Tuesday 8 August 2017

AUREN FANSA 35

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS

 _We don't just entertain and educate, we touch the heart of readers_

P.M.L

     
                🌹35 🌹
   
http://MaryamSBello.blogspot.com


Washe gari aka kai lefen Zarah akwati bakwai da kit, yayinda aka kai ma Jidda akwati takwas da kit.

An fara gudanar da shagalin biki a wadace, sai dai matsalar Jidda d'aya da ta masa maganar kud'i sai sunyi fad'a, sannan idan har suna tare yana nuna mata so da k'auna marar iyaka amma da zarar sun rabu shikenan ko kiranta baiyi sai dai ita ta kirasa. Hankalinta ya fara tashi haka kuma ta soma tunanin ko maganin ya fara dena aiki ne?

Ranar da akeyin event d'in Jidda anyi kwalliya ta gogaggun 'yan matan nan, ta had'u har ta gaji duk da ba wani kyau gareta na azo a gani ba. 'Yan matanta kansu da ka kallesu kaga gagaggun 'yan mata masu ji da kansu, Luby best friend d'in amarya ita nata ashobin ya banbanta da na sauran ya kuma fi tsada da kyau.

Suma kuwa su Zarah na can suna shan tasu hidimar, da yake bazasuyi abubuwa da yawa ba, kuma bikin nasu yafi tsari da kyau.

K'arfe biyar da rabi Faruk ya iso ya kira wayar Jidda, can sai ga ta fito itada k'awayenta su da yawa kamar wata tawaga.
Bayan sun iso aka fara gabatar da events cike da kwanciyar hankalin, Luby ita ta fara bud'e wurin da rawa yadda kasan ba kowa wurin haka take tik'ar rawa ba ko kunya.
An gayyato amarya da ango don taka rawa, shi kam ango kunya ta hana shi rawa sosai ba, ita kuwa amarya bako kunya sai wani rausaya takeyi kamar ba amarya ba. Faruk sai yanzu yake k'ara gane halin Jidda, bai ta6a tunanin haka take ba. Sai yanzu ya fara tunanin aurensu shida Meenah komai cikin tsari haka akayi shi.

K'arfe sha d'aya aka tashi taron, ya ajiye Jidda gida shima ya nufi nasa gidan.
Washe gari ya tashi yana ta hidimar d'aurin aure. K'arfe biyu daidai dubban mutane suka shaida auren Jidda da Faruk sai Zarah da Khaleel.
Dad'i Meenah takeji Zarah kusa da su za'a kawo ta, bayan an gama aka zarce 'yar walima da Faruk ya had'a masu.


****

Tana zaune  kan gado taji ana maganar an d'aura aure, haba kanta ya k'ara girma ji take kamar a mafarki, mutumin da take ganin shine class d'inta yau ta malleke shi a matsayin miji, wani murmushi tayi tare da lumshe idanu, Luby ta daka mata duka a baya tace
"Banza keda wa kike murmushi ke kad'ai?"
Ta dube ta tace
"Ina tunani gami da yin mamaki wai yau nice na zama matar ya Faruk ya zama mallakina fa kenan?"
Luby tace
"Ke ni ba wannan ba, kinsan mutumin nan yana da mata, kuma kinsan yadda yake k'aunar ta kawai suddabarunki ne yake aiki, baki gudun maganin ya bar aiki mu shiga uku mu lalace? Ke nifa na fara ji miki tsoro kar ya wulak'anta ki, sannan yasan babu, baki gudun labari yasha banbam?"
Ras ras! Gabanta ya yanke ya fad'i tace
"Haka ne fa, ko da yake ay kin min tanadi mai kyau kar kiji komai."
Luby tace
"Keni sheyasa nake son auren yaro wanda baisan dawon garin ba, amma masu mata ay sun san komai."


Haka aka cigaba da shagalin biki, jikin Jidda yayi mugun sanyi saboda gudun abinda zaije ya dawo tsakaninta da angonta.
K'arfe tara da rabi motoci suka soma layi a k'ofar gidan su amarya, bayan fad'a da nasihohi daga Mama da Dada har Faruk sai  da yasha fad'a sosai da nasiha.



Uwar gida kan gida Meenah tana zaune a d'akinta ta ci ado tsayawa fad'ar kwalliyarta ma 6ata baki ne. Gud'a ta matan da suka rako amarya itace ta fara yo sallama, Meenah ta danne kishinta sosai ta k'ak'alo murmushin dole, amarya tana rik'e a hannun wata mata.
Kansu tsaye d'akin amarya suka nufa, 'yan kawo amarya, k'ofa ce kawai zatayi linking d'inka zuwa d'ayan 6angaren na sashen Jidda.
Masu kawo amarya suka shiga zagaye gidan don kashe kwarkwartar ido. Suka gama kallon komai sukayi niyyar tafiya gida.


Washe gari akayi walima k'arfe biyar na yamma Hajiya Lami ta rik'o hannun Jidda ta nufi parlon Meenah, sukayi sallama Meenah ta amsa. Hajiya Lami ta ce
"To ga amarya nan don Allah ku had'a kanku ku zauna lafiya, yanzu an bar haukan kishin nan zaman lafiya shi kowa ke buk'ata.
Tayi murmushi
"To Allah ya taya mu rik'o."
Suka tashi suka maida amarya d'akinta bayan iyayen sun kama gabansu, d'akin ya rage daga amarya sai 'yan matanta wad'anda ke zaman jiran ango.
Luby tace
"Kar fa kiganta kamar mutuniyar kirki ki raga mata, idan tace miki kul ki ce mata cas cas! Kinji na fad'a miki."
Nan sukayi ta zuga ta har akayi isha'i.
K'arfe takwas, tara, goma, shiru ba ango ba alamunshi, har dai sha d'aya ta wuce
Luby tace
"Nidai zan tafi gida na gaji da jiran ango."
Haka suka tarkata suka tafi, Sai dai ta dinga binsu da ido don batada bakin magana da kuma tana son jin dalilin rashin zuwan ango duk da tanadin da tayi masa, haushi kamar zai kashe ta.
"Kar dai yana wurin waccan tsinanniyar?"
Gabanta ya fad'i, ta hau sak'e sak'e, tayi ta kiransa yana rejecting, daga k'arshe ya tura mata sak'o kamar haka:
"Kiyi hak'uri ki bar kirana yau bazan shigo wurinki ba."
Ta rud'e ta gigice gashi maganin idan aka wuce yau shikenan ya kare!
Ta hau salati tana cigaba da kiransa amma ina sai ma ta kira taji ta a kashe.
Safa da marwa takeyi daga k'ofa zuwa gado, tana tunainin mafita a gareta, don akwai had'ari muddin ango baizo gareta ba a daren yau ba!



MSB💖

No comments: