Thursday 12 August 2021

YAR AGADEZ PAGE 44

 YAR AGADEZ

 

 

              {Page 44}



To read all my books click the link below👇🏻

Maryamsbello.blogspot.com




Kura ma ceiling idanu tayi dakin bakajin karar komai sai karar machines alamun ICU, jikinta in banda ciwo babu abinda yake mata hawaye kuwa sunkasa tsaya mata, kanta nade yake da katon bandage, fuskarta manne da oxygen mask, drip kuwa ansa mata kala biyu daya na ruwa daya na jini duk suna shiga a kowane hannu, zagaye kwayar idanunta takeyi sannan ta tabbatar a asibiti take, "Alhamdulillah kin tashi?" Taji muryar wata ta fada a gefenta, matar ta share mata hawayen da suka kasa tsaya mata, hannu Khadija tasa ta zare oxygen din a hankali bakinta na kyarma ta furta, "Where's my Mummy?" Dafa ta tayi ta mata murmushi, "Bari na kira Doctor, yanzu zaizo ya duba ki, you're a brave girl everything will soon be alright sannu ko?" Ta fita ba jimawa ba sai ga Mummy ta shigo kamar an tunkudo ta, dah da farko tsaye tayi saboda itama har yanzu ba karamin kuka take ba, tsaye tayi bakin kofa tana ta goge hawaye saida ta tabbatar kukan ya dan tsagaita sannan tayi ajiyar zuciya ta karasa ciki, a hankali ta tsaya gefen gadon tana kare mata kallo, Khadija ta juyo da fuskarta suka hada idanu sai ta fara kokarin tashi zaune, Mummy tasa hannu ta dafata tana ce mata, "No don't get up, an maki surgery a kasanki doctor yace mana karki yi moving Khadija, wait sai wurin yayi sauki tukunna." Ko sauraren Mummy batayi ba tana sheshekar kuka tana kokari tashi zaune, Mummy ta riketa gam tana girgiza kai hawaye na faman zubowa daga idanunta, "Why am I still alive?? Why do you save my life? Ay da bari kukayi na mutu meyasa kuka ceto rayuwata? Meye sauran amfani na kuma? Rayuwata batada wani amfani kuma." Ta fashe da wani irin kukan fitan hankali, da sauri Mummy tayi hugging dinta, "Karki ce haka Khadija, ba kanki aka fara fyade ba, kuma kaddara ce bata wuce kan kowa so please ki daina fadan haka Khadija rayuwarki nada sauran amfani a garemu we all love you so much...." ture Mummy ta shiga yi tana shesheka, "No! Mine is different Mummy! My own father raped me! He molested me over and over again, mahaifina! How do you expect me to continue living my life? Just how?!" Mummy ta kara rungume ta zuwa yanzu ta kasa controlling kanta kuka takeyi kamar ranta zai fita, a hankali aka turo kofar dakin Doctor ne ya shigo nurse na biye dashi a baya, Mummy ta janye jikinta daga na Khadija tana share hawaye tana kakalo murmushin dole, "My patient how are you feeling today? And why are you crying?" Ya furta yana kokarin zama gefenta, bata bashi amsa ba sai ma kukanta da ya karu, umarni ya ba Mummy da nurse din akan su bashi wuri ya ga patient din tasa zai kirasu back, fita sukayi shi kuma ya maida dubansa ga Khadija wacce ke shar6ar kuka kamar wacce ake yanka ma naman jiki. Dr Hafiz bai ce mata komai ba yabita da idanu har sai data tsaigaita da kukan da takeyi sannan yace mata, "Feel better?" Ta gyada kai tana share hawaye, murmushi yayi sannan ya dauko ruwan dake cikin bottle kan side table din dake gadon da cup ya tsiyaya mata half cup ya mika mata, "Drink thisvwater you'll feel much better." Ta karba a hankali tasha ta mika masa, gyara zamansa yayi sannan yace mata, "Komai da kikaga ya faru da mutum kaddara ce, Allah yana san bawa ya dauki kaddara mai kyau ko marar kyau, duk abinda ya hukunto maki ki karba hannu bibiyu sai kiga komai yazo maki da sauki...." girgiza kai ta shiga yi wasu sabbin hawayen na wanke mata fuska, "Doctor mahaifina.... he....he...." kasa karasawa tayi saboda kukan da yaci karfinta, don dole ya mike ya kira nurse taje ta siyo allurar bacci akayi mata, itama tana fizge fizge da surutai babu abinda take fadi sai, "Mahaifina ne.... mahaifina ne... shine ya cuceni.." abu daya take ta nanatawa babu abinda Mummy keyi sai kuka wane an aiko ta, sai can bacci yayi gaba da Khadija sai sannan Mummy ta samu yar natsuwa cikin ranta, ta jima a nan zaune tana bin Khadija da kallo kafin Doctor din yace, "Meet me in my office Hajiya I want to speak to you privately." Gabanta ya dan fadi can dai ta dake tace "Ok Doctor."  Daga haka yayi gaba nurse din ta sake gyara Khadija ta chanza mata drip sannan ta fita. A corridor ta iske Zarah, Hoodah da Hafsat zaune jugum jugum ko wane ya rafka tagumi, Mummy ta dafa Hoodah, "Hoodah ya kamata ki koma gida kije ki huta sai Zarah ta tafi dake ta bude miki dakina, you need rest my dear you see your condition bai kamata kina stressing kanki ba...." Hoodah tayi murmushi "An not stressed I am okay Mummy." Mummy zata sake magana Zarah tace "Don't worry Mummy she's fine." Mummy ta kakalo murmushi "Okay, em... Zarah ga Khadija nan please look after her zanje in dawo." Ta gyada kai Mummy ta wuce inda ta tadda Ashraf, Yasir da Sultan suma suna zaune ko wane da tunanin da yake, tace masu "The Doctor wants to see me, I think you should come with please," suka gyada kai suka mike a sanyaye. Da sallama suka shiga dakin Dr Hafiz da alama su yake jira yana ganinsu yayi murmushi yace "Please come in." Suka shigo a sanyaye, bayan sun zauna ya sauke ajiyar zuciya, "Kamar yadda kukasani Khadija was molested and abused, lokacin da aka kawo mana ita munyi mata duk wani gwajin da ya dace muyi mata thankfully she's okay, hiv negative etc. Mutumin ya halbeta ba a ciki ba iyaka which badly affected her womb, I really don't want to say this to you amma dole ku sani..." Ya numfasa gaba daya gabansu faduwa yakeyi, "Na farko shine Khadija bazata taba haihuwa ba her womb was damaged completely, sai buguwar da tayi da ya wurga ta kasa ta bugu a bayanta whiich badly affected her spinal code, zaiyi wuya ta sake takawa I thought we can fix it but sadly we couldn't, she has to be on wheelchair for the rest of her life, am so sorry for this news ba yadda zanyi dole in fada maku.... and lastly, she broke her hand ya taba mata jijiyar hannu which caused the side to be paralyzed in zaki kula dazu tana ta kokarin tashi zaune ta kasa sannan zaki lura hannun hagunta kadai take dagawa dayan bata daga sa, inshaAllahu with time zamu dinga mata physiotherapy zata dawo da hannunta, sai kun dinga daurewa shima maganarta ya danyi affecting amma kadan thankfully ba da yawa bane in no time zata dawo da hannun and her speech will be clear. Sai kun bata kyakyawar kulawa sannan you have to support her through this journey har Allah ya iyakance mata, maganar karshe you don't have to tell her now zaku barta har sai taji sauki in ba haka ba it will worsen her condition, keep any bad news apart just try and make her happy..." zuwa yanzu Mummy bata iya kwakwaren motsi, a sanyaye Ashraf da Sultan suka mike suma kansu sun saka magana suka fice daga office din,  a hankali Yasir ya kamo Mummy wacce ta kura ma Doctor din idanu tun dazu, ta mike tsaye Yasir yace "Mungode Dr." daga haka yaja mahaifiyarsa wacce ke behaving kamar marar lakka, bakin kofar dakin ICU din ya zaunar da ita sannan ya zauna gefenta hannunshi cikin nata, yana zama ta jinginar da kanta bisa shoulders dinsa ta runtse idanu wasu hawaye masu shegen dumi suka gangaro mata, suma su Zarah hankali tashe suke tambayar lafiya babu wanda yake da energy din magana saidai Yasir ya bisu da idanu kafin yace, "Please don't stress Mummy with questions for now, yanzu Mummy tana bukatar hutu in ba haka ba she will also fall sick, please ku kula da ita da kyau." Ya fada yana mikewa tsaye, da sauri su Zarah suka zauna gefenta sai faman magana suke mata kamar ma bata san sunayi ba, karshe ma da suka isheta sai ta mike tsam batace dasu komai ba tayi dakin ICU din ta shiga a hankali, jingina tayi da kofar tana kallon Khadija wacce ke bacci da alama tayi nisa a baccin nata, a hankali take tafiya har ta isa bakin gadon har yanzu bata dauke idonta a kanta ba, zama tayi tare da kamo hannuwanta ta damke tare da dora kanta bisa hannun ta lumshe idanu, dagowa tayi tana kallonta hawaye na gangaro mata tace "Khadija ko kinyi ma wani ko wata laifi ne? Ko kuwa Allah kikayi ma laifi?" Mummy ta tambayeta tana tsareta da idanu kamar tana jinta, tafi minti goma tana kallonta kafin ta goge hawayenta da sauri ganin ta fara motsi...

2 DAYS LATER...

A hankali ta bude idonta ganin Mummy gefenta ya sanya ta fara kokarin tashi, Mummy tace "No Khadija don't move please, na fada maki da aiki a kasanki ba'a son yawan motsi." Daina motsin tayi ta koma ta kwanta tana bin Mummy da kallo, can tace "Can I ask you a question?" Mummy ta gyada mata mata kai "Sure darling what is it?" Khadija tace, "Bayan na suma what happened after that? I can't recall anything abinda kawai na iya tunawa kawai shine ina jin ana tafiya dani bisa emergency bed but daga nan bansan meyafaru ba after that." Mummy tayi murmushi gamida kamo hannunta, "Nothing much sweetheart, meyasa kikeso kisani yanzu?  Ki bari idan kinji sauki I will tell you everything, but for now you rest and rest, that's all you need to do for me okay?" Khadija tayi murmushi, "Okay but please one last question Mummy?" Mummy tayi ajiyar zuciya tace "Okay ya akayi?" Tace "Where's my dad?" Shiru Mummy tayi na yan seconds kafin tace "He's where he deserves to be right now, he is in police custody Khadija, kuma InshaAllah za'ayi masa hukuncin daya dace dashi so please don't worry okay?" Khadija tace "I know, can I see him amma?" Mummy ta bata rai, "Me xakiyi masa after what he did to you he doesn't deserve to be called a man or a father!" Mummy ta fada a fusace, Khadija tace "I know Mummy, I just wanted to tell him some things he should know, sannan to tell him how much hate I have for him in my heart!" Mummy ta shafa kanta, "Don't stress yourself because of that monster, that's exactly how he did to my sister, he dated her for 5 months thinking he was the right guy for her, but then he showed his true colors, he did exactly what he did to you." Ta fada wane cikin bacin rai, Khadija feeling hurt tace "Then why did you let him get away with it back then?" Mummy ta share guntun hawayenta tace "We tried our possible best Khadija, but that man left this country, kinsan dai tunda ya riga ya gudu wata kasa we don't have any right to do something har sai dawo." Khadija tace "He's wicked and heartless," Mummy ta kakalo murmushi "Hakane, saidai babanki ne no matter what ba'a chanza ma tuwo suna, addu'a kadai zaki taya shi Allah ya shiryeshi kinji??" Ta gyada kai, Mummy tace "That's my brave girl, now what do you want to eat?" Ta girgiza kai, "Nothing bana jin yunwa." Mummy tace "A'ah, you have to eat koda liquid ne don kisha magungunan ki." Tana fadan haka ta mike ta nufi waje don samo mata wani abu har Mummy ta kai kofa Khadija ta tsaida ta, Mummy ta juyo da murmushi saman fuskarta tace, "Do you need something?" Khadija tace "Can I speak to Zarah and you Mummy?" Mummy ta dawo kusa da ita tace, "Meyafaru haka? Me kikeso kice mana?" Khadija tace "I will say it if Zarah is here." Mummy tace "Alright let me get her," Mummy ta tafi ba'a juma ba sai gata itada Zarah sun shigo, Khadija tace so take ta jingina a gadon Mummy ta taimaka mata, bayan ta gyara zaman nata ne ta kallesu sannan ta fara magana, "A wannan zamanin baza'a taba samun butulu ba kamar ni...!" Cike da mamaki Mummy ta matso kusa da ita ta zauna harda rike mata hannu tace, "Subhnallah Khadija! Ki daina furta kalmomi makamantan haka! Kar ki sake kiran kanki butulu a ina kika yi butulci? Kuma wa kikai mawa? Please keep that word out of your mind!" Girgiza kai Khadija ta shiga yi, "It's true Mummy! Nayi maku butulci, ban kyauta ba I am ashamed of myself now I don't deserve your love Mummy Instead I deserve your hatred!" Mummy ta kalle ta cikin shock idanunta a waje tace, "Why are you talking in riddles? Explain yourself!!" Zarah tace "Khadija maganar nan ya wuce basai kinyi wani bayani ba please a manta da abinda ya riga ya wuce..." Mummy ta juyo tana kallon Zarah sannan ta mike tsaye ta isa dab da ita tace "What are you hiding from me Zarah? Me Khadija tayi miki da ni banida labari?" Zarah ta hadiye kukanta amma still saida stubborn one ya zilalo mata, Mummy ta girgiza ta tace, "Talk to me Zarah! What happened between you two?" Zarah dai batace komai ba sai kukan da takeyi, Mummy ta juyo tana kallon Khadija, Khadija ta fara magana cikin karfin hali kanta na kasa, "Bayan na dawo hutu sai naga Ashraf a gidanmu at first I was pissed off sai daga baya na kamu da sonsa! I started becoming jealous of Zarah ina neman hanyar da zan raba su, I even drugged him, na kwanta dashi saboda Zarah taji haushi ta rabu dashi, but none happen! I keep plotting against Zarah even after I find out we are not related, ban tsaya a nan ba na rubuta mummunar letter lokacin bikinta bayan ta tare kafin na dawo gida, a letter din na rubuta abu mafi muni inda na sa suka fara fada tsakaninsu bayan nan naje nayi photoshop fuskar Ashraf da wata kafira tsirara na aje a wardrobe din Ashraf, I guess sun gano ni sheyasa suka shirya, despite what I have done Zarah bata taba fada maki ba ta rufa man asiri cuz tasan idan kika sani zata bata relationship dinmu dake! I know sheyasa abinnan ya faru dani my father raped me meyafi wannan bakin ciki? Ina girbar abinda na shuka gradually! Da haka nake cewa Mummy ki yafe man nasan I don't deserve your forgiveness. But you are a good person kin rike ni fiye da yadda kika rike yayan cikinki amma ga abinda na saka maki dashi, please forgive me Mummy na tuba...!" Tunda Khadija ta fara magana Mummy ta zama shocked tsaye tayi har ta gama saurarenta kafin ta fara ja baya a hankali, "Khadija...! Dama ashe haka kike?" Khadija ta fara girgiza kai ga ba halin tasowa, "Mummy don Allah kiyi hakuri ki yafe man wallahi na gane kuskurena! And I love you please don't punish me by not forgiving me I cannot bear it..." Zarah ce ta taro ta ganin har ta kai kofa amma ina kafin ta karasa har Mummy ta fita da sauri daga dakin, Zarah ta kwala mata kira sannan ta bita a guje, Khadija kuwa kokarin moving takeyi har sai da ta kai karshe gado ta zube akan gadon saboda bata iyawa, wani kuka na fitan hankali tasa tana fadin, "I made a huge mistake please forgive me Mummy!" Kuka take kamar ranta zai fita ji take gaba daya duniyar ta isheta kuka ta dinga rigza tana kiran Mummy har baccin wahala ya dauketa.

Tun daga ranar Mummy ta fita harkar Khadija, gaba daya ta janye daga jinyarta da takeyi ko tazo saidai tazo ta duba ta amma bata wani bata kulawa kamar da, amma komai tanayi duk wani payment da medication dinta bata fasa ba, saidai ta chanza mata sosai, Zarah da Hafsat kadai ke faman jinya Hoodah kuma sun koma itada Sultan cikinta ya cika wata takwas cip sheyasa ma Mummy tace su tattara su koma haka nan. Abinnan ba karamin damun Khadija yakeyi ba har sunyi sati uku yau babu abinda ya chanza itama Mummy taji babu dadi amma ta dake she's just so angry at her. Satinta hudu chip aka sallameta sun siya wheelchair sannan za'a dinga dawowa physiotherapy sau biyu a sati. Khadija ba karamin shiga senses dinta tayi ba duk ta chanza ta zama shiru shiru da ita. Zarah ma sun tattara sun koma Agadez itada angonta Ashraf.

--------

A hankali ta bude idonta a daidai lokacin ne duk abubuwan da suka faru a daren jiya suka dawo mata, wani irin faduwar gaba taji at the same time kuma zuciyarta fal take da farin ciki marar adadi ji take kamar a mafarki. A hankali ya turo kofar dakin ya shigo da wani irin kayataccen murmushi a fuskarsa, saurin kauda kai tayi tare da lumshe idanunta sabuwar kunya taji ta ziyarce ta, wata irin kunya taji wacce bata taba zato zataji ba. Zama yayi gefenta har lokacin ta kasa bude idanunta, "Princess ba gaisuwa? Ko yan masifar ne suka taso?" Batasan lokacin data bude idanunta ba harda murguda baki, "Wai suka taso sai kace wata mai aljannu!" shiru yayi kawai yana binta da kallo yana jin sonta na kara shigarsa yana ratsa ko wace jijiya da kuma ga6o6insa. Saida ta bari ta mike tayi hanyar kofa sannan tace "Ina kwana?" Tana fadan haka sai ta fita daga dakin gaba daya. Yar dariya yayi kafin ya mike ya shiga bathroom don yin wanka. Side dinta ta tafi ta wanke bakinta tayi wanka, har ta karasa wankan nan murmushi bai bar lips dinta ba kaunar mijinta na sake linkuwa a cikin ranta da ruhinta. Tana fitowa ta shafa creams wanda Mummy tasa akayi mata hadin kamshi ta shafa ta fesa sprays kala kala a jiki, wata red gown ta atamfa ta saka ta daura dankwalinta tasa costumes, kwalli kawai ta shafa sai lipstick kadan tayi kyau ba kadan ba, wayarta ta dauka ta fito tana ta kamshi dama gidan baiyi wani datti ba dan kara kimtsa shi kawai tayi sannan ta tafi kitchen tana faman tunanin abinda zata dafa da rana. Cak ta tsaya tana bin dining din da kallo yadda ya cika shi da abinci yayi setting dinshi gwanin ban shaawa. Yadda kuka san shine matar gidan, wani irin dadi taji a ranta, zuciyarta fal haka ma fuskarta ta kasa daina murmushi haka ta juya da niyyar tafiya side dinsa sai gashi ya shigo waya kara a kunnensa, babu abinda ke tashi parlon sai kamshin turarensa, binshi tayi da kallo sai ma taga bai taba mata kyau ba irin na yau sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda blue color hular kansa ta shiga da kayan da ya sanya, yanata waya fuskarsa cike da annuri sai murmushi yakeyi, take sai taji tukukin kishi ya taso mata wai dawa yake waya haka sai wani murmushi yakeyi? "Ah haba na isa in manta dake?... haha kin fiya abin dariya wallahi... yanzu dai kinsan tsada garemu ki biya in kinaso a bata." Jin alamar da mace yake waya sai kawai tasha kunu ta zauna kan dining gamida zuba abincin tana wasa dashi gaba daya sauraren conversation din nasa takeyi. Tun yana tsaye yana wayar har yaja kujerar dining ya zauna yana fuskantarta yafi minti sha biyu sannan taga ya katse wayar, kallonta yayi yadda take ta juya abincin fuskar nan a tamke wane tana jiran dambe, yar dariya yayi sannan ya matso gefenta ya zagayo da hannayensa saman wuyanta yana kissing gefen fuskarta, "Sana'ar ta taso kenan?" Wata irin harara ta watsa masa ta gefen ido tana ture hannayen nasa dake sargafe saman wuyanta. "idan ka gama wayar sai kazo kaci abinci, ko wayar ta kosar da kai ne?" Wata dariyar ta su6uce masa ba shiri yana jin nishadi a cikin ransa, plate ya janyo ya tura gabanta, "Ayi hakuri ranki ya dade bata kosar dani ba yet, zanci abincin." Zuba masa tayi cikin masifa ta hankada masa plate din gabansa, murmushi yayi ya girgiza kai sannan ya fara cin abincinsa a natse, a hankali ko wanensu ya fara cin abincinsa gaba daya zuciyar Zarah cike take da tunanin dawa yake waya haka? Kodai Khadija ce ta kirashi da salon kara yaudara? Nan take taji zuciyarta har tafasa takeyi, "Zarah kodai in tafi wurin aiki ne?" Da sauri ta dago da wani irin expression a kan fuskarta tace, "Bangane ka tafi aiki ba, dama bazakaje aikin ba?" Danne dariyar shi yayi yana shan tea a hankali kafin yace, "Kin manta na dauki hutu wurin aikina? Amma naga kullum fada muke Zarah ba gara in tattara inawa inawa ba in koma wurin aiki ba? Idan baki ganina kila kin fi jin dadi," kallonsa takeyi kafin tace, "Tou ay kwana biyu bamuyi fada ba."  Batasan lokacin da maganar ta fito daga bakinta ba, murmushin data ga yanayi ne yasa tayi saurin cewa, "Idan wurin wacce kuke waya zakaje tou ka gayyace ta tazo gidannan kaga sai ku huce takaicin rashin ganin juna da bakuyi ba." Tana gama fadan haka ta mike da sauri ta tattara kwanukan tayi kitchen dasu don wankewa, gaba daya kishi duk yabi ya addabeta gashi yaki gaya mata dawa yake waya. Wanke kwanukan ta farayi duk ranta babu dadi, ba zato kawai taji ya rungumeta ta baya nan ta fara mutsu mutsu akan ya saketa, "Wai bakaga aiki nake ba?" Ya kara matse ta, "Tou kawo in tayaki wai princess fushin na menene? Kefa da bakinki kike cewa mun daina fada why can't we continue living that way happily?" Taji ya fara kissing bayanta da kanta lightly, tace "Ba kace aiki zaka koma ba halan tayi missing dinka tace ka dawo ta ganka?" Gimtsa dariyarsa yayi sosai kafin yace "Wai wacece wannan ake ta fushi akanta?" Ta kara hade rai "Wacce kuke waya dazu da ita mana! Sai wani narke murya kake kana kashe mata murya, indai haka ne gaskiya na fasa soyayyar da kai sai ka tafi wurinta tunda ita kakeso yanzu bani ba!" Ta karasa gamida murguda baki, a hankali Ashraf ya juyo ta, "Zarah da Hoodah fa nake waya, wannan kasa da murya da kika inayi nace mata ay bacci kike kar na tashe ki, Zarah a tunaninki zanyi waya da wata a gabanki nasan daga ni har ita bazamu tsira ba wurinki? Besides ni matata kuma princess dina kawai nakeso, ita kadai ta samu damar mallakar zuciyata." Harara ta watsa masa duk da cewa fuskarta dauke take da murmushi alamar taji kunyar abinda ya faru, "Ni ka daina man haka kunya nakeji, sai kayita man rashin mutunci sai kuma a dawo ana cewa ana sona ehe!" Dan peck yayi mata a goshi zuciyarsa cike da farin ciki sannan yasa hannayensa ya zagayo dasu saman waist dinta ta sunkuyar da kanta fuskarta dauke da murmushi, Ashraf yace "Niii Ashraf yaushe nayi rashin mutunci? Ya zaayi in wa matata rashin mutunci duk yadda nake kaunarta?" Yar hararar wasa ta masa, "Da wannan maganar dama kawai hakuri ka bani da yafi," hancinta yaja yana dariya, "Kiyi hakuri kinji princess? My love, my chicken peri peri, my curry, my onion..." wata irin dariya takeyi har dukewa takeyi shima yana tayata hugging dinsa tayi tana kyalkyatar dariya shima yana dariyar yakeyi sai da tayi mai isarta sannan ta tura shi waje ta rufe kitchen din, "Go and watch football or news ka barni nayi aikina in peace abeg!" Tana juyo dariyarshi yana fadin "Your wish is my command your highness!" Aikinta ta cigaba da yi cike da nishadi kafin wayarta ta fara ringing, AirPod dinta ta dauko ta jona a kunne tana dariya tace "Hello..." ta furta farin ciki mamaye a zuciyarta.. Can bangaren tace, "My Inlaw how far ya kike?" Zarah tace "Wallahi lafiya lau mai girma Sarauniya! Ko kin haihu ne mu taho?" Hoodah tayi dariya sosai tace, "Kaji ki da zolaya Fatima, ay kafin in haihu zan kiraki ki garzayo kece zakiyi raino!" Zarah ta kyalkyale da dariya, "Ba dole ba ay shima babyn bai isa ya fito ba sai uwarsa tazo!" Hoodah cikin dariya tace, "Gaskiya bai isa ba, yanzu dai ina wuni? Ya kuke? Ya amarci? Ya ango? Ina fatan ana kula min da yayan nawa yadda ya kamata?" Zarah tayi dariya cike da nishadi tace, "Wannan tambayoyi haka Sarauniyar mu? Hehe Tou komai kalau kalau wallahi ya gajiyanku?" Hoodah tace, "MashaAllah, ah gajiya tabi jiki ay ya me jiki kuma?" Zarah tace, "Haka akeso ay, me jiki dasauki alhamdulillah mungode fa da dawainiya Allah ya kara girma da arziki." Hoodah tayi dariya "Ah meye na godiya kuma? What are family for? Aa ni kam ki daina mun godiya." Zarah tayi murmushi kurum, Hoodah tace "Gaskiya Zarah you're a great person, dan zaman da mukayi asibiti na shaku dake we became good friends, tunda na dawo nakejin ba dadi I really miss you all." Zarah tace "Same here my dear, am glad we met, yanzu ay mun zama yan uwa." Hoodah tace, "InshaAllah... tou bari naje dama na kiraki mu gaisa naga kin wani manta dani kina ta amarci ko?" Zarah ta kyalkyale da dariya,  "Wallahi ba haka bane, nagode sosai Sarauniya, take care regards to sarki..." Hoodah tace "You too InshaAllah." Suka katse wayar zukatansu fes a haka ta karasa aikin ta kimtsa kitchen din sannan ta fito parlor.  Tana fitowa parlor taji an fizgo ta, a tsorace ta saki kara Ashraf ya saki dariya yace, "Lallai yarinyar nan kin cika tsoro, daga na jawoki sai ki kama tsorata? Wai dama raki gareki a haka zaki haihu?" Ta saki dariya, "Haihuwa kuma? A ina zan iya haihuwa yar yarinya dani?" Dariya ya kyalkyale da ita harda dukewa, ta saki baki galala tana kallonsa, can yace "Yarinya kuma? Kodai rowa zakiyi man? Nida nake sa ran by next year muna nan rike da babynmu?" Ta wangale idanu cikin wasa tace, "Ni Ashraf? Rufa man asiri in haihu ay nayi yarinya da haihuwa, banma iyawa gaskiya." Ya daga mata gira daya sama "Haka kikace? Tou ko nazo na gwada ne?" Kauda fuskarta tayi gefe tana wata irin dariya, "Kuut Ashraf ko kunya wani wai ka gwada, kuma mutum yana kusanto ni zan fasa ihu mai gadi ya shigo ehe!" Dariya yayi sosai yana hugging dinta ta waist a hankali ya fara matsowa saida ya zo gab da fuskarta tuni ta fara zille zille tana neman guduwa, "A'a ki tsaya mu gwada mana mugani, kinga kenan nan da wata tara cip lokacin mun gama soyayyar mu har mun gaji." Tayi dariya cikin jin kunya tace, "La la wai dama idan akayi aure rashin kunya akeyi wallahi da ba haka kake ba, ni ka kyaleni tafiya xanyi in kwanta in danyi bacci." Kara rungume ta yayi, "Me nayi nakawai inyi iskancin da hujja." Wara idanu tayi sannan tasa hannunta ta toshe bakinta alamun mamaki, "Na shiga uku nidai ba ruwana kar kaja man sharri." Dariya yayi yana faman kissing din kanta yana kara matseta sosai hade da lumshe idanu, "Ina sonki Zara'u sosai fa ba kadan ba." Dagowa tayi tana kallonshi wani irin kallo as in kallo na masoya wani soft look mai kwantar da hankali, hannu tasa saman zuciyarsa hade da lumshe idanu, "Ay ga zuciyarka nan na bugawa tana dim dim dim!" Shiru yayi yana kallonta, pecking lips dinta yayi lightly sannan yace "Tunda da gaske bacci kikeji muje mu kwanta tou." Kokarin zillewa takeyi tana dariya ya riketa gam; "Kaida wa?" Yace "Da matata mana." Murmushi yayi ya jawo hannunta suka tafi daki duk son zillewarta haka ta hakura suka kwanta hannunshi rike da nata kamar wanda akace za'a sace masa ita a haka bacci yayi awon gaba dasu....




Tou yan team Zarah sai ku shirya zuwa suna nan da wata tara nikuma yar team Khadija (zuba ido hade da tagumi)😔

1 comment:

Hausa Novels said...

Download Hausa Novels https://mynovels.com.ng/