Sunday 27 August 2017

AUREN FANSA 40

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS

 _We don't just entertain and educate, we touch the heart of readers_

P.M.L

     
                🌹40🌹
   
http://MaryamSBello.blogspot.com


Ya shigo gidan a lokacin da ya tarar da Meenah a bakin k'ofa, tana sanye da brown and cream atamfa d'inkin riga skirt, tayi kyau sosai, da sauri ta taro sa ya k'ura mata idanu yace
"My baby ya akayi ne?"
Yaushe rabon da taji sunan nan a bakinsa har ma ta manta, tayi murmushi tace
"Jidda ce tun d'azu banganta ba, ko da saninka ta fita?"
Ya kwashe labarin komai ya fad'a mata, tace
"Ikon Allah kenan, amma Jidda bata yi wa kanta adalci ba, amma sai inga duk bai kai na saki ba my soul."
Ya kamo ta suka dawo parlor suka zauna yana kallonta sosai yace
"Rabuwa da Jidda shine mafi alkhairi a garemu my baby, saboda a gaskiya bazan iya cigaba da zama da ita a matsayin matata ba, besides ba'a son raina na aure ta ba."
Ta dube shi cike da mamaki tace
"Bangane ba my soul."
Yace
"Wato akwai wata rana na fito zan tafi aiki sai naji Jidda na magana da mahaifiyarta tana ce mata ita ba wanda takeso sai ni, a nan naji Mama na ta rarrashinta akan tayi hak'uri tunda ni ba sonta nakeyi ba, tun daga wannan lokacin sai na karaya nake ganin kamar ban kyauta ba, abin yana ta damuna sosai, a ganina abinda kawai zanyi na faranta ransu shine na bijiro da maganar auren Jidda, a tunanina sun mani komai a rayuwa bai kamata d'iyarsu tana sona nak'i ta ba."
Meenah ta kamo hannunsa tana murmushi tace
"A gaskiya kayi tunani mai kyau kuma ka kyauta, sai dai daman tun farko kayi min bayani da sai nafi fahimtarka my soul."
Yace
"Naso yin hakan my baby, amma a lokacin sai na rasa dalilin da yasa na kasa fad'a miki gaskiya, kuma wallahi bansan yadda akayi ba sai dai naji ance wai matata ce, abin zai baki mamaki is like bansan abinda nakeyi ba, kuma a lokacin Jidda tayi amfani da magani wajen jawo hankalina gareta, nidai kawai idan ta warke zan sallame ta, taje can ta nemi wani daidai da ita."
Tace
"Bazan iya saka yin abinda baka so ba, duk abinda kaga yafi dacewa kayi ni kuma zan baka goyon baya d'ari bisa d'ari my soul."
Ya kamota ya rungume a k'irjinsa gami da lumshe idanu yace
"Sheyasa nake sonki my baby."
Tace
"Nima haka, yanzu muje kayi wanka kaci abinci ko, na dafa maka abinda kafi so."
Cike da jin dad'i yace
"Allah my baby?"
Tace
"Wallahi kuwa."
Yace
"Shikenan muje, don yau ma kece zakiyi min wanka da kanki."
Ta tashi tana fari da ido tace
"Muje."
Ta wuce yabi bayanta.



****


Yana zaune a office d'insa aiki yasha gabansa wayarsa ta fara ringing, ganin Hajir ya sanya ya dakata ya d'auka.
"Hello Hajir."
Tace
"Hello Sir ina wuni?"
Yace
"Lafiya lau, ya dai?"
Tace
"Aikinka na kammala komai Sir, yanzu ya za'ayi?"
Cike da jin dad'i yace
"Da gaske kin had'a komai da komai?"
Tace
"Yes Sir komai ya kammala."
Yace
"Wow Weldon Hajir, a gaskiya nayi matuk'ar farin cikin jin haka, yanzu abinda za'ayi, ki shirya zuwa gobe zan shigo gidan, dana kiraki sai ki fita daga shigar Atika ki koma Inspector Hajir d'inki. Sauran bayanin zan kiraki. Yanzu wani d'an bincike nakeyi akan wad'anda suka turo domin kashe iyayena, nama kammala don har na tura a kamo yaran, don muna buk'atarsu."
Tace
"Yayi haka sir, sai Allah ya kaimu goben."
Yace
"Amin, thank you."
Daga haka sukayi sallama, Faruk yayi murmushin jin dad'i sosai.


****

Kiran farko na sallar asuba a kunnensa akayi, domin ba bacci yake ba, saboda tsabar farin cikin kalar matar da Allah ya bashi, shi kwata kwata bai k'ara tabbatarwa ba sai yau, tambayar kansa yakeyi anya kuwa akwai wanda ya kai shi sa'a?
Ya lalubi bed side lamp sannan ya dube ta tana bacci, numfashinta yana fita a natse.
Kyakkyawar fuskarta nata annuri, yayi ta kallonta baya ko kyaftawa har sai da idanunsa suka kawo ruwa sannan ya dawo hankalinsa, ya sunkuyo a hankali ya manna mata light kiss a goshinta, ya numfasa, Allah kad'ai yasan tarin son da yake mata. Da k'yar ya lalla6a ya sauka daga gadon ya shiga toilet yayi wanka ya fito da alwalarsa, ya shimfid'a sallaya yayi nafilfili har alfijir ya fito, sannan ya nufi masallaci.


Yanda ya barta haka ya dawo ya same ta, yayi tsaye a gaban gadon rungume da hannayensa yana kallonta.
"Wai lallai baby an gaji."
Ya zauna gefenta ya tallabo kanta sannan yace
"Meenah... Meenah..."
Ta bud'e ido a hankali tabi shi da kallo har idon ya washe gaba d'aya. Yace
"Ki tashi kiyi sallah, ko gajiyar ce ta hana ki tashi?"
Ta runtse ido tana k'ok'arin tashi, yayi murmushi kawai ya d'aga ta cak sai toilet, ya tarba ruwa masu d'umi ya saka ta ciki, ita kuwa idonta har yanzu a lumshe yake, yana tsaye yace
"Haba ragguwa sai kace first time dai."
Tayi murmushi kurum, daga haka ya fita ya bata wuri don ta kimtsa.
Tsawon minti 20 tafito, ya matso yana dariya.
"Ragguwa kawai ni tuni naje masallaci na dawo."
Ta wuce shi tayi shirin sallarta tana jin wani irin nishad'i marar misaltuwa. Kwanciyarsa yayi, ta gama sallarta tayi adduo'inta gami da mik'a godiyarta ga Allah da ya karkato mata da hankalin mijinta gareta tana fatan su dauwwama haka har k'arshen rayuwarsu. Sai kuma ta tuna Jidda ko a wane hali take yanzu? Ta dad'e tana mata addu'ar samu sauk'i, tana gamawa sai kawai ta maida kanta bisa sallayar tana lazumi. Ya d'ago yana dubanta yace
"Ya zaki kwanta a nan?"
Tace
"Haka nan."
Yace
"To kodai?"
Ta k'udundune fuskarta da hijabi ta k'yale shi, cicci6o kanta yayi ya d'ora bisa jikinsa yace
"Tashi mu koma kan gado."
Tayi shiru tana kallon kyakkyawar fuskarsa, yace
"Allah yayi miki albarka my baby."
Taji dad'i sosai ta amsa da
"Amin my soul."
Ya cigaba da fad'a mata dad'd'an kalamai masu rikita lissafi, ganin haka yasa na tashi na baro d'akin, sai dai fatan Allah ya kawo k'azantar d'aki.



MSB💖

No comments: