Wednesday 4 September 2019

RYAUWAR HOSTEL PAGE 08

🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘
*RAYUWAR HOSTEL*
🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘🏘

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
        P.M.L

Na

*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO*
*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA*
*JANNAT LAMEED'O*
*RUFAIDA YUSUF*

*hmmm wani kaya sai amale sahun giya yatake na rak'umi pure Ikon Allah kainuwa dashan Allah, mun wuce sharrin mai sharri nangani nanbari d'umaman mayyah*
       Up
             Up
                    Up
Pure moment this gouges page to u oll😍

 *Page 8 by:*
*jannart lameed'o*
   (Babyn garkuwa)

K'arfe 5 Zulaihat ta farka daga barci ,bakin ta d'auke da salati, a hankali ta sauko daga kan gadon tanufi toilet danyi alwala, bata wani d'auki lokaci ba tafito daga toilet d'in,
      Sallah tayi tukunna ta fara lazimi har wajan karfe 7, har zuwa wannan lokacin Rukky barci take sha hankali kwance,
     Zulaihat kuwa damuwan duniya ta damai tah, tunani take yadda wannan Abu ya kasance batare da sanin ta bah , wasu zafafan hawaye suke zuba akan face nata , zuciyan ta sai zafi yake mata a hankali take furta,
  "Astagafurullah, Allah na tuba, Allah kaya femun, rashin sani ne"
   Ta kuma fashewa dawani sabon kuka tare da kifa kanta kan dadduman da tayi sallah,
  Kukan Zulaihat shine ya farkar da Rukky daga barci , aikuwa tana bud'e ido tayi tozali da Zulaihat sai aikin kuka take, dasauri Rukky ta duro tanufi wajan Zulaihat, ta kama hannun ta dukka biyu,
     "Maiya faru haka Zulaihat sai kuka kike ko Ummah ce ta rasu"

  a hankali Zulaihat ta d'ago jajayan idon ta ta d'aura su akan na Rukky wacce ta kafai ta da ido tana sauraran ta,
   "Yanzo abunda kika mun Rukky kin kyauta kenan? Daman kin kawoni nanne danki b'atamun rayuwa? Kin cuceni Rukky wallahi sai Allah ya sakamun"
  Dasauri Rukky ta d'aga mata hannu cikin masifa,
   "Loook Zulaihat daman kafin na baki kud'in da za'ayi aiki wa Ummah ae saida na fad'i miki sharad'i, to wannan shine sharad'i Nah"

   Tana kaiwa nan tayi shige toilet ba tare da takuma sauraran Zulaihat bah,
   Kasa magana Zulaihat tayi sai tsananin mamiki Wanda ya fureta lokaci guda, tana nan zaune Rukky ta fito daga toilet d'aure da towel a jikin ta bakin gwado tana nufa tare da jawo mai tafara shafawa,
   Ta maida kallo ta wajan Zulaihat wacce tayi zugum tana ganin Ikon Allah, tashi tayi tare da komai kusa da itah,
    "I'm so sorry Zulaihat nima banso haka ta faru ba nayi iya kan k'okari wajan danna bukatata Amman abun ya gagara , 4 give me Sweetheart"
   Ta karashe maganan tana kukan munafurci dasauri Zulaihat tarike hannu ta
     "Babu komai na yafe miki Rukky Amman kiji tsoran Allah karki kuma aikata hakan akan kowace, sannan mu dage wajan naiman yafiyan ubangijin mu"

    "Insha Allah Zulaihat, yanzo tashi kiyi wanka kafin na samo manah karin kumallo"
     "To"
Zulaihat tace sannan tanufi toilet d'in, tana shigewa Rukky tayi dariyan mugunta,
   "Zakici ubanki kuma wasa farin girki yanzo muka soma shegiya kawai"
  Tasake fashewa dawani dariyan , sannan tayi shirin ta ta fita Dan sama musu Karin kumallo, Ikon Allah babu zancan sallah kuma Allah ya kyauta,
  Bata wani jima ba ta dawo d'auke da tekaway a hannun ta, tana shiga ta taran da Zulaihat harta gama shiryawa Amman fuskanta babu walwala ko kad'an zama tayi ta kafe Zulaihat fa ido tana jin wata sabuwar sha'awan ta mai karfi, cikin sarke wan murya ta farah magana,

    "Sauk'o muci abinci Zulaihat saimu komai skull"
   "To" kawai Zulaihat ta iyah cewa,
   Cin abinci kawai take Amman a zahirin gaskiya d'aci abincin yake mata kaman wani magani,
haka de suka gama cin abincin kowa da sake_sake cikin ransa,
   Bayan sun gama ne suka hada kayan su sai skull suna shiga d'akin su Zulaihat ta zube kan katifan tayi shuru Rukky kuwa suna ajiye kayan su tace wa Zulaihat zata je sayo maganin ciwon kai tayi ficewar ta,
  Zulaihat kuwa tunani ta cigaba dayi har barci b'arayo yayi awun gaba da itah,
   Rukky kuwa tana fita wajan su Big boy tayi daman sunyi waya akan zasu had'u yau a wani hotel dake bayan skull d'in su,
  Tana isah suka saka iho, Big boy ne ya fara magana,

   "Rukky baby manyan mata duk wacce ta ja dake saita mutu sakara,"
   Dariya Rukky sannan tace,
   "Fad'i ka kara fad'i wannan haka yake ni inuwan giginyace duk kuwa wacce tayi kokarin shiga gonata baxata ga da kyau ba"
 
  Jibson ya amshe
"Baby mufa kinsamu a duhu Dan wallahi a matse nake da yarinyan gwara kimana bayani"
   "Shege Jibson ba'a wasa da harka ni nafika kwad'etuwa da yarinya danni wani sa'in har  mafarkin ta nakeyii"

   Cewa KB, Eesha ta amshe,
   "Mufa duk ba wannan a gaban mu, kubari muji kan bayani tukunna, Dan babu wacce batason kasance wa da yarinyan"
      Dariya Rukky ta kwashe dashi  tayi mai isarta sannan ta tsageta, ta kwashe duk yadda sukayi da Zulaihat ta fad'i musu sannan ta d'aura da cewa,
    "Amman nima bangaji da itah ba don wallahi yarinya daban take cikin sauran matan danayi mu'ama da su, kuma saina sake samun ta akaro na biyu"

Tofa masu karatuπŸ€”anya kuwa Rukky zata nasara akan Zulaihat karo na biyu kuwa? Kubiyo mu danjin yadda za'a kaya,

*pure moment*

No comments: