Thursday 29 June 2017

AUREN FANSA 09

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹



          🌹09 🌹

http://MaryamSBello.blogspot.com

Haka kuwa akayi washe gari da safe Hamza da Bilki suka fita don saka Meenah a makaranta. Gobarau Academy itace makarantar da suka nufa, da zuwansu da komai basu wuce minti talatin ba aka kammala komai aka saka ta Pre nursery, duba da shekarunta kuma a k'a'idar makarantar idan yaro bai kai shekara 3 ba to baza'a saka shi nursery ba daman. Daman 'yan pre nursery ba'a saka musu uniform.
A ranar aka barta makaranta kuma ko kuka batayi ba da su Hamza zasu tafi don ta samu abin wasa sai dad'i takeji.
K'arfe 12 suke tashi don haka dole Bilki ke d'auko ta don Hamza na wurin aiki lokacin, ba yadda ta iya haka nan take hak'ura tana d'auko ta d'in.

Haka rayuwar ta cigaba da gudana cikin hukunci da hikimar ubangiji, Meenah har ta shiga nursery. Meenah Allah ya bata k'walwa komai aka koya mata ta iya sai dai idan ba'a koya mata ba, kuma idan ta dawo gida ta dinga yi kenan ko gajiya batayi.

Ba'a saka Zarah makaranta ba sai da Meenah ta shiga nursery 2 a lokacin ita kuma Zarah tana da shekara 3 a duniya yayinda Meenah keda hud'u.


Ranar wata juma'a akayi ma su Meenah hutu suna zuwa gida Meenah ta fara neman babanta don nuna mai report card nata, sai
dai rashin sa'a yayi tafiya zuwa Lagos a safiyar ranar, tayi ta kuka tana kiran ita Baba.
Bilki tana tsaki ta ansa report card nata dana Zarah tana dubawa, abin takaici a wurinta wai Meenah na d'aya tayi ita kuwa Zarah na ashirin tayi cikin su ashirin da shidda. Bilki kamar tayi kuka don takaici. Wato Meenah dai tafi d'iyarta k'ok'ari kenan?
"Gaskiya da sake!" Ta kalli Meenah tace mata "Ke! Zo nan!" Meenah tayi tsaye idanunta k'wal hawaye a duniya tana tsoron Bilki, fizgo ta tayi da k'arfi.
"Ke dan ubanki sai da kika yi na d'aya wannan karon ma? Kin manta bugun da nayi maki last term kenan? Salon kija babanta ya dawo ya zane Zarah ko? Ke ga mai k'ok'ari ko? Shegiya mai kama da mage! Wuce ki bani wuri!" Da gudu Meenah tayi d'aki tana kuka sosai, jawo Zarah tayi ta rungume tace.
"Don Allah d'iyar Baba ki dage kifi waccan yarinyar k'ok'ari kinji?" Zarah ta gyad'a kai.

Da rana ta zuba ma Zarah abinci ta shiga wanka, Meenah na zuwa Zarah tace.
"Zo muci." Ba musu ta zauna suka fara cin abincin tare.
Ba'a jima ba Bilki ta fito wanka tana lek'owa taga Meenah nacin abin da d'iyarta abinda ta tsana! Da tsawa tace
"Ke!" A firgice Meenah ta tashi tana kyarma,
Bilki ta k'ara daka mata tsawa.
"Bana hana ki cin abinci tare da Zarah ba? Shegiya wuce ki tafi d'aki." Tayi d'aki da gudu a tsorace. Zarah ta aje cokalin hannunta tace
"Bazan ci ba nima sai da Meenah." Daman Bilki tasan abinda zatace kenan, tsaki taja tace
"To sai dai kar kici wallahi amma bazakici tare da Meenah ba, kinji na fad'a miki!"
Aikuwa aje cokalin tayi tana fushi sosai ta bar parlon. Tsaki Bilki ta k'ara yi tana k'ara jin haushin Meenah...


***

Sauri yakeyi ya dawo gida don nuna ma iyayensa result nasa na shedar kammala jss3 nasa. Driver na yin parking ya fito da gudu yana murna shigarsa keda wuya ya taradda abinda ya d'aga masa hankali, ya kuma gigita shi a lokaci guda, take zuciyarsa ta fara bugawa da sauri a yayinda k'walwarsa ta tsaya cak! ta bar aiki lokaci d'aya!!!
Iyayensa ne kwance jina jina, a yayinda wasu mutane kusan su bakwai ke tsaye cikin bak'ak'en kaya hartta fuskokinsu an rufe da black mask!
Tsaye yayi ya kasa tantance a wace duniyar yake, take kuma ya fashe da kuka yana fad'in.
"Su waye ku? Mey...asa ku...ka kashe min iyaye?"
Direwa yayi k'asa yana kuka yana jijjiga iyayen nasa a yayinda yake kiran Anisah! Mutumin yayi dariya yace.
"Ka bar kuka yaro, sun tafi inda ba'a dawowa kaima kuma yanzu zaka bisu!" Yakece da dariya sannan ya saita bindigar daodai saitin k'irjinsa ya harba.
A gigice ya farka duk da Ac d'in da ke aiki amma hakan bai hana sa yin sharkaf da zufa ba. Ta6a jikinsa ya soma yi amma baiga jini ba, ajiyar zuciya ya sauke ya shiga yin addu'a don ba k'aramin tsoro yaji ba.
"Wane wane irin mafarki ne haka..... ?"
Ya fad'a yana mai k'ara tunawa da mafarkin da yayi. Zumbur! Kuma ya mik'e ya fice da gudu don duba lafiyar iyayensa don gani yake kamar da gaske ne....!




MSB💖

No comments: