda komai zai iya faruwa, so we have to be very careful sosai, sannan dole ne fa sai makaranta ta d'auki mummunan mataki akansu, don barin irinsu *untouchables* had'ari ne sosai."

Dr Maheer ya numfasa yace
"A gaskiya aboki na wannan shawara taka tayi, kuma nagode sosai Allah ya saka da alkhairi, sannan da na fara karaya da al'amarin amma yanzu shawarar da ka bani ta taimaka min sosai, na kuma samu k'warin gwiwa, kuma insha Allah sai na auri Zulaihat."

Dr Khaleed yayi murmushi yace
"Haka nakesonji daga bakinka, anjima sai muje a nemo mata suitable gida, da kuma irin mutanen da suka dace su tsare maka ita."

Dr Maheer yace
"Haka ne Allah ya shige mana gaba."

Dr Khaleed yace
"Amin."


Da yamma suka tafi neman gida, inda sukayi  sa'a suka samu gida irin estate d'innan kuma wurin yayi kyau sosai, nan suka gama duk wani abinda ya dace suka tafi neman wad'anda zasu sanya da zasu tsare Zulaihat...


To masu karatu shin ya *untouchables* zasuji idan aka ce Zulaihat ta bar hostel? Kuma shin Dr Maheer zai auri Zulaihat kamar yadda ya fad'a? Sai kun biyo mu a next page don jin yadda zata kaya.


MSB AND MRS FAWWAZ
(Maman Ameema and Maman Inteesar)😘😘😘


UNTOUCHABLESπŸƒπŸ»‍♀️

RYAUWAR HOSTEL PAGE 22

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

```bamu rok'i kowa ya karanta novel d'in nan ba,amma a farko kafin mu fara sai da muka ce bamu yi don cin zarafin kowa ba idan yayi dai-dai da rayuwar da kike ciki muna miki fatana shiriya, to indai ba mutum ya San halin shi muke fad'i ba meye za'a fara bin mu da Allah ya isa? Idan kin Fasa zagin mu kin raina gyatumar ki kuma ke ba 'Yar halak ba ce, zagin ki da Allah ya isa ba zai sa mu daina tona miki asiri ba sai dai ma ki k'ara bamu k'arfin guiwar ci gaba da abinda a muka fara. Tunda kuma haka halin ki yake muna miki fatan shiriya ```

Page 22 by
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ*😘

      Daga wajen boka Ruky hotel ta koma direct inda Alhajin keta  jiranta.

      Sun Dad'e suna lalacewa kafin daga baya ta yakice shi da k'yar ta shige toilet domin yin wanka.

      Bayan ta shiga ne Alhaji ya d'auko wrapper 1000 notes guda uku ya saka mata a jaka,kawai sai hankalin shiya kai kan k'ullin maganin da ta karb'o d'in,haka kawai sai jikin shi ya bashi maganin nan shi zata yiwa amfani, don haka sai ya d'auke shi ya b'oye ba tare da sani ba.

      Bayan ta fito ta shirya da k'yar Ta samu ya barta ta tafi domin bai gaji da ita ba kawai dai Dan ta matsa sai ta tafi ne.

     Duban ta yayi yana wani kashe ido shi a Dole ga D'an bariki ya ce ke "Ruky shiga rai ne da ke wallahi gaki kuma da jan Aji,sai kin wana mutum kike bashi kayan dad'i"

      Wani fari tayi da ido ta ce "kasan shi gold ba a samun shi sakaka Dole sai an wahala"

     Dariyar k'eta yayi mata yace "haka ne babayna,amma da kin bari mun kwana gobe sai ki tafi"

     Ta ce "Gaskiya dole na tafi don akwai important abun da zan yi ba don haka ba da na kwana na k'arasa rikita maka lissafi"

      Wata dariyar ya sake yi had'e da D'an bugun bum-bum d'in ta yace "Ruky kayan dad'i",

tace "Alhaji naira".

     Har bakin mota ya rako ta ya ce mata "akwai sak'on ki a cikin jaka"

      Lek'a jakar tayi ta ce "I trust you Alhaji sai next week d'in"

       sai da ta bar compound na hotel d'in shi kuma ya koma ciki yana fad'in "yarinya ni wallahi na fi k'arfin wannan tsubbace-tsubbacen naki, yanzu da na d'auke maganin Ai naga da abin da zaki sihirce ni, ki mai da ni wani sha-sha-sha da k'arfi da yaji".

      A Daren ranar suka fita meeting around 1:00am Na dare,inda suna ganin Ruky suka fara hailing d'inta suna " The untouchable Ruky"

      Ita kuma sai bada fad'i take yi domin ta san ta samo musu solution na problems D'in zulaihat.

     Nan ta gaya musu yanda suka yi da boka, suka k'ara kaurewa da tafin murna ta ce "to yanzu ga magani sauran aiki kuma naku ne",ta nuna mazan.

      Zura hannu take a jaka da nufin d'auko maganin,sai dai me? Magani yace "d'auke ni inda kika ajiye".

     Abu kamar wasa fa Ruky ta nemi magani bata gani ba,don haka sai ta ce "guys ina jin fa na baro maganin nan a wajen boka ko kuma a hanya na jefar da shi"

      Gaba d'aya suka had'a bakin cewa "shit", big boy harda dukan hannun shi da jikin bishiya don ya gama cin buri.

      Ganin haka ya sa ta ce "Guys not to worry gobe insha Allah zan koma na duba maybe a can na baro, idan ma ba can bane sai na sake karb'o mana wani"

       Wannan ya sa suka D'an ji relief,daga nan kuma suka ci gaba da tsara yadda shi kanshi doctor d'in zasu b'atar da shi.

*wannan kenan*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 21

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*Page 21 by*
*mmn khadijah*πŸ’…

*WANNAN SHAFIN NAKINE KE KADAi YAR UWA AISHA ALIYU GARKUWA*
*LALLAI DAUKAKA TA ALLAH CE NAYI MURNA MATUKA ALLAH YA KARA* *DAUKAKAKI DA MA DUKKAN MUSULMI*
*ALLAH YA KARRMU DAGA SHARRIN MASU SHARRI YA TSOKALE IDON MAHASSADAπŸ‘„❤πŸ˜πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ*

_happy birthday k'awata farida musa swerry allah ya albarkaci rayuwa yasa ayi na gaba da alkhairi_πŸŽ‚πŸ§πŸ­

duk magaΓ±Γ n da sukeyi dr Maheer najinsu dan yanΓ  tsaye a gefensu, gaba d'aya ji yake jikinshi ba dad'i kanshi kuwa haka yakejin wani dumm kamar an d'aura masa dutse.
*Allahumma ajirni fi musibaty wa akhlifni khairan min ha*abinda yaketa fad'a kenan acikin ranshi dan bakinshi ya kasa bud'ewa gaba d'aya ya masa nauyi.

Mai machine ya tare ya hau suka nufi gida.yana zuwa kwanciya yayi ko zai samu bacci dan ya samu relief, amma ina tunanin ya hanashi sak.

Zulaihat ina matuk'ar sonki,kin had'a duk wani qualities da nake nema a tattare da mace,wallahi in har kika barni bazan rayu cikin farin cikiba,ki daure mu rayu a inuwa d'aya,haka dr yaketa sanbatu shi kad'ai a d'aki.ganin ya kasa samun mafita ne ya dan'na numbern abokinshi khaleed,nan fa ya fad'a masa halin da yake ciki,nan khaleed yace yana zuwa.haka dr yaci gaba da sak'awa da kwancewa.

********
Ab'angaren zulaihat kuwa bayan fitansu ta d'auki dogon lokaci tana abu d'aya,sai da tayi ya isheta tayi shiru,nan fa ta fad'a kogin tunani,abubuwa gaba d'aya sun jagule mata ta rasa mafita gashi Fatima bata nan bare ta bata shawara,a yanzu ji take ta tsani kanta dan duk abinda ke faruwa da ita, ita tajama kanta,kukan takaici ta k'ara fashewa dashi.

K'ofa taji an turo, da sauri ta tashi zunbur ta zauna tare da goge hawayen idonta,dan ita a tunaninta su Rukky ne.
Halima shehu ta gani ta shigo coursemate dintace kuma a da kusa da dakin su zooly take zama, amma yanzu ta koma cikin gari da zama sai dai ta shigo tayi lectures ta koma gida,tun wataran da yayanta ya kawo mata sak'o daga gida da daddare yaga yadda mata suke bad'ala a bakin hostel,wajen ya cika da yan mata da samari kamar ana cin kasuwa,ga bakin duhu dan ko tafin hannunka baka gani amma a haka wai ana hira,wasu cikin mota,wasu ko akan cool down,wasu gindin bishiya wai nan duk hira ake,tunda ya fad'a a gida daddynsu yace ta tattara kayanta ta koma gidan babban yayansu da zama dan yafi kusa da makaranta.

Zama Halima tayi kusa da Zulaihat tare da sakin wani murmushi,tace "sunana Halima ni coursemate dinkice,nasan ba lallai kisanniba kasancewar munada yawa a course d'in."

Zulaihat ko da mamaki ya gama bayyana a fuskarta da kyar ta iya cewa "na ganeki sannu da zuwa".

"Yawwa "Halima tace tare da cigaba da bayani."nasan zakiyi mamakin ganina,to karkiyi mamaki dan ni da alkhairi nazo gareki,idan bazaki damuba inaso mu zama k'awaye idan har kin amince,saboda ni tunda kika shigo makarantar nan kike birgeni,dan tarbiyyarki tamin.naji wani iri alokacin dana ga kin fad'a kungiyar su untouchables tun daga nan naji kin siremin,sai kwanan nan naga kamar yanayinki ya canza kina zuwa lectures ga kuma shigarki ba kamar daba shiyasa na yanke shawarar sanar dake ko zaki karb'i k'awance na".

Duk da zulaihat tana cikin tashin hankali amma bayanin Halima saida yasa ta saki murmushin da batasan sanda tayi shiba,"Allah sarki ashe har yanzu bazan rasa masoyaba,na amince da k'awancenki Halima kuma gaskiya bani da kamarki duk fad'in Hostel d'in nan,kinzo min a lokacin da kowa ke guduna saboda bar nan dana aikata a baya".

Tashi zulaihat tayi taje bakin window sanan taci gaba da magana,"hak'ik'a na tafka babban kuskure a baya,nayima rayuwata tabonda ba lallai ya gogeba,bansan yadda akayi na fad'a cikin wannan kungiyaba,gashi yanzu sun zamamin k'adangaren bakin tulu",kwashe duk abinda ya faru da ita tayi ta fad'ama Halima dan tana matuk'an neman shawara.

Nan fa Halima tace "karta rabu da dr danyana tsananin sonta kuma kasancewa dashi kamar wani garkuwa ne a tattare da ita",ba k'aramin shawara Halima ta bata ba, kuma taji dad'i sosai danji tayi kamar ta cire mata damuwar gaba d'aya,haka suka dan tab'a hira bayan wani lokaci ta rakaka ta hau mashin dan zuwa gida.

********
Ab'angaren untouchables kuwa bayan aika - aikan dasukama dr wajen meeting d'insu suka wuce,dan basu da buk'atar datafi samun hanyar da zooly zata dawo garesu,da kuma yin abinda zasu bak'antama dr Maheer.

Sun dau tsawon lokaci suna tattaunawa daga k'arshe suka yanke shawarar sace zooly su kaita inda ba wanda zaiyi tunanin tana can,suyi amfani da ita yadda suke so dan gaba d'ayansu suna mararin tarayya da ita.

Bayan kawo wannan shawarar big boy ne yace "yanzu ta wace hanya kukega zamu bi wajen   saceta?kungafa yanzu ba zuwa inda muke takeyiba,sanann ba huld'a sukeyi da su Rukky ba,ya kukega zamuyi".?

"wannan ba abin damuwa bane,zanje wajen malam kore imani ya bani sa'a daga nan zan gudanar da komai "cewar Ruky.

wani wawan ihu suka saki wanda saida fankar wajen tayi motsi,cak suka dauki Ruky suna murna, daga nan kuma suka ajeta suka fara bata kiss ta kowani sashi na jikinta.

Bayan sun tashi Rukky ta wuce Hotel d'in da take zaune ita da wani Alhaji,wanka tayi ta shirya ta nufi wajen malam tafi da imaninka.

Anan ya tabbatar mata da cewa akwai sa'a,ba zooly ba ko dr zasu iya sacewa indai tayi amfani da wanan k'ullin maganin.

Karban maganin tayi ta saki wata shuumar dariya ta wuce ta tafi.

*danjin yadda zaa kaya ku dakacemu a shafi na gaba*

*muna kara baku hakuri da rashinnjinmu da kukayi bunch of love*πŸ‘„❤
*the untouchables*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 20

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘


PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*


*kamar yanda muka tsara labarimu haka zai tafi duk wata shegiyar da ta sake ja mana Allah iyasa muma mun barta da Allah in halunki yazo dai-dai da mutanen littafin saiki fad'i magana akanmu dan rainin wayo? Mu munsankine ko munsan daga duniyar da kike ne? Abunda muka sani shine muna fad'akar da al ummah akan abunda ke faru kuma mu fatanmu shine Allah yasa rubutun mu ya zama hanyar shiryuwan masu irin halinsu Ruky duk wacce ta zagemu mun barta da mai sama, a ci gaba dagashi suya sai ran sallah*

Wannan pagen nakune
*Maryam Abdool*
*Ummu khady*
*sisin mama*




Page20 by:
*Faridat musa (sweerry)*



Hostel tayi da sauri tanaji Dr Maheer na kiranta amma tak'i waiwayawa. Kwanciya tayi ta shiga rera kuka marar sauti ita kad'ai tasan yanda takeji a cikin zuciyarta,ta tabbatar sonda takema Dr bazata iya dainawa ba tace su rabune kawai dan ya zauna lafiya, hakan ne kawai mafitar da zaisa *Untouchables* su rabu dashi.


A b'angaren Dr kuwa kasa matsowa yayi ba abunda kunnensa yakeji sai sautin kukan Zulaihat abun na tab'a masa zuciya,
"Duk rintsi bazan barki ba koda ke zaki iya rabuwa dani" irin wannan maganganun ya rink'ayi a cikin zuciyarsa har isa yanda zashi.



Kwance take a Hostel tana duba lecture note inta taji an shigo d'akin bako sallama, d'aga ido tayi dan ganin wani mai k'arfin hali ne haka, Ruky da Eesha ta gani cikin mummunan shiga abunba ko kyan gani sanye suke da kaya iri d'aya amma diffrent colours, guntun skirt ne da riga wanda baida hannu fuskar nan tasha uban heavy make up kai kuwa yasha attachment se tauna chiewing gum sukeyi irin na rik'ak'k'un karuwai.


"Zooly ki tashi ki shirya kinsan yau ne birthday d'in budurwan Big boy ko?"
Ruky ta fad'a tana ta tsina fuska abunko kyan gani babu.

Shiru tayi bata tanka ba hasalima bazakace da ita ake maganar ba.

Eesha ce ta kalli Ruky da ido tayi mata alamar ko bataji me tace bane, sake maimata maganar tayi ganin stil shiru ta sake ya tabbatar musu da taji sharesu tayi.



Cikin hassala Eesha tace "wannan wani irin iskanci ne ana miki magana kinajin mutane kin mayar dasu 'yan iska wannan ma ai rashin mutunci ne!"


Ruky tace bai kamata ki bita da masifa ba sarkin hasala kinsan yanzu haushinmu takeji saboda Dr amma ahankali zata dawo hanya, pls Zooly tashi ki shirya mutafi man kinsan bai kamata ace baki jeba Big boy bazaiji dad'i ba sam."


Duk maganar da sukeyi tak'i kulasu hasalima sun fara kaita bango an kusa zuwa stage d'in da zata iya kai mari wanda ahalin yanzu bata fatan hakan wanda tayi da farko ma ya isheta dayayi sanadin shiganta gararin rayuwa,tattara lecture notes d'inta ta fara da niyar bar musu d'akin ai inta fita suma zasu fita.


Ganin hakanne yasa Ruky sakin wani sakalin murmushi ta matso kusa da ita ta zauna ta dafa kafad'arta " Zooly menene dalilinki nak'in yimana magana? Bayan duk maganganun da muka miki?" .

"Rayuwarmu ba iri d'aya bane Ruky tun farko ninayi gangancin shiga cikinku amma yanzu Allah ya ganar dani duk wani wajen dazaku dan Allah kuna tafiya kawai batare da kunzo guna ba ku manta da mun tab'a rayuwa tare pls na rok'eku" ta k'arasa maganar tana sharan k'wallah.

Eesha ce ta dube ta cikin mamaki kana ta yatsina baki " kinyi ganganci tun farko kuma yanzu is too late k'arya kikeyi ki shigo cikinmu kuma kice zaki fita ko da da ubanki ki kike yawa Zooly".
" Enough! Eesha duk iskancinki ya k'are a kaina amma banda iyayena dan bazan lamunta ba".

"Iyayenkin har wani value suke dashi da baza'a zagesu ba ? Matsiyata ne fa!"

"Eesh ya isa mana " Ruky ta fad'a cikin b'acin rai.
Tashi Zulaihat tayi ta tsinke Eesha da mari sannanta ta nunata da yatsa " ki fita a harka ta daga yau karna kuskura na k'ara ganin k'afarki ad'akin nan if not wallahi saina miki mummunan illah banza jaka kawai".

Sake baki Eesha tayi tana jin furucin Zooly wanda da alama bata cikin hayyacinta.

Jan hannunta Rukky tayi sukayi waje ransu gaba d'aya ya gama b'aci.

Durk'ushewa awajen Zulaihat tayi tasa kuka mai tsanani tayi kaicon rayuwar da tayi a baya gashi a banza taja wa mahaifinta zagi wanda yake kwance a cikin kabarinsa.



A maimakon tayi masa addu'a se gashi tasamu masu aibatashi.

A take ta k'arajin gaba d'aya rayuwarta fita mata arai gab'a d'aya duniyar batayi mata dad'i nadama da danisani su suka addabi zuciyarta.


Daga ganin fuskokin su Ruky Jibson suka gane akwai matsala, saboda sun dad'e kuma basu fito da Zoolyn ba.


Kb ne yace " akwai matsala ko?". Girgiza masa kai Ruky tayi alamar eh.

" wai meye yarinyar nan takeji dashi ne da zatana mana haka?". Big boy ya fad'a cikin b'acin rai.
" me kuwa banda shegen Dr nan,yanzu dai ya akayi?" Jibson ya tambaya cikin sonjin abunda ke going.

Nan Ruky ta kwashe kaf abunda yafaru ta fad'a musu wani ashar Kb ya sake " lallai ma yarinyar nan tasamu kanta amma meye mafita guys?".

"Ai mafitar kenan mu b'atar da gayen nan sannan muyi sabon aiki a kanta tayanda zamu samu mu cika burinmu na kawar da k'ishin mu akanta".
Ihu suka saka sannan sukace "hege Big boy ashe kanka naja magarka tayi dai-dai yanzu next agendern mu shine b'atar da Dr".




*Anya kuwa zooly bata k'ara d'ebo ruwan dafa kanta ba?*



*shin abunda suka fad'a zai tabbata ko kuwa?*


*anya kuwa Dr zai iya satuwa?*


Ku biyo mu danjin yanda zata kaya.





*Sweerry ce*πŸ‘ŒπŸ»

RAYUWAR HOSTEL PAGE 19

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page 19 by
Maryam S bello

Haka Dr Maheer yana ji yana gani ya tari machine ya hau ya tafi asibitin don neman da ake masa.
Sai da ya gama abinda yajeyi sannan ya d'auki mechanic suka hau machine tare suka biya dole sai da ya siyo taya guda uku kasancewar yana da extra d'aya a booth nasa.
Sai da aka kwashe kusan awa ana fixing tayoyin motar kafin daga k'arshe aka gama. A ranar kud'in da Dr Maheer ya kashe ba kad'an bane.

Gidansa ya wuce yayi wanka yaci abinci ya d'an kwanta domin ya huta, tunani yakeyi tare da jinjina wannan al'amari na *Untouchables*
Duk yadda ya d'auke su sun wuce nan, kuma zasu iya aikata fiye da hakan ma. Amma ya kud'iri a ransa cewar bazai rabu da Zulaihat ba, saboda Allah yaga zuciyarsa  da kyakkyawar niyyarsa, yana sonta tsakani da Allah kuma yana son aurenta, don haka dole sai ya tashi tsaye ganin yadda zai 6ullo ma al'amarin.

Washe gari da yamma ya fito daga clinic zai tafi wurin Zulaihat, turus yaja ya tsaye ganin glass d'in  motarsa gaba d'aya an farfasa masa,innalillahi wa inna ilaihi rajiun abinda ya dinga fad'a kenan,sai da ya dauki kusan 3mnt a tsaye kafin ya iya d'aga kafarshi,gaban motan yaje ya tsaya yana k'areta da kallo.

A gefen glass din yaga an cusa takarda,cikin zafin nama ya ciro tare da bud'ewa,sako ya gani kamar haka:-

_dr maheer dafatan kaga aikin untouchables kamar yadda muka fad'a maka tun a farko akwai sauran aiki da zakaita gani_

_untouchables bama tab'uwa a koina dan baa banza muke bearing sunan muba_.
_Kuma duk wanda yayi yunkurin rabamu  toh sai dai ya gaji ya bari_.
_har yanzu kanada sauran daman da muka baka ka rabu da zooly ka zauna lapiya idan ba hakaba ba kaiba har ita zoolyn kuna cikin matsala_
*Don forget mune dai untouchables*

Yana gama karantawa ya yayyaga takardan tare da sauke wani nannauyan ajiyar zuciya.wayarshi ce ta fara ringing bak'uwar number ya gani ba tare da tunanin komaiba ya d'aga.

"Dr ya zaka yaga mana takardanmu,ai da ka aje zatai maka anfani wani lokaci,fad'a da cikawa shine aikinmu,bama fad'an abu bamu aikataba,ko kuma dan barazana,yanzu dai kanada zab'i uku,ko ka rabu da zooly dan tamuce mu kadai,danmu kawai aka yita ko kuma kayi kararmu ga hukumar mak'aranta,kasan ba koruwa zamuyiba,ko kuma kayita ganin b'arna da batancinmu,hhhhhhhhhhhh dont forget untouchables" Ruky ta k'arasa maganar tare da hura masa iska cikin kunne, kit ta kashe wayar ba tare data tsaya danjin me zaiceba.

*********
Abangaren zooly kuwa taci gaba dayin baya baya da shiga cikinsu Ruky,lectures ko yanzu tana zuwa ba kama kafan yaro,abu d'aya ne yake damunta yadda course mate d'inta suke mata,sun kasa sakewa da ita kullum ta shiga hall sai an samu masu zancenta,wani lokacin har nunata akeyi da hannu da baki,kullum sai dai taje can baya ta zauna ita kadai,ana tashi ko da sauri take fita,

Kamar kullum yauma an tashi daga lectures tana sauri ta koma hostel dan dr yace mata zaizo,kamar ance ta waiga can gefe ta hango dr yanata faman waya,wani farin ciki taji ya lullub'eta dan ita duk sanda ta ganshi tsintar kanta takeyi acikin farin ciki da annashuwa.

Shiko be gantaba yanata faman waya,ta baya tabi inda bazai gantaba, taje ta tsaya a bayanshi ta dauki wani dogon tsinke ta shafa masa a kunne,da sauri ya waigo tare da sosai kunne,dariya ta saki harda tafa hannu tana fad'in "na baka tsoro ashe dai kai matsoracine",katse wayar yayi yana dariya shima.

"har kin gama lectures kenan"?.

Bata kai ga bashi amsaba idonta ya Kai ga motar shii duk glass a fashe.
cike da kulawa tace "honey meya sami motarka?".

Cike da wayin cewa yace "hmm abu na buga bansaniba,"ya fad'a mata hakanne dan bayason ta shiga cikin damuwa.

"Dan Allah ka fad'amin gaskiya dr,nasan ba yadda zaayi ka buga abu duka glass d'in ya fashe haka,dan Allah ka fad'a min",tuni ta fashe da kuka cikin kukan take fad'in,"nasan wannan aikin su Ruky ne dan wallahi nasan zasuyi yafi haka,ta sanadiyyana kanata shiga cikin tashin hankali,asara kala kala kanatayi daga wannn sai wannan,dan allah ka rabu dani saboda kasancewarmu tare bak'aramin tashin hankali bane,wallahi nagode da kaunar daka nunamin, ta dalilinka na dawo hayyacina,bazan tab'a mantawa dakai a rayuwataba",kuka taci gaba dayi wiwi.

maganganunta ba k'aramin sanyayama dr gwuiwa suka yiba,sun tab'a masa zuciya sosai,yana matukar son zulaihat baya kaunar ya ganta cikin damuwa,dan yanzuma kukan da takeyi har ranshi yakeji.

Cikin karfin hali yaketa ba zulaihat hak'uri tare da lallashinta da kyar ya samu tayi shiru,nanfa ya dinga bata baki,ai kuwa ta tattara dukkan natsuwara tana sauraronshi saida ya gama tsaf tace.

"Dr maker ina matukar kaunarka kuma bazan juri ganinka cikin damuwaba,ni nasan halin su Ruky da rashin mutuncinsu, yanzu dukiyarka suke tab'awa gabafa lapiyarka zasu tab'a,wanda bazan juri ganin hakanba,nayi maka alk'awari duk rintsi bazan tab'a komawa cikinsuba,yadda in an mutu ba dawowa haka nima na fita daga cikinsu ba komawa",tana gama fad'an haka ta juya da sauri ta nufi hostel.

Haka dr maheer yaita kiran zooly amma ina ko waigowa batayiba,haka ta barshi a tsaye.

*Mmn khadijah*πŸ’…

*tirk'ashi readers gafa zooly ta bar dr maheer ko zasu rabun kamar yadda ta nema*
*kubiyoni dan jin yadda zata kaya*

*the untouchables*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 18

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*HERE IS YOUR PAGE MY AUNTIES*

*Aunty sakeena (Ummeen Yusrah)*
          *&*
*Aunty sadiya (Sadnaf)*
*you are so special in my heart i loves you loadi-lodi*❤❤❤❤❤❤❤

*Page 18 by:* *Faridat musa (swerry)*

Untouchables ne  zaune a majalissarsu suna shan iska kamaΓ± yanda suka saba,wannan ya wuce su zageshi wannan ya wuce suyi masa dariya..

Motar Dr Maher suka hango tana shigowa cikin harabar makarantar, dariya sukayi suka tafa,da alama da wani abunda suke k'ullawa.

Tashi sukayi cikin ta kunsu na isa da tak'ama, suka nufi wajensa.

Parking yayi cikin kwanciyar hankali ya fito zuciyarsa d'aya ba tare da tunanin komai a ransa ba.

Turus yaja ya tsaya ganin sun kewayesa, ko wannensu fuskarsa ba annuri ballantana walwala.

Jibson ne ya matso daf dashi ya kallesa shek'ek'e tun daga sama har k'asa ya kwashe da dariya.

Ganin abun nasu na rainin wayone yasa Dr cewa " wannan wani irin iskancine zaku zo kusani a gaba da dariya, ni sa'ankune?, wato iskancinku ya tashi daga kan students ya dawo kaina kenan? To wallahi ku sani bazan tolereting nonsense ba…".

"Heyy!! Enough Dr", Eesha ta katsesa ta hanyar dakatar dashi.

Kb yace "ba dogon turanci muke nima ba munzone danmu kashema concrete warning, akan zooly, ka fita a hark'armu bama son shishshigi a lamarinmu, daga yau ka fita a hark'ar Zooly if not u will regret".

Jibson yace "Zamu iyayin komai akan Zooly, saboda haka ka d'anja guntun mutuncinka da muke gani,tun kafin mu fara sauk'e maka buhun rashin mutunci".

Ruky tace " is better fa kabi advice d'inmu, in bahaka ba zaka wahala, inkunne ya ji…jiki ya tsira" tana k'arasa maganar tasa dariya.

Tsaye yayi kaman mutum-mutumi yana kallonsu, a zahirin gaskiya ya tsorata da lamarinsu, amma kuma bazai bari su gane hakan ba, danzasu iya raina sa, dariyan k'arfin hali yayi ."naji nagode da advice amma kuje da abunku bana buk'ata, kuma ku sani tarayyata da Zulaihat yanzu na fara ba gudu bajada baya".

"Ince haka kace ko?to mu zuba mu da kai muga wanda zaici riba".Ruky ta fad'a tana huci.

"Haka nace 'yan mata" ya fad'a yana kashe mata ido, ya ratsa ta gefensu ya wuce.

Binsa sukayi da kallo har ya k'ule sannan Big boy yayi k'wafa " Amma fa gayennan zaisan damu ya ke magana,sai mun zamo masa k'adangaren bakin tulu… guys muje ko" yana gama fad'a suka sa kai suka tafi kamar dama command d'insa suke jira.

Ab'angaren Zulaihat kuwa suna gama meeting d'insu tayi Hostel, kwanciya tayi da niyar yin bacci amma ya gagareta inta rufe ido ba abunda take tunawa sai Dr wani masifaffan sonsa takeji yana ratsa dukkan wani sassa na jikinta,ganinta na niman zaucewa ne yasata tashi ta d'auki littattafanta tayi skul area, _wannan kenan_.

**********************

Zaune yake a office d'insa yana duba wasu files da alama zaiyi aiki ne akansu, wayarsa ne ta fara ruri alamar tana neman taimako, da sauri ya d'auka yasa a kunne, a d'aya b'angaren akace ya zo ankawo patient a clinic d'insa ba yanda take tana ta bleeding.

Cikin sauri ya tashi ya rataya jakar lapton d'insa ya fita, wajen motarsa ya dosa.

Jiki a sanyaye ya tsaya ganin an sace masa dukkan tayoyin motan, gumine ya fara karyo masa, badan komai ba sai dan tunanin  nisan dake tsakanin inda yake da gate, gashi yamma tayi duk colleagues d'insa sun tafi.

Horn yaji anayi masa kaman za'a chire masa kunne, hmmm!! Sassauk'ar ajiyar zuciya yaja dan atunaninsa d'aya daga cikin abokan aikinsa ne, juyawa yayi da niyar ganin ko waye.
*untouchables* ya gani sunyi parking suna k'ok'arin fitowa, ji yayi kaman ya gudu amma ya dake kasancewarsa namijin duniya kuma na gaske.

"Barka da yammaci Dr Maherr" Ruky ta fad'a tana d'aga masa gira.
"Barka dai Ruky" ya bata amsa cikin zak'ewa.

"Hala fita zakayi yanda naga kad'au saurinnan ammafa saidai hak'uri d'azu munzo wucewa mukaga motarka anan, haka kawai mukaji mu sace tayoyin,ya ka gani abun yabada kala ko?" Jibson ne yayi wannan maganar cikin tak'ama da gadara.

"Wannan duk ba damuwa na bane kowa yayi na gari dan kansa,kuma kusani lokaci ya kan maimaita kansa *"kama tudini tudan"*ni dai fatana agareku shine Allah ya shiryeku". Yana gama maganarsa yasa kai ya fara tafiya.

" 'Dan dakata Dr " Kb ya tsayar dashi.
Big boy ya matso wajensa cikin sarsarfa yace " wannan d'aya ne a cikin d'ari ammafa inbaka fita sabgarmu ba,inka fita shike nan inko kak'i kenan casa'in da tara na baya".

Mtssss tsaki yayi ya girgiza kai yace "Allah ya shirya" ya ci gaba da tafiyarsa yana jinsu sunata haukarsu.

*Anya kuwa Dr bai d'auko ruwan dafa kansa ba?*

*shin da gaske Zooly ta shiryu ko da sauran rina a kaba?*

Ku buyomu danjin warwaran k'ullin dake ciki.

*Sweerry ce*πŸ‘ŒπŸ»

RAYUWAR HOSTEL PAGE 17

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘


PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*



*Wannan shafin nakune ga duk wata mai suna khadija da hafsat ina kaunarku matuka❤πŸ˜πŸ‘„*


*Page 17*
*by mmn khadijahπŸ’…*


Kwana biyu da sallamar Zulaihat aka sallami Eeshat itama ba laifi ta sami sauki sosai da yake ta samu kwararrun likitoci.

Zaune suke a d'aki suna hiransu."zooly ce tace hmmm nifa har yanzu inhar na tina abinda ya faru damu sai naji yarrr a jikina,wadan nan shegun mutane kamar wanda aka aiko?"

"ai inma aikosu akayi zasu gane sunyi kuskure babba a rayuwarsu,Alhaji Ali sabon kud'i yasa yan sandan farin kaya (SS) su bincikosu nasan wallahi in har aka ganosu zasu gane basu da wayau,danni kaina ina tausaya musu" cewqr Ruky.kamar jira ake ta rife baki sai wayar zooly ta dau ruri *Honey*shine abinda muka gani akan screen din wayar,cikin nutsuwa da soyayya dake wayarta dan saika kasa kunne sosai zakaji abinda take fad'a.

Eeshat kuwa kallan Ruky tayi suka buga tsaki a tare dan sun fahimci da Dr take waya sukuma ji suke kamar su soka masa wuk'a basa kaunar alak'arsu.

Sun dad'e sosai suna waya a karshe mukaji tace "owk sai kazo,love youuu" ta sauke wayar a kunne.

Duk wayar da tayi su Ruky suna zaune basu motsaba,bayan ta gama ne Eeshat tace "nifa wannan mutumin haushi yake bani naga sai wani shige miki yakeyi,toh maganar gaskiya wannan ba class d'inki bane,ai tuni kin wuce ajin wannan, keda kike a high class inake ina kula k'ananan kwari ,yanzu insu Alhaji suka ganki da wannan ai sai su rainamu,gaskiya karki ja mana raini,better change ur mind".


"fad'a mata dai dear,ko taji naki,dan naga bata d'auki nawaba" cewar Ruky.

Ita dai Zulaihat bata kulasuba sai murmushin da takeyi kawai,a ranta ko fad'i take ku kuke daukanshi a lower class,amma ni yafi min duk wani wanda nayi hurd'a dasu abaya.

Ringing d'in wayar Ruky ce ta dawo da ita daga maganar zucin da takeyi.

"hello Jibson,harkun k'araso.....owk ba damuwa gamunan zuwa yanzu".

 "kad'dai har sunzo cewar Eeshat.
"eh sunce muyi sauri,kunga ku tashi ku fara shiri tunkafin su k'ara kira,kun sansu da wutar ciki".

Cikin sauri Ruky da Eeshat suka hau shiri, wad'an nan shegun kayan nasu suka dak'ko kowacce ta fara k'ok'arin sawa,Zooly kuwa tana kwance ko gezau batayiba bare tayi yunk'urin tashi.

"sweatheart ki tashi mana ki shirya".

"sai kun dawo ni ina nan" ta fad'a ba tare data kalli inda sukeba.

Cak suka tsaya da abinda sukeyi,"me kike nufi da ke kina nan ?" Ruky ta tambaya tare da matsawa kusa da ita.
"tana nufin bazata ba mana" Eesha ta bata amsa.

Toh ai naga dai ba abinda zakiyi inkin zaunan ma,kuma wannan meeting d'in kinsan dashi tunda ba yau kika shiga cikinmu ba,please tashi ki shirya inba dai kuma da abinda kike nufi ba.


Tuna maganar da Dr ya fad'a mata jiya tayi,kamar yasan hakan zata faru,dama yace mata karta ce zata fita a cikinsu da k'arfi dan yasan zasu iya mata wani illan,tabisu a hankali amma dai ta rink'a baya baya dasu,sannan ya k'ara jad'dada mata ta rik'e azkar d'in daya bata sosai."i'm sorry da bacci nakeson nayi amma muje in'na dawo nayi.

Wata doguwar riga ta d'akko daga cikin wanda Dr ya kawo mata ta saka ta had'a da hijab d'inta iya guiwa,ba yadda su Ruky basu yi ba akan ta cire wannan kayan amma tayi kunnan uwar shegu dasu,ba yadda suka iya haka suka barta amma badan ransu yaso ba.


**********
A zaune suka sami su Kb kowa da kwalban lemu  a gabanshi suna zama Bigboy ya mik'a musu nasu tuni su Ruky suka fara sha,itako zooly tak'i sha dan tasan akwai k'waya aciki.bayan sunyi shaye-shaye da wasan banzan da suka saba, Kb ya tashi ya fara karanta agendan meeting.kusan duk akan zooly za'ai meeting d'in.
    Jibson ne ya fara magana ya dubi zooly ya ce "madam gaba d'aya fa mun daina gane kan ki, kin daina zuwa meeting regularly,gashi sai wani mugun dressing kike mana kamar ba big girl d'in da muka sani ba, haba sai kace ba zooly easy ba kamar wata matar liman? Gashi idan ana parties ba kya halarta. Gaskiya ya kamata ki gyara don wallahi mugun bada mu kike yi"
      Haka duk suka dinga kawo complains d'in su akan ta,ita dai tana zaune tana sauraron su amma bata ce komai ba har aka gama meeting d'in aka Watse.
     Bayan ta tafi ne Big boy yake cewa "ni fa ina ganin kamar wancan gayen na clinic ne yake warware mana tufka dole ne mu d'auki mataki a kanshi". Kowa ya yarda da wannan shawarar.
     Daga nan fa suka fara shirya irin tuggun da zasu had'awa Dr har sai zaman school d'in nan ya gagare shi.



*Tou Dr maheer ka tab'o UNTOUCHABLES  mu sai dai muyi fatan abun ya zo maka da sauk'i*


*Untouchables*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 16


🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘


PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*




*Page 16*
*by mmn khadijahπŸ’…*


K'okarin take ta tuna inda tasan wannan fuskar amma abin yaci tura,katse mata tunanin yayi da cewa."sunana dr Maheer ina aiki a clinic dake school Ι—inku."owk tabbas a clinic nasan fuskar nan ta faΙ—i a
 zuciyarta.

Dr Maheer ya cigaba da cewa na fito yin uzirina ba zato naga abu ya faΙ—omin ta sanadiyya haka na kaΙ—eki,shiyasa na Ι—akkoki na kawoki private hospital Ι—ina.

"tnx ta faΙ—a a hankali.
Kara duba kafar yayi sannan ya fuce.

Kai gaskiya na auna arziki,ni wannan kaΙ—an alkhairi ta zama mini,dan bacin ita bansan me waΙ—an nan mazan zasumin ba,Allah sarki Eeshat ko kina wani hali oho,Allah yasa basu miki komai ba,katse  mata tunanin yayi da cewa.

"me kuka fitoyi cikin daren nan?kuma ina zakuje??.

"rasa abin faΙ—a tayi sai kai ta sunkuyar k'asa tana dana sanin wannan fita.

Jin tayi shiru yasa Dr cigaba da magana,taya zaayi maza bazasu biyo kuba,kuna fita cikin dare sannan da irin wannan shigar,ta iya yuyuwa da kunyi shigar mutunci bazasuyi attemting zuwa wajenkuba,amma duk wanda ya ganku a irin wannan dare da kuma irin wannan shiga dole zai raya wani abu aransa game daku,dan allah  ki kiyaye badan komaiba kodan kula da lapiyarki,dr Maheer yaa Ι—au lokaci yana ma zooly nasiha kuma maganganunshi da alama sun ratsata dan har kuka saida tayi,haka ya tafi ya barta jiki duk a sanyaye.


4:00pm dr ya dawo dakin Zooly dan k'ara dubata,bayan yayi komai ya gama har zai fita Zooly tace dr pls inason ka taimakeni.

"Wani irin taimako kike nema.

Gyara kwanciya tayi sannan tace "gaba kaΙ—an da inda ka kaΙ—eni na bar k'awata a wajen da sauran mazan da suka taremu,sannan motata tana wajen don allah ka taimaka kaje ka dubamin ta karasa maganar tare da fashewa da kuka.

"owk ba matsala daga nan can na nufa insha allah stop crying.

"tnx,nagode dr.

Office ya shiga da sauri ya Ι—akko key na mota ya nufa inda Zooly ta masa kwatance.

Yana Zuwa kuwa yaga motar a gurin sai dai kuma ba Eesha kamar yadda ta faΙ—a,yayi dan dube dube ko allah zaisa ya ganta dan har k'asan motar saida ya duba amma wayam bega kowaba.

BuΙ—e motar yayi ya fara bincike acan kasan kujera ya hango waya beyi sanyaba ya dakko ya buΙ—eta saboda a kashe take,kamar jira ake ya buΙ—e wayar aiko saiga kira ya shigo, sweatheart ya gani akan screen Ι—in wayar be kulaba haka ya barta ta karaci ringing harta katse shiko yaci gaba da bincike a cikin motar  ko zai samu information akan Eesha.

Saida akai miss calls uku kafin ya Ι—aga,assala......."katse masa maganar akayi daga can Ι“angare da cewa zooly kina ina inata nemanki wayarki bata shiga,nashiga tashin hankali gani a asibiti nida Eesha ba yadda take mazan da suka tareku duk su huΙ—un saida sukai mata fyaΙ—e, sannan sukasa reza suka farka mata gabanta saboda rashin kunyar datayi musu wani bawan allah ne ya tsinceta a yashe shine ya kawota asibiti dajin muryar Ruky kasan tana cikin tashi hankali.

"yanzu kuna wani asibiti dr maheer ya tambaya.

"wayyo na shiga uku malam dan allah ina zooly dama dakai nake magana bada zooly ba,plsease where is she?karkacemin wani abu ya sameta please i beg of you.
"dakyar dr ya shawo kan Ruky tai shiru ta saurareshi be Ι“oye mata komai akan abinda ya faru da zooly ba,nan ya bata address Ι—in asibitin da zooly take ahaka sukai sallama.

Haka Ruky taci gaba da jinyar k'awayenta koda yaushe tana hanya bata asibitin da Eesha take bata asibitin da zooly take.

Shima dr maheer ba'a barshi a bayaba wajen kula da zooly,ya bada lokacinshi sosai a wajenta kuma in har yaje Ι—akin saiya mata nasiha cikin siyasa,ahankali nasiharshi ta fara tasiri a zuciyarta dan har mamari take yazo.

Dr maheer ya gano zooly tana jin daΙ—in nasihar da yake mata dan haka saiya canza salo ya farayin duk wani abu da zaisa ta soshi,zooly batai auneba taji son dr ya fara shiga zuciyarta.

Haka lamari yacigaba da kasancewa tsakanin dr da zooly yanzu in ka gansu zakace sun shekara tare dan ba karamin shakuwa sukayiba.

Yau itace ranar da aka sallami zooly dan saida tai sati biyu a asibiti.siyayya sosae Dr ya mata sannan ya kaita har bakin Hostel,basu tsaya wani hiraba dan yana sauri haka sukayi sallama ta shige ciki.


Bata sami kowa a Ι—akinsuba suna wajen wani programme da akeyi acikin sch dan haka ta baje Ζ™Ζ™ledar da dr ya bata.

Kayane sosai aciki wanda ya haΙ—a da dogayen riguna normal ba irin wanda take sakawaba masu nuna shape Ι—in jiki,takalma da turaruka ,wani murmushi ta saki mai ciki da love kamar a gaban dr take."allah sarki my honey insha allahu zan cika maka alk'awarin dana Ι—auka, bazan sake shigar da be kamataba,zanyi kokari in koma *zulaihat* Ι—ina ta asali.

Yanzu ba laifi zulaihat ta shiryu dan kusan kowa ya fahimci haka kota yanayin shigarta,kayan da dr ya bata shi take sawa da wasu Ι—inkuna na atamfa datayi amma suna kama mata jiki,gaba Ι—aya ta daina fita da gyale sai hijabi.


*toh zulaihat allah yasa dai ba tuban muzuru kikayiba*
*ina labarin su ruky da kawarta a asibiti ku biyomu danjin ya aka kaya*

*the untouchables*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 15

🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘


PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page15
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ*


     Ya Dad'e tsaye a wajen hana tunanin abinyi har ta gama lectures d'in ta fito,sai dai kash tana fitowa yaga ta nufi inda untouchables ke zaune suna tata rashin mutunci, a duniya ya tsani yaran don ya kula basu da mutunci kuma da alama sun Gagari kowa a school d'in.
     Ganinta tare da su ba k'aramin sanyaya masa guiwa yayi ba, daga gani she's part of them, sai dai kuma she looks soo innocent, bata yi kama da lalatattu irin su ba.
     Haka ya juya ya shiga motar shi zuciyar shi a jagule,ya rasa abinda ke masa dad'i a duniyar nan. Tambayoyi ne fal Cikin zuciyar shi, shin ita wacece ne? Kuma menene alak'arta da Wannan sangartattun yaran marasa tarbiyya? Lallai dole ne ya San yanda zai raba ta dasu tun kafin suyiwa rayuwar ta illa ( muko muka ce zancen yaushe?)
     Haka ya shiga gida yana ta faman tunani da Neman hanyar da zai bi ya samu information a kan ta.


*** *** ***
       Da dare misalin 12:00am Eesha da zooly na ta faman shiri zasu je birthday d'in wata k'awar su, sun yi shiga ta rashin arzik'i, kan nan yasha attachment. sai dai inda zooly take burge kowa bata tab'a shafa wani mai da zai jirkita mata complexion ba, bak'a ce kuma she's proud of her colour don a cewarta "black Is beauty".
      Ruky bata nan sunyi tafiya da wani Alhajinta.
       Kowacce ta cokala uban takalmi suka fito, da motar Zulaiha zasu tafi don haka ita ke driving,suna cikin tafiya sai motar ta tsaya a tsakiyar hanya, iyakar k'ok'ari sunyi wajen ganin motar ta tashi amma Abu ya gagara, suna nan tsaye sai suka ji alamar ana tahowa wajen su, d'aga kan da su yi sai gani suka yi wasu manyab maza sun kewaye su suna fadin" 'yan mata ya akayi ne? Motar ce ta tsaya," dayan ya kai hannu kan bum d'in Eesha ya ce WoW "amma fa akwai ki da kayan aiki" Eesha ta buge masa hannu ta ce "kai Dalla ja can da wani tsamin hannun ka kana tab'a mutane,mannerless human being kawai".
     Lashe inda ta buge d'in yayi had'i da kallon ta ya lashi leb'enshi ya ce "ina son jarumar mace kamar ki".
     Ita kuwa Zulaiha gaba d'aya ta gama tsorata da ganin Wannan bayin Allah, hankalin ta gaba d'aya a tashe yake,jikinta sai rawa yake yi tana faman had'a gumi.
      Da taga abun na Neman ya fara nisa sai ta ce musu "Dan Allah kuyi hak'uri kar kuyi mana komi wlh Indai kud'i kuke so da motar duka zamu Baku amma kar Ku mana komi please I beg of you".
     Wanda da alama shi ne babba a cikin su yace "Ai 'yan mata baki da kud'in da zaki bamu ya kashe mana thirst d'in da muke ciki a yanzu, kawai Ku D'an bamu abun duniya mu D'ana don ni da ganinki na kwad'aitu da ke sosai" ya k'arasa maganar yana mik'a hannu kan bust d'inta da suka yi tummm a cikin Riga sleeveless,sai kuma leggings da ta saka daga k'asa,ita kuwa Eesha bum shorts ne a jikinta da wata top wadda ko cibiya bata rufe mata ba.
       Zulaiha kuwa Ganin ya mik'o hannu zai tab'a mata bust ya sata ja da baya tana mai nadamar fitowa a wannan uban Daren ga su babu suturar arzik'i a jiki,sai yanzu taga wautar su Daba su bi su j.b ba suka taho su kad'ai.
      Ganin tana na ja baya ya sa shi sake mastawa kusa da ita da niyyar kai hannu jikin ta,Ai bata San sanda ta ranta a na kare ba, mutum biyu suka rufa mata baya.
     Gudu take a kan titi ba tare da sanin inda zata je ba, ga uban takalmi a k'afar ta Wanda idan ba k'wararriya ba tafiya ma ba lallai mutum ya iya da shi ba, amma ita har da gudunta,ana haka ne ta gurd'e k'afa dunduniyar takalmin ta cire,amma ina Zulaiha bata tsaya ta bi ta kan k'afar ba haka ta ci gaba da gudunta.
       A dai-dai kan kwana bata Ankara ba sai kawai jin wani Abu tayi kamar an jona mata electric shock,daga haka bata sake sanin inda kanta yake ba.
      Su kuwa ganin haka yasa suka koma inda suka bar Eesha da wasu mutum biyun har sun turmushe ta suna k'ok'arin raping d'inta.


*********

     A hankali ta bud'e idonta,ta ga fanka na jujjuyawa, sai da ta gama zagaye wajen da idon ta kafin ta gane wannan d'akin asibiti ne, sai a lokacin ta tuna  abinda ya faru.
      Tana cikin tunanin wane hali Eeshat take ciki sai ta ji an turo k'ofar d'akin,takai duban ta ga k'ofar don ganin wanene?
     Sai taga fuskar kamar ta tab'a ganin shi, to amma a ina? Tabbas he looks familiar,kafin ta kai ga tuna inda ta sanshi ya ce mata "malama ya jikin?"
      Voice d'inta a dashe tace "da sauk'i".
 "to Allah ya k'ara sauk'i"
"Ameen".
"Yanzu ina ne yake miki ciwo?" Tace "k'afa da kai".
     Sai a lokacin ne ta tuna Ashe fa ta gurd'e da takalmi,ta kai duban ta ga k'afar taga an nad'e da bandages.


*Tou mu dai sai mu ce Zooly Allah ya k'ara lafiya, Amma shin waye  Wannan da ya kad'e zooly? Kuma ina ta San shi? Shin me ya faru da Eeshat a wannan Daren? Shin Dr.maheer zai sake had'uwa da zooly kuwa? Idan sun had'u ya zata kasance?* _Ku biyo mu don samun wannan answers din._


*pure moment*

RAYUWAR HOSTEL PAGE 14

🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘


PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

Page14
*ʍʀs Κ„aΥ‘Υ‘aʐ* 😘

       Haka Ruky da Eesha suka dinga sake dulmiyar da zulaihat, sai tayi kamar ta saduda sai su sake mayar da ita ruwa,zaman hostel d'in ma ba sosai take yi ba don su Ruky basa son su barta a hostel don kar a samu masu gaya Mata gaskiya.
     Ana haka Rannan zooly ta tashi da wani matsanancin ciwon ciki da fever Wanda ya sa ta bata bi su Ruky yawon gal-gal d'in su ba.
      Tana kwance a d'akin sai ga fatima ta dawo daga lecture,tayi mamakin ganin zooly a hostel d'in , don rabon data kwana a hostel harta manta,k'arasawa tayi ta dafa ta tace "zulaiha ya dai na ganki a kwance?"
       Ta ce "wallahi fatima am sick"
       Tace "subhanallah me ya same ki?"
   "Cikina ke ciwo wlh ga tunda na tashi nake faman amai,ga fever sosai"
      Tace "eyya sorry dear, tashi na raka ki clinic a baki magani"
     Da k'yar Zulaiha ta iya mik'ewa,abaya kawai ta d'ora kan night gown dake jikinta,sai ta naΙ—e kanta da veil d'in abayar suka nufi clinic fatima na mata sannu.
      Suna tafiya ma Zulaiha haka ta dinga sheka amai a hanya.
       A haka har suka isa clinic d'in duk ta gama galabaita, da yake school d'in babba ce manyan doctors na zuwa 2 times a week,don haka a ranar sun yi sa'a doctor ya zo.
     Basu wani Dad'e ba suka samu ya gansu, a nutse yake ma Zulaiha tambayoyi itama kuma a nutsen take bashi answer yana rubutu a k'aramin card di'n dake gaban shiahi, sai da ya gama ya basu takaddar ya ce suje lab ayi mata test ,babu dad'ewa aka yi aka basu result suka dawo office d'in.
      Doctor ya duba yace " 'yan mata ya aka yi kika bari typhoid tayi miki wannan mugun kamu haka?"
      Bata ce masa komai ba sai dai tayi murmushi kawai ta sunkuyar da kanta k'asa.
      Magunguna ya rubuta mata sannan ya sallame su,sai da suka biya ta pharmacy suka siya sannan suka koma hostel Wanda dai-dai wannan time d'in ne su Ruky suka dawo tare da wani Alhaji mai K'aton ciki,ya sauke su.
       Tunda suka hangota  suka iso gareta suna fadin "baby ya aka yi ne naganki haka?" Wani mugun kallo Eesha tayiwa Fatima gami da ture hannun ta daga shoulders d'in Zulaiha, don tuntuni suka gano cewa tana gaya mata gaskiya.
      Fatima kuwa ganin haka yasa tace "Zulaiha Allah k'ara sauk'i bara naje shop" ta wuce sum-sum kamar munafuka.
     Zulaiha tace "to fateema tnx a lot", daga haka su Ruky suka rik:e ta zuwa hostel, Eesha ta bi bayan fateema da wani mugun kallo tace "I hate this girl" ,Ruky ma tace "wallahi kamar kina reading mind d'ina".
     
****
    A d'aya b'angaren kuma *Dr MAHEER* NE  kwance a kan tangamemen gadon shi,tunanin ta yabi ya Dame shi, haka kawai yake jin ya damu da lamarinta,da ita ya kwana a ranshi da ita ya tashi, yana son ya San halin da take ciki amma bai San ma ta ina zai fara Neman ta ba.
     Ganin tunani ba shine mafita ba ya sa shi tashi ya shirya ya nufi school d'in, ba shima da call a ranar amma haka ya tafi with the hope zai sake ganin ta.

 *** *** **

     Kwanan ta biyar tana jinya sannnan ta samu lafiya garau kamar ba ita ba.
   La'asar ce sakaliya, ansha ruwa an gama gari yayi dad'i,ganyaye sunyi green abin ban sha'awa,yanayin ya mata dad'i.
    Sanye take da short gown pink colour an rubuta *Bea* a gaban rigar da lemon colour,ta saka lemon d'in leggins, sai kuma veil d'in kanta shima lemon toms d'inta kuma pink.
       Tayi kyau sosai,da books a hannun ta, yau tayi ra'ayin shiga lectures d'in.
      Shi kuma ya fito daga clinic d'in don ya neme ta har ya gaji da nema ya hak'ura zai koma gida sai ya hango ta tana tafe tana rangaji kamar reshen bishiya a cikin yanayin damuna.
      Wani irin dad'i yaji ya mamaye mishi zuciya, yana nan tsaye yana kallon ta har ta shige lecture hall d'in.
     Sai da ta shige sannan ya dawo cikin senses d'in shi, gaba d'aya ta gama tafiya da imanin shi,lokaci d'aya yaji he's in love with her, sai dai bai so ganin ta da wannan dressing d'in ba sam.


*Ana wata ga wata kenan, shi dai doctor maheer ya ga matar aure, amma shin zooly easy zata amince da tayin shi kuwa? Shin akwai ma aure a agender dinta?, Ku biyo untouchables don ki ji yadda zata k'ark'e*