Friday 6 August 2021

YAR AGADEZ PAGE 42

 YAR AGADEZ

 

 

              {Page 42}



To read all my books click the link below👇🏻

Maryamsbello.blogspot.com





A rude ya shiga kitchen ya debo ruwa ya dawo da wani irin sauri a hankali ya dinga yayyafa mata a fuska amma ko motsi batayi ba, ba karamin rudewa yayi ba ya mike a guje ya dauki wayarsa ya kira Yasir (oops na manta na fada maku he's a gynecologist) nan ya sanar masa abinda ake mata idan hakan ta faru a gida, da sauri ya nufi kitchen yayi warming ruwa a kettle, ya samu bowl ya debo da towel dan karami, a hankali ya janye rigarta zuwa cikinta ya cigaba da danna mata ruwan zafin nan a hankali yana warming marar, minti kusan goma yana abu daya har dai ya gaji dole yabi option 2, jawota yayi ya rungume ta tsam a jikinsa wasu hawaye na zulalo masa, a hankali ya gyara mata kwanciya bisa kirjinsa sannan ya nade hannunsa yasa iya karfinsa ya danne cikin aikuwa sai gashi taja wani irin dogon numfashi, baisan lokacin da yasaki wata uwar ajiyar zuciya ba gamida yin murmushi, tana bude ido ta ganta bisa kirjinsa nan take ta nemi ciwon marar ta rasa, kara hugging dinsa tayi ta shige cikin jikinsa sosai ta fashe da kuka mai ban tausayi, shima take wasu hawayen suka fara bin kuncinsa, Zarah sai kuka take tana kara shigewa cikin jikinsa, dagota yayi yana share mata hawaye yana girgiza mata kai alamun kar tayi kuka. A hankali ya mikar da ita tsaye ya hau gado ya jawota ya kwantar da ita akan kirjinsa yana shafa kanta yana kara hugging dinta, sunyi shiru na kusan minti uku kafin ya fara magana, wannan itace damar da yake da ita zaiyi clearing duk wani misunderstanding da ya shiga tsakaninsu, "Zarah kiyi hakuri da duk abubuwan da suka faru tsakaninmu tunda mukayi aure bamuda kwanciyar hankali, bayan letter din da kika gani da wadannan photos din nasan cewa ba banza ba, so I decided to investigate and see wanene yake son shiga tsakaninmu, I had my doubt at first amma ni bana son insa ma raina Khadija is behind all this, saboda ban taba tunanin daidai da rana daya ace bata shiryu ba, amma ki fada man in banda Khadija waye kike da shi da zai maki haka? All fingers were pointing at her, as I was saying sai na kira wani abokina, I paid him yaje inda Khadija take suyi magana ya tatso man information, nace masa yace mata inma tanaso ya rabani da Zarah zaiyi, without her knowing tayi exposing kanta da kanta, nan ta bashi original photos din da tayi photoshop dani tasa fuskana a kai,  bayan ya dawo ya kirani ya fada komai tace masa harta letter dinnan itace ta rubuta don ta rabamu, Zarah Khadija is behind everything bata hakura dani ba, hakika tayi betraying dinmu abinda yafi hurting dina the most yadda kikayi saurin yadda Zarah, I can understand kishi ne amma kina tunanin zan aikata maki haka Zarah?" Ya karasa yana kallon Zarah wadda tunda ya fara magana take kuka, a hankali ta zare jikinta daga rikon da yayi mata ita kuma tana mashi kallo mai wuyar fassara, kuka take bil hakki tana jin dama bata san Khadija ba a rayuwa, fuskarta duk wani pain, heartbreak da kuma farin ciki duk suka taran mata a lokaci daya. Cikin sheshekar kuka ta fara magana, "Ashraf ka yafe man, Khadija ta cuce ni! We are not even from the same parents...." a razane yake kallonta, "Me kika ce Zarah? Khadija is not your blood sister?" Ta gyada kai wasu hawayen na bin kuncinta, "Eh hakane, Nima ban dade da sani ba, Mummy ce ta fada mana da kanta, maybe wannan ne ya kara bata kwarin gwiwar ganin zata iya mallakarka tunda ba iyayenmu daya da ita ba...."

Tana fadan haka sai ta fashe da wani kukan, bude baki yayi zaiyi magana ta tsaida shi, a hankali ta mike tsaye kai kana ganinta kasan a fusace take, don dole shima ya mike tsayen amma baice komai ba gudun kar ya kara frustrating dinta ganin yanayinta, "Wannan shine karo na karshe da Khadija zata kara shiga rayuwata! Wannan shine karo na karshe da Khadija zatayi min mugun abu! Am going to bring her down! I will take my revenge I promise you that! Khadija sai ta gwammace dama bata taba sonka a duniya ba! This will be the last time she will do something bad to us! Na gaji I have heard enough! I wil not take this anymore! Ta ja ma kanta da kanta sai na dauki mummunan mataki a kanta, tunda ita ta nuna muguwa ce azzaluma! Wannan wane irin so ne haka? So hauka ne? Ko kuwa ana so dole? Khadija have hurt me beyond major and I promise I won't rest until she apologizes to me for her mistake.....!" Durkushewa tayi don zuwa yanzu kukan yaci karfinta shi kuwa Ashraf binta yayi kasan gaba daya idanunsa sun cika da hawaye, a hankali ya rungume ta ya dunga rarrashinta wane karamar yarinya, fuskarsa daga ganin kasan yana cikin bacin rai, kunci hade da dana sani marar adadi fuskar nan tayi jajir. "Khadija was loved by my mom despite the fact that she is not her biological daughter she took care of her more than us, bata taba kawo ma ranta cewar iyayenta basa tare da ita ba saboda daidai da rana daya Mummy bata taba bari ta gane ba, wallahi wallahi da muna yara za'a iya siyo mata toys din da suka fi nawa komai da tsada, Mummy tasha nuna tafi kaunarta a kanmu, tun abin na bani haushi har na saba, da muka girma kuwa ba irin batata da ba'ayi ba da kaya what ever tace tana so Mummy zata bata, an bata freedom fiye damu, Mummy bata iya hana ta or ta kwatse ta ko kuma idan tayi laifi tayi mata fada sam batayi mata, an kula da ita fiye da tunaninka ko wannan kadai ay ya kamata ta duba ta raga man, amma da yake son zuciya ya rufe mata ido da soyayya bata ji bata gani, Allah ne ya hadamu Ashraf, Ashraf ina sonka kuma zan iya bin duk wata hanya naci uban Khadija na shiga tsakaninmu da tayi, my biggest fear is that kar Khadija ta rabamu ko kuma tasan hanyar data bi don ta aure ka, bazan iya jurewa ba Ashraf I can't let her take you away from me...." kafin ta ida magana Ashraf yayi hugging dinta saboda he can't take it anymore, Kuka ta kara fashewa da shi sannan ta kara rungume shi tsam, "Ya isa kukan nan haka Zarah", rocking dinta yakeyi alamun rarrashi kafin yace

"it's okay Zarah, let bygone be bygones, karki biye mata kice zaki hukuntata wallahi komai zatayi bazan taba sonta ba, you're the only woman for me inshaAllah har aljanna, so ki daina jin tsoron wata Khadija bata isa tayi miki komai ba wallahi sai abinda Allah yayi miki, kuma karki damu shifa Allah yana ganin komai kina zaune zai maki sakayya tunda ke kinsan bakida hakkinta." Dagowa tayi tana kallonshi shima ya kalleta a take suka sakar ma juna murmushi, "Ashraf kaje kayi sallah..." ta fada tana sakinshi alamun ya tashi, a hankali ya mike yana kallonta cike da kauna kafin yace "Will you take care of yourself?" Ya tambaya cike da kulawa, "InshaAllah I will don't worry." Murmushi ya sakar mata "Tashi ki kwanta sosai tou, ki kwanta ki huta kinji?" Ya fada yana kokarin dagata da sauri ta cire masa hannu tana girgiza kai, "No I will stain everywhere." Ta fada tana sunna kai kasa, nan ya gane abinda take nufi, "Kinma tuna man idan nayi sallah zan wuce shop sai in siyo maki daga nan." Tayi murmushi tana gyada kai yayi mata murmushi sannan ya fita. Zarah na nan shiru har bacci ya fara surarta can cikin baccin ne taji takun tafiyarsa, window ta leka taga garin har yayi duhu haka, shigowa yayi da sallama hannunsa dauke da leda yana mata murmushi,  gefenta ya zauna yana kallonta, "How are you feeling princess?" Tayi murmushi cike da kunya tace "Alhamdulillah." Yace "Haka nake sonji, ga pad dinnan jeki kimtsa ko?" Ta karba da murmushi saman fuskarta "Thank you." Tana jiran ya fita ta tashi taji shiru, "Tou ka fita in shirya." Ta fada a shagwabe murmushi kawai yayi sannan yayi hanyar kofa, harya kai kofa yaji ta kurma wani uban ihu, a rude ya juyo yana tambayar lafiya? Dariya ta fashe da ita kamar zata siqe, shi kuwa cike da sha'awa ya tsaya yana kallon dariyarta so adorably, saidai tayi mai isarta sannan tayi shiru tana maida numfashi, "Am sorry Ashraf I just wanna see your reaction and how much you care, tou mr caring find your way out please yan mata zasu shirya thank you." Ta fada cike da tsiwa harda mashi gwalo, dariyar shima yayi sannan ya fita, yana fita ya sake jin dariyarta tana fadin, "Ashraf ka daina dariya fa kar bakinka yayi ciwo..." tana fadan ta sake yin wata dariyar, har Ashraf ya isa parlor bai daina murmushi ba zuciyar fes kuma cike da kaunar matarsa Fatimah Zarah.

-------

Sultan ne ya shigo fada inda ya iske Sarauniya Hoodah da maids kusan biyar ko wace da abinda takeyi, daya na bata labari mai ban dariya, daya na mata tausa a kafa, daya jakadiya ce amma sabuwa ce tana bata wani abu kamar pap cikin bowl tana bata a hankali tana sha, daya kuma tana tsaye da katon mafecin feather mai colors a jikinsa tana ta mata fifita a hankali. Sallamarsa ce ta katse masu abinda sukeyi suka dakata suka gaishe shi cike da ladabi, "Duk wannan aikin da suke maki aikina ne ba nasu ba." Ya fada yana murmushi, ya karbi hand fan din yana fadin "Zaku iya tafiya." Duk suka mike cike da ladabi suka fita, jakadiya har ta kai kofa ta dawo da sauri ta sunkuya, "Ranki shi dade kina da bukatar wani abu? Allah shi kara maki lafiya Sarauniya..." Sultan ya juyo yana kallonta "Eh Shuwaka...." ya fada yana bin Hoodah da murmushi "Ki dafa soup din shuwaka na Hoodah, yana da kyau ga mace mai ciki, kiyi shi da dan yaji." Ta sunkuya "Tou ranki ya dade Allah ya kara girma yanzu kuwa InshaAllah." Tana gama fadin haka ta fita da sauri, gefenta ya zauna ya dauko bowl din pap din ya cigaba da feeding dinta, "Naji dadi kina cin abinci Hoodah..." tayi murmushi "Only if you feed me." Ya kalleta "Shhh oya bude bakin." Tayi dariya ta bude bakin yasa mata a haka ya dinga bata har ta shanye tas, ya aje bowl din bisa table ya juyo yana kallonta gamida da gyara mata gashinta daya fito ta gefe gefe, "So tell me wace kasa kikeso ki haihu?" Tayi murmushi tana kamo hannunsa "Here Sultan, I don't wanna go to anywhere I want to give birth right here darling." Yayi murmushi "As you wish my queen..."

------

Shirin makaranta takeyi a gaggauce saboda ta kusa makara zuwa class ga in kayi late ko kafi kuda kwakwa lecturer din koraka xaiyi, sanye take cikin dogon bakin wando da riga yar ficit ash color sai ta yafa black gyale, hills tasa masu shegen tsini sannan ta dauko bag dinta da wayarta, chewing gum ta jefa a baki tana wani cika tana batsewa, room mate nata mai suna Sakinah wacce ke kwance da novel tana karantawa sanye da kayan bacci ta dakata tana kallonta kafin tace, "Wai Khadija club zakije ko School?" Wani shegen kallo tayi mata kafin ta maka mata wani uban tsaki, "Tou uwar sa ido club zanje mtseww aikin banza." Tana gama fadan haka ta fito a fusace ta fara tafiya kai kace bata son taka kasa, har ta kusa bakin gate da yake babu nisa school din daga hostel din nasu wata bakar Prado ta paka ta gabanta, tsaye tayi baki sake har aka fara zuge glass a hankali, nan tabishi da kallo mutumin dattjo ne zai kai kimanin shekara hamsin da biyar, a hankali ya fito yana binta da kallo daga sama har kasa sannan yace "Yan mata in bazaki damu ba don Allah ki ara man lokacinki minti biyar kacal yayi yawa." Wani mugun kallo ta watsa mashi sannan ta bishi da tsaki, "Banida lokaci koda na kyauta ne balle kuma na aro, don haka inada abun yi bazan tsaya bata lokacina akanka ba, don Allah malam ka rabu dani school zanje ina da class..." kusa da ita ya matso tare da cire glass dinsa, kana ganinsa kasan ba karamin mai kudi bane naira ta xauna daram a jikinsa, wata yar dariya yayi yace "Ba damuwa..." clapping kawai yayi... Da sauri body guards nasa ko wane sanye cikin bakaken suits suka fito da katuwar jaka hannu kawai guard din yasa ya zaro kudin da baisan ko nawa bane ya mika ma ogan nasu, ogan nasu ya karba sannan ya basu izinin tafiya, kallonta yayi yana wani murmushi kafin yace "Ga wannan kisa kati ko? And also here's my card you can call me anytime don't hesitate..." baki bude take kallon kudin zasu kai dubu dari sai juya su takeyi tana washe baki tace "Tou baka fada man sunanka ba?" Yayi wani shu'umin murmushi "You can call me Alhaji Hamza, Kefa what's your name yan mata?" Tayi murmushi "Khadija." Yace "Nice name, Khadija yanxu inada meeting karfe sha daya na safe, I wish to talk to you more but am kinda busy, zaki iya zuwa gidana muyi magana a can?" Shiru tayi take taji gabanta ya fadi, "Meyasa baxako ka sameni a hostel ba? You see bazan iya zuwa gidanka ba kuma every weekend ina zuwa gida why not ka sameni gidanmu?" Shiru yayi alamun tunani yace "Dear really is fine in baki iya xuwa, besides a waje fa zamu zauna inma kina ganin wani abu, kuma gidan da mutane kawai magana ce ta fahimtar juna nida ke kinga daga nan in kikayi approving nawa sai in cigaba da xuwa gidanku, donni ba wasa nake ba aurenki nakeso inyi..." tayi ajiyar zuciya "It's okay, yaushe kake ganin ya dace inzo? And give me the address." Yace "I will text you in har xaki iya bani number ki dear, and batun zuwa around 5pm idan yayi maki lafiya lau...." tace "Okay ba matsala zanzo anjima." Yayi dariya "Okay, can I drop you to school?" Ta girgiza kai "No nayi late ma, I think zan juya in koma hostel," yace "okay, in kina ganin ba matsala zan iya turo da mota a dauke ki anjima?" Tace "Ok nagode." Daga haka sukayi sallama ta juya shi kuwa Alhaji Hamza ya bita da kallon kurilla yana hadiye yawu sannan ya shiga mota. Da yamma ta shirya cikin wani dakakken material dinkin yayi bala'in kyau, turare ta fesa ta yafa dan karamin gyale, hills tasa da wata yar kucit din handbag itadai Sakinah sai kallonta takeyi har ta gama shirinta tsab ta fito, tana fitowa motar na isowa ta bude ta shiga, ita dai tunda suka shiga take latsa waya, saida tafiyar tayi nisa ba zato ba tsammani kawai taji an fesa mata wani abu a fuska, ihu ta kurma ta saki wayar take tana jin kanta na mata nauyi idanunta na rufewa, duk yadda taso hana kanta bacci abin ya faskara a hankali ta silale bisa car seat din a yayinda duhu ya mamayeta....




Bana jin dadi sosai har yanzu sheyasa kuka jini shiru thank you🥰🤗

No comments: