Wednesday 4 September 2019

RYAUWAR HOSTEL PAGE 22

šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜
*RAYUWAR HOSTEL*
šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜šŸ˜

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

```bamu rok'i kowa ya karanta novel d'in nan ba,amma a farko kafin mu fara sai da muka ce bamu yi don cin zarafin kowa ba idan yayi dai-dai da rayuwar da kike ciki muna miki fatana shiriya, to indai ba mutum ya San halin shi muke fad'i ba meye za'a fara bin mu da Allah ya isa? Idan kin Fasa zagin mu kin raina gyatumar ki kuma ke ba 'Yar halak ba ce, zagin ki da Allah ya isa ba zai sa mu daina tona miki asiri ba sai dai ma ki k'ara bamu k'arfin guiwar ci gaba da abinda a muka fara. Tunda kuma haka halin ki yake muna miki fatan shiriya ```

Page 22 by
*ŹŹ€s Ź„aÕ”Õ”aŹ*šŸ˜˜

      Daga wajen boka Ruky hotel ta koma direct inda Alhajin keta  jiranta.

      Sun Dad'e suna lalacewa kafin daga baya ta yakice shi da k'yar ta shige toilet domin yin wanka.

      Bayan ta shiga ne Alhaji ya d'auko wrapper 1000 notes guda uku ya saka mata a jaka,kawai sai hankalin shiya kai kan k'ullin maganin da ta karb'o d'in,haka kawai sai jikin shi ya bashi maganin nan shi zata yiwa amfani, don haka sai ya d'auke shi ya b'oye ba tare da sani ba.

      Bayan ta fito ta shirya da k'yar Ta samu ya barta ta tafi domin bai gaji da ita ba kawai dai Dan ta matsa sai ta tafi ne.

     Duban ta yayi yana wani kashe ido shi a Dole ga D'an bariki ya ce ke "Ruky shiga rai ne da ke wallahi gaki kuma da jan Aji,sai kin wana mutum kike bashi kayan dad'i"

      Wani fari tayi da ido ta ce "kasan shi gold ba a samun shi sakaka Dole sai an wahala"

     Dariyar k'eta yayi mata yace "haka ne babayna,amma da kin bari mun kwana gobe sai ki tafi"

     Ta ce "Gaskiya dole na tafi don akwai important abun da zan yi ba don haka ba da na kwana na k'arasa rikita maka lissafi"

      Wata dariyar ya sake yi had'e da D'an bugun bum-bum d'in ta yace "Ruky kayan dad'i",

tace "Alhaji naira".

     Har bakin mota ya rako ta ya ce mata "akwai sak'on ki a cikin jaka"

      Lek'a jakar tayi ta ce "I trust you Alhaji sai next week d'in"

       sai da ta bar compound na hotel d'in shi kuma ya koma ciki yana fad'in "yarinya ni wallahi na fi k'arfin wannan tsubbace-tsubbacen naki, yanzu da na d'auke maganin Ai naga da abin da zaki sihirce ni, ki mai da ni wani sha-sha-sha da k'arfi da yaji".

      A Daren ranar suka fita meeting around 1:00am Na dare,inda suna ganin Ruky suka fara hailing d'inta suna " The untouchable Ruky"

      Ita kuma sai bada fad'i take yi domin ta san ta samo musu solution na problems D'in zulaihat.

     Nan ta gaya musu yanda suka yi da boka, suka k'ara kaurewa da tafin murna ta ce "to yanzu ga magani sauran aiki kuma naku ne",ta nuna mazan.

      Zura hannu take a jaka da nufin d'auko maganin,sai dai me? Magani yace "d'auke ni inda kika ajiye".

     Abu kamar wasa fa Ruky ta nemi magani bata gani ba,don haka sai ta ce "guys ina jin fa na baro maganin nan a wajen boka ko kuma a hanya na jefar da shi"

      Gaba d'aya suka had'a bakin cewa "shit", big boy harda dukan hannun shi da jikin bishiya don ya gama cin buri.

      Ganin haka ya sa ta ce "Guys not to worry gobe insha Allah zan koma na duba maybe a can na baro, idan ma ba can bane sai na sake karb'o mana wani"

       Wannan ya sa suka D'an ji relief,daga nan kuma suka ci gaba da tsara yadda shi kanshi doctor d'in zasu b'atar da shi.

*wannan kenan*

No comments: