Wednesday 7 July 2021

YAR AGADEZ PAGE 35

 YAR AGADEZ

 

 

              {Page 35}



To read all my books click the link below👇🏻

Maryamsbello.blogspot.com



Wannan page din naku ne my pipu, Faty Mansur, Maryam Mansur, Farida Bature, Hafsat Bashir, Ayshat Fareedat and Nana Aisha❤️❤️❤️🤝🤝your comments always keep me going thank you 🥰👌



Kamar wata mahaukaciya haka ta nufi inda take aje magunguna, zazzago su tayi ta fara bincike idanunta kuwa jajir kamar wata zombie, cin karo tayi da wani maganin bacci dauko shi tayi da sauri tana karantawa, da azama ta mike ta leka parlor nan taga Ashraf kwance bacci yana fizgarsa sama sama, dakinsa taje cikin sa'a ta iske ya aje ruwa wanda ya fara sha a bottle da cup a gefe, da sauri ta bude bottle water din ta jefa tablet kusan guda biyar a ciki sai data tabbatar yayi diluting a ciki ta kara shaking kwalbar, rufewa tayi dasauri ta fito bayan wata kujera ta buya yadda ba'a ganinta, tafi minti 20 a nan sai can taji alamun shigowarsa, leke ta fara yi taga ya sa kai cikin dakin ya shiga, da rarrafe ta fito a hankali ta tsaya wurin kofa daga baya baya tana leken abinda yakeyi, gefen gado taga ya zauna yana latse latse a waya, yafi minti goma a haka kafin ya kishinga kan gadon, komai yagani kuma sai ya mike zaune ya bude ruwan nan ya zuba half cup ya kafa kai yana sha, shidai har sai daya gama shan ruwan nan sai yaji taste dinsa ya chanza, har yana tunanin kodai bakinsa ne? Juya cup din yakeyi kafin ya aje shi, can kuma yamike ya shiga bathroom, yana fitowa sai ji yayi kansa ya sara masa idanunsa na ganin biyu biyu, dafe kai yayi yana jin dakin na juya masa da kyar ya iso bakin gado da kyar yake gani sai faman bude idanunsa yake forcefully amma ina kafin kace me ya zube kan gado, Khadija na ganin haka ta mike da sauri ta shigo dakin ta rufe kofar, tsaye tayi bakin kofa tana harde hannuwa, "Yau ce ranar da Zarah zata fara tsanarka a duniya, today will mark the end of your relationship, and beginning to ours my dear Ashraf." Smirking tayi ta fara takowa inda yake kafin ta fara unbuttoning masa riga, ta window take leke bayan kusan minti sha biyar sai ganin Zarah tayi ta shigo gidan, sauri tayi ta gyara masa kwanciya kafin ta yaga rigarta, gashin kanta tayi squeezing duk ya watse kamar wata sabuwar mahaukaciya ta haye gadon tana murmushin mugunta. 

Zarah na shiga side dinsu direct dakinta ta nufa, ta cire hijab dinta ta saka wayanta charge sannan ta fada bathroom don yin alwala ganin lokacin sallar azahar har ya dan gota, bayan ta fito tayi sallah tayi addu'ointa ta mike ta linke prayer mat din da hijab din ta aje su inda suke, fita tayi ta sauka kasa kitchen ta shiga tace bari kawai ta dafa spaghetti tunda sunada miya cikin fridge inta dafa sai ta kai ma Ashraf nasa daki ko kuma tunda ta lura yafison zaman dining yanxu sai taje ta kirashi yaci a nan, a natse take aikinta tana tunanin ko yaushe ya Yasir zai dawo daga Abuja shida Mummy? Don ta kirasu jiya suka ce mata har yanzu basu sa date din dawowa ba, da wannan tunanin ta kammala aikinta ta gyara kitchen din, dining taje tayi arranging tana murmushi kafin ta nufi 6angaren su Ashraf, tana shiga parlor din ta fara takawa ciki ta jiyo wani irin ihu har saida ta firgita, tsayawa tayi ko zata kara jin ihun kodai kunnenta ne ya jiye mata ba daidai ba? Kara jin wani ihun tayi wanda yafi na dazu, a tsorace ta fara takawa dakin dafe da kirji har ta isa bakin dakin ta kasa shiga, ita kuwa Khadija dama saida ta tabbatar ta taho side din kawai sai jawo Ashraf tayi ta rike masa wuyan riga, wannan ihun nata shi ya tashe sa yana ganinta ya razana ya fara kokarin kwace kansa ita kuwa ta kama rigarsa gam gam ta rike, jin yadda ihun ke fita kamar na Khadija ay Zarah batasan lokacin data murda kofar ba ta shiga ciki, wata irin mutuwar tsaye Zarah tayi, batasan lokacin data saki tray din juice din data dauko masa ba da cup duk suka watse kasa, tsayawa tayi cak bata kwakkwaran motsi, jikinta har wani rawa yakeyi har hannuwanta da kafafuwanta, ji take kamar an soka mata wuka a kirji, makoshinta kuwa bayan bugawar da yakeyi har ji takeyi kamar zai shige cikin kirjinta, hawaye kuwa kamar an bude pampo, ita kuwa Khadija ta rike masa riga tana ihu tana ganin Zarah sai ta sake shi taja gefe ta rakube tanata kuka, shi kuwa Ashraf yana ganinta ya mike tsaye a razane yana girgiza kai, ji yake kamar zuciyarsa zata bar kirjinsa, matsowa yayi dab da ita yana ta faman girgiza kai, "Is not what you think...."  Zarah wani irin wawan ihu ta kurma tana gunjin kuka "Dont come near me Ashraf," nuna kanta takeyi jikinta na 6ari tace "Kanwata Ashraf? Khadija is my sister dama ashe son karya kake man? Innalillahi wa inna ilahir rajioon..." ta fara ambata tana masa wani irin kallo, kwatanta yanayin da Ashraf ya shiga ma bata baki ne, ba abinda bakinsa ke furtawa illa "Is not what you think, ban san ya akayi haka ta faru ba...."  kuka yake wiwi ji yayi ya nemi numfashinsa ya rasa gaba daya hankalinshi ya gushe, Zarah toshe bakinta tayi da hannunta kafin ta juya ta fita daga dakin a guje, zubewa yayi kasa hawaye masu zafi na sauko masa, ji yayi zuciyarsa na masa wani masifaffen radadi da ciwo, this is the worse day of his life, mikewa yayi yana ma Khadija wani irin mugun kallo, ji yayi bai taba tsanar mutum a duniya ba kamar yadda ya tsani Khadija, she's heartless and selfish gaba daya karfinsa yasa ya damki Khadija, batayi arba ba taji wani irin masifaffen mari a kumatunta har ji tayi kunnenta yayi dif, kara mata wani yayi a dayan kuncin nan ta fara ihu tana kokarin kwace kanta amma ta kasa, wata irin azaba ce ta rufe fuskarta don wani irin naushi ya kai mata a hanci, wani irin ihu ta saki ta fara kukan fitar hankali, "Ashe dama ke muguwa ce makira bansani ba? Nace maki bana sonki bana kaunar ki, tsanar da nake miki a da ta linka sau dubu, I hate you!" Yana gaman fadan haka ya damko hannunta har akaifa yasa mata nan taji wani zafi ya shigeta, a haka ya dinga janta daga cikin dakin yana fita waje yayi jifa da ita nan ta fadi kasa ta bige kai, nan fuskarshi ta koma ja jijiyoyin wuyansa suka firfito waje zuciyarsa sai tafasa takeyi, ita kuwa Khadija tsoro ne ya shige ta bata taba ganinshi haka ba, nan tsoro da fargaba suka dirar mata, mikewa tayi da niyyar guduwa ya wani damko ta, "Where do you think you're going? Babu inda zakije sai kin fada min abinda kika zuba man nasha." Dukanta yake kamar Allah ya aiko shi jikinta yayi rudu rudu, ihu kawai take kurmawa fuskarta duk ta kumbura, damko ta yayi fuskarshi na wani shaking "Zakiyi magana ko sai na kasheki?" Wani irin dagata yayi ta fara shure shure, dagata yayi zai cillota kasa ta fasa wata irin razananniyar kara tana fadin "Zan fada maka na tuba, kayi hakuri don Allah don annabi, kar ka wullani!" Saukota yayi tare da damke gashin kanta "tell me now!" Kyarma ta fara yi tace "I drugged you, amma wallahi nayi ne saboda ka rabu da Zarah, I want you all to myself!" Wasu marukan ya sauke mata a kuncinta hagu da dama kafin ya fara dragging dinta har side din nasu... 

A 6angaren Zarah kuwa jikinta babu kwari tayo cikin gida. Saidai ta tsinci kanta cikin dakinta zaune akan gado, bata ma san ya akayi ta iso ba tsabar bata cikin hayyacinta, wani irin tukukin bakin ciki ke cinta cikin ranta, hawayen ma sun kasa daina zuba daga idanunta kuka takeyi kamar ranta zai fita, kanta ya fara mata ciwo tsabar kukan da takeyi ba sassauci, data tuno Image din Khadija da Ashraf sai ta sake rushewa da kuka, tana zaune sai ji tayi an banko kofar da karfin bala'i, jajayen idanunta ta daga masu digar hawaye tana kare masu kallo, a tsorace take kallon Khadija ganin kammaninta sun chanza, Ashraf kuwa kamar bashi ba idanunsa sunyi jajir fuskarshi ma haka, tunkud'o ta yayi ta fado gefen Zarah ji kake tim, karasowa yayi cikin dakin ya silale kasa ya kamo rigar Zarah, ganin haka yasa Zarah ta mike da sauri tana sauke numfashi, fizge kafarta tayi wasu hawayen na sake zubo mata nuna shi take da yatsa har wani kyarma takeyi tace "How dare you come into my room Ashraf? Ka fita! Ka fita nace!" Ta kurma wani uban ihu a gigice ya mike idanunsa na fitar da kwalla, "Can't you see? Khadija tayi planning don ta rabamu kin manta sona takeyi? And she can go to any length ta raba mu, wallahi tallahi bansan ya akayi haka ta faru dani ba, I think she drugged me Zarah," Takawa bakin gadon yayi ya finciko Khadija da jini duk ya bushe mata a fuska, gaban Zarah ya wullota har sai data hade da Zarah, ture ta Zarah tayi tare da matsawa baya, Ashraf yace "Ki fada mata! Kifada mata abinda kikayi tell her is not my fault, ke kikayi drugging dina tell her what you just told me outside!" Shiru Khadija tayi nan Zarah ta kure ta da idanu Khadija kuwa ta kasa furta koda kalma daya ce, can ta shiga girgiza kai tana hawaye "Haba Ashraf! What do you think of me? Yes ina sonka amma bazan taba stooping so low ba haka, believe me Zarah ba abinda na aikata..." matsowa tayi kusa da ita tana girgiza kai kamar ta kirki tana sunkuyar da kanta kasa, "Bayan kin tafi sai ya ce min na kawo masa ruwa, ba tare da tunanin komai ba na tafi kai masa ashe kuma yanada mummunar manufa akaina," ta fada tare da rushewa da kuka, Ashraf kallonta yakeyi in shock not able to believe his ears. Ba zato ba tsammani sai jin hannun Zarah Khadija bisa kuncinta, a razane ta dago tana kallon Zarah dafe da kunci, kafin Zarah ta fara magana a fusace "Karya kike makaryaciya! Khadija na tabbatar zakiyi abinda yafi haka ma don ki kwaci Ashraf a hannuna! Amma kisani my love for him is pure and I believe what he just told me..." ta karasa tana kallon Ashraf, cak Ashraf ya tsaya yana kallonta baki sake, wani irin farin ciki ne yaji marar misali, kirjin Khadija wani irin bugawa yayi... Dariyar jin dadi Ashraf ya saki irin dariya sosai dinnan kafin ya matso daf da Khadija "Alhamdulillah naji dadi da Zarah ta yarda dani you are nothing but evil, selfish and heartless! You tried to separate us but your plan has failed! Khadija na tsane ki tsana mafi muni! Ban taba jin na tsani mace ba kamar yadda na tsane ki Khadija! Kuma wallahi komai zakiyi bazan taba sonki ba bazan kuma aure ki ba," Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Zarah, "Zarah ina sonki son da ban taba yi ma wata ya mace a duniya ba! Bazan taba iya cutar da ke ba, bazan taba iya jefa ki cikin ko wane  irin mugun hali ba, baxan taba so na zama sanadin zubar hawayenki ba, bazan so in ganki cikin bakin ciki ba ko yaya yake, I respect women alot burina bai wuce na saki farin ciki ba, da kika gudu daga side dinmu na tsorata a tunanina shikenan zaki tsaneni ashe ba haka bane, ban taba haduwa da mace mai saurin fahimta ba kamar ke, I will never forget yardarki agareni, thank you so much Zarah..." bazan iya kwatanta maku irin kallon da yake mata ba a yayin da yake fada mata wadannan kalaman, gaba daya jikin Zarah ya mutu baki sake take kallonsa tsabar yadda yake furtar kalamansa with pure sincerity, Khadija kuwa tsabar bakin ciki ma fita tayi daga dakin don ji take bata taba yin abu yayi failing ba kamar yau, murmushi Zarah tayi tana share hawayen farin ciki kafin tace "Koda kaga na bar side dinku zafin abinda nagani ne da kishi ba komai ba, amma na yarda dakai nasan bazaka taba cin amanata ba," Shiru yayi cike da farin ciki, yana kallonta, kallonta yakeyi cike da so da kauna kafin ya juya ya fita daga dakin yana murmushi, ya fita parlor daidai kofar fita yaji an damko masa hannu, juyowa yayi yana binta da kallon tsana, wani irin wawan mari ya dauke ta dashi har sai da sawun hannunsa suka bayyana saman kuncinta, nunata yake da yatsa kafin yace "Ki fita daga harkata babu ruwanki dani! Kuma kar ki sake tabani daga yau, if not sai na yanke hannuwanki." Muryarshi har wani rawa takeyi sannan ya tunkudeta ta fada kan kujera, kafin ya juya a fusace ya bar parlon....




Kuyi hakuri da wannan ba charge nepa sunki kawo mana wuta kuma😂❤️🤝

No comments: