Wednesday 4 September 2019

RYAUWAR HOSTEL PAGE 13

๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜
*RAYUWAR HOSTEL*
๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*WANNAN SHAFIN NAKUNE MASOYA LABARIN RAYUWAR HOSTEL*๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜
*SAKONNINKU NA FATAN ALKHAIRI YANA ZUWA GAREMU*
*muna kaunarku aduk inda kuke❤❤*

Page 13
*by mmn khadijah๐Ÿ’…*

Gyara wajen kwanciya Fatima tayi ta kwanta,zooly kuwa k'ara shiga cikin kogin tunani tayi ahaka har bacci ya kwasheta.su biyu suka kwana a ษ—akin dan yau Ruky bata dawo hostel ba.

Da asuba suka tashi suka mik'a ibada,Zooly ce ta mik'e ta dakko alQurani ta fara tilawa.

Wani farin ciki Fatima taji ya lulluษ“eta,a take ta ษ—aga hannu tayi adduar neman shiriya ga kawarta Zulaihat.

Ta ษ—auki dogon lokaci tana karatu kafin ta rufe littafi mai tsarki ta tattara wanki ta nufi bakin fanfo kasancewar yau sunday.mu dai muna gefe munata tunanin ko nasihar fatima ta shiga jikin zooly ne.

Ta taradda mutane a bakin fanfon kowa da abinda yakeyi,wasu wanki wasu wanke wanke,wasu na gefe suna ta kitso,wasu kuma hira sukeyi.ajiye bucket ษ—in tayi akan layi ta koma gefe kafin a iso kanta.

Salma dakema Husna kitso tace,yawwa Husna kinga yarinyar da ake taษ—i jiya a
Room 14,da sauri Husna ta ษ—aga ido tace laaa wallahi naganeta,kiga sanda ta shigo makarantar nan very gentle bazakice zata aikata abin duk da kuka faษ—a ba.

"iyi ba ta biyema yan iskan yaran nan ba *untouchable* yarinya da mutuncinta da komai,ni shiyasa wani lokacin bana ganin laifin iyayen da suke hana yaransu ci gaba da karatu,saboda ba kowace yarinya bace ke iya rik'e mutuncinta,sai kiga yarinya ta fito daga gidan tarbiyya amma tana shiga manyan makarantu sai ta ษ—ai ษ—aice,ko rantsuwa zan iyayi nasan iyayen yarinyar nan basu san abinda takeyiba.

"Husna ce tace ke salma kiyi a hankali fa tana jinmu,."yoo tajiman ai nafison taji,ai ni bacin karta min wani fassara dana sameta na mata nasiha.

Dariya suka kwashe gaba ษ—aya haka suka cigaba da hirarsu kuma duk maganar dasukayi a kunnen zulaihat.

Gaba ษ—aya zooly taji ranta ya mata ษ—aci ta kasa gane a sama take ko k'asa,ko motsi kasayi tayi ta shiga kogin tunani.

"Sister ga naki can nasa miki ki matsa kusa watace ta faษ—a tare da taษ“a zooly.
"owk nagode.

Tana gama tara ta ษ—auki kayan ta mayar ษ—aki dan ji tayi zazzaษ“i na neman rufeta,sai da tasha kukanta sannan bacci yayi awan gaba da ita.

12:00pm su  Ruky suka dawo cike da zumuษ—i suke tashin zooly,baby dan Allah ki tashi akwai news,dakyar ta iya tashi ta zauna fuskar nan ba walwala kamar wanda aka aiko ma da manzon mutuwa.

"Cikin haษ—in baki da nuna kulawa sukace baby baki da lpy ne?,.

"kai ta jijjiga alamun a'a.
"toh meya sameki?
"bata ษ“oye musu komai ba haka ta kwashe duk abin da taji ta faษ—a musu sannan ta k'ara da cewa ni yanzu nadama tazo mini,zan dena komai,zan yarda duk wani makaman iskanci , zan koma zulaihat ษ—ina ta da,zanyi k'okari in cikama iyayena alk'awarin dana ษ—auka.

"Mtsss amma sweatheart kin bani mamaki,bansan har yanzu kinada k'arancin wayewaba,ashe bazaki iya tantance masu sonki da kuma masu miki hassada ba,toh wallahi wannan yarinyar bak'in ciki take miki,taga dare ษ—aya Allah ya ษ—aga darajarki,kin mallaki abubuwa da dama.

 abinda har ta mutu inba wani ikon Allah da tsananin raboba ba  lallai ta mallakesu ba,ko tantama banayi inda zata sami damar da kika samu bazatayi wasa da ita ba.

baby ki cire duk wani tunani a ranki ki tsaya ki kwashi arziki,kiji daษ—i, ki fantama, ki wataya, Ruky ta k'arasa maganar tare da kai mata kiss.

"Easher ce tai caraf tace baby ki nunamin yarin nan ko yar gidan uban waye,wallahi sai na mata cune,saita gane munci sunan mu na *untouchable*

"no ba za ai hakaba barta kawai na gane talauci ke damunta,yanzu kawai a ษ—aura daga inda aka tsaya.

"shiyasa nake k'ara sanki babyna,allah dai ya bar mana love.

Toh fa readers har yau dai akwai sauran rina a kaba,dan ga dukkan alamu zooly bata ganeba,muje zuwa...

*jannart Allah ya k'ara lapiya,yasa kaffara ameen*
*maryam muh'd lawal*๐Ÿ’…

No comments: