Saturday 31 July 2021

YAR AGADEZ PAGE 39

 YAR AGADEZ

 

 

              {Page 39}



To read all my books click the link below👇🏻

Maryamsbello.blogspot.com




-----

A hankali ta shiga bakinta dauke da sallama tsaye tayi bakin kofa dauke da tray din hannunta ganin yana faman hada kayansa cikin akwatinshi, wata yar faduwar gaba taji wai gobe fa zai tafi? Ji take kamar in ya tafi sai ya shekara bai dawo ba, dagowa yayi yana kallonta da mamaki yace "Zarah?  Me kikeyi a bakin kofa? Ki shigo mana." A sanyaye ta shigo ta aje mood dinta duk ya chanza ganinta haka yasa shima mood din nasa ya chanza a take, "Abinci na kawo maka, na kula kwana biyu ka saba zama da yunwa ko Ashraf?" Zama yayi ya jawo tray din ya bude warmers din, murmushi yayi ganin favorite dinsa ne ta kawo masa amma yau dinnan bai jin zai iya cin abincin, don kwata kwata baida appetite, cin abincin yake ba don yaso ba don shima kewarta ce ke dawainiya dashi, "Goben karfe nawa zaka wuce?" Ya hadiye abincin dake bakinsa yana dubanta yace "Wallahi flight din safe ne na karfe tara," wani abu taji kamar ta rusa ihu can dai tayi karfin halin cewa, "Tou yanzu in ka tafi sai yaushe kuma?" Shiru yayi kamar mai tunani yace "Ay bazan dade ba, da naje zanwa Abba maganar aurenmu, duk da nasan sai anyi gwagwarmaya da matarsa kila ma tasan makircin da tayi ya hana ni yin auren." Ya fadi cike da damuwa, itama da damuwa a fusakanta don kuwa ta san labarin Umma kaf ya fada mata babu abinda ya boye mata, tace "Ay Allah yafita inshaAllah, besides bamu fatan ace har yanzu tana gidansa ma ya kamata ace Abba ya gano halinta yayi waje out da makirar." Yayi murmushi "Allah yasa haka da sai nafi kowa murna, don yadda na tsani matarnan kamar na kasheta nakeji." Tace "Kar kace haka, inshaAllah ma basu tare kaga shikenan bakada sauran wata damuwa," yace "InshaAllah zanso inga irin tarbar da Abba zaiyi mun," ya fada kwalla na cika masa idanu, tayi karfin halin kawar da zancen, "Bari na tayaka packing din." Ta fadi tana mikewa ta nufi wurin kayansa tana packing din cike da nutsuwa, a haka ya tuttura abincin don kar tace ay ta kawo masa abinci amma bai ci ba. Yinin ranar a tare suka wuni jone, gaba daya ba karamin missing din juna zasuyi ba. Da ka kalli Zarah kasan gaba daya cikin damuwa take, shima ne yake dan kwantar mata hankali akan cewa fa ay sun kusa mallakar juna saura kadan ya rage InshaAllah, hakan ne ma yasa ta dan saki ranta har ma tana dan walwala kadan. A bangaren Khadija kuwa tafi shiga tashin hankali sai dai ko kadan bata bari ba ta nuna komai ba, har ma ita ke consoling Zarah tana bata baki.

Washe gari yana gama sallar asuba ya fara shirin tafiya, ya fito wanka yana faman tsane jikinsa gaban mirror Yasir dake kwance bisa gado ya farka daga bacci kenan yana kallon aminin nasa yace "Zadai ka tafi ka barmu da kewa Ashraf, kasan ance ba mutuwa ake ma kuka ba sabo ake ma kuka, zamuyi missing dinka abokina." Ashraf yayi dan murmushi yana jin wani iri a cikin ransa ya juyo sannan yace "Wannan haka yake, am going to miss you too." Daga haka ya cigaba da shiryawa, wata shadda dark blue ya saka da matching hula sai kyalli takeyi, yayi mugun kyau tsab ya kimtsa ya kara gyara akwatinsa ya kai parlor, yana kallon Yasir yana duba time yace "Karfe takwas da minti sha biyar kana ganin zaka iya kaini airport yanzu?" Yasir yace "Eh amma ka bari kayi breakfast mana sai muje ko nasan yanzu mutuniyar taka zata kawo maka ay." Yayi murmushi don yasan gaskiya ya fada amma bai jin zai iya cin abincin saidai kawai ya hada tea yasha. Aikuwa sai ga yar halak din da sallama ta shigo dauke da katon tray, kanta na kasa ta gaida Yasir da Ashraf sannan ta aje tray din, dagowa tayi suka hada ido ta sauke kanta da sauri tana murmushi, mayar mata yayi ya sauko kasa yana fadin, "Ay da baki wahalar da kanki ba Zarah, saboda tea kawai nakeso insha kafin na tafi." Yasir ya juyo yana fadin "Nidai daka daure kaci abincinnan Ashraf, traveling with an empty stomach is not right." Ashraf yace "Ay nace zansha tea, ya isheni fa." Yasir yace "Okay tou ni ka bar min su na cinye." Zarah ta mike jikinta babu kwari ta fita daga dakin gaba daya she's not herself, bata taba tunanin zata ji wannan feeling din ba sai yau. Da kyar Ashraf ya tura tea dinnan yana faman tunano yadda yaga mood na Zarah take shima sai ya dinga jin ba dadi cikin ransa, rabin cup kawai yasha ya mike ya cire charger dinsa a jikin socket, ya dauki wayarsa ya kalli Yasir "Tou nidai zan wuce Yasir." Yasir ya mike ya zura jallabiya ya dauki key din motarsa suka fito daga dakin bayan ya rufe da key. Yasir ke ja masa akwatin har bakin kofar main entrance ya barshi a nan sannan suka sa kai ciki, parlon babu kowa hakan yasa Yasir yace bari ya kira Mummy din a daki, bai dade sosai ba ya sauko shi da Mummy, Khadija da Zarah suna binta a baya, zama tayi a gefensa tana murmushi tace "Wai tafiyar ta taho haka?" Ya sunkuyar da kansa kasa ya zauna yace "Eh wallahi Mummy yanzu zan wuce ma." Tace "Ikon Allah, tou Allah ya tsare hanya Ashraf ya kai ka lafiya." Yace "Ameen Mummy, nima na gode sosai da dawainiyar da kukayi dani Allah ya saka da alkhairi." Tace "Haba babu komai Allah yayi maka albarka." Ya amsa da amin sannan ya mike duk su Zarah suka mike suma fir taki yarda su hada idanu don kiris ya rage ta fashe da kuka kuma bata so haka ta faru. Har bakin mota suka raka shi Yasir ya sa masa akwatinsa a booth, yayi ma su Zarah bakwana su Khadija ma duk sukayi masa Allah ya tsare kafin Yasir yaja motar ya fita daga gate. Har airport ya kaisa saida ya tabbatar ya shige sun fara boarding sannan ya juyo cike da kewa ya dawo gida.

-----

Gab da masauratar agadez taki kadan ya tsaya yana kare ma gidan kallo, yana murmushi yana tuna abubuwan da suka faru shekarun baya, komai yana dawo masa fresh da kalar rayuwar da yayi, nan Hoodah ta fado masa a rai saida yaji wani iri take yayi saurin kawar da tunanin daga ransa, yafi miti sha biyar tsaye ya zurfafa cikin tunani kafin ya dawo hayyacinsa da yaji guards na faman gaishe shi ko wane na kallonsa cike da mamaki da kuma farin ciki, don shi sam baima san ya iso gate ba saida yaji muryoyinsu tukunna yayi firgit, "Allah ja zamanin Yariman agadez! Allah ya kara maka tsawancin rai, barka da isowa dan sarki jikan sarki takawarka lafiya yarima! An gaishe ka yarima!" Suka fada cike da murna suna kawo masa gaisuwa, karbar masa kayansa sukayi da sauri suka wuce ciki dashi, baisan lokacin da yayi murmushi ba idanunsa cike da kwalla ya wuce ciki gabansa na dukan uku uku, "Assalamu Alaikum." Abba na zaune a fada ya juyo a firgice gamida mikewa tsaye, Idanunsa ya kwalalo waje tare da bakinsa ya bude yana kallonsa cike da mamaki, "Ashraf!" Ya furta cikin tsananin farin ciki da mamaki sannan ya fara takowa kamar mai counting steps ya iso daf dashi tare da damko masa kafadu da duka hannayensa, kallonsa yakeyi from head to toe kafin ya janye hannunsa ya fara taba masa fuska, "Ashraf kaine? Ashraf ina ka tafi ka barni lokacin da nake bukatarka a kusa dani? Ashraf ina ka shige tsawon lokacin nan ba tare da kako waiwayi gida ba, baka nemeni ba ko sau daya, bansani ba ko kana raye ko baka raye Ashraf." Ya fada baisan hawayen na zurara daga idanunsa ba, "Ka yafe man Ashraf abubuwan da nayi maka, ba laifina bane." Ya fada yana mai hugging dinsa gam gam take Ashraf yayi hugging dinsa back yana fadin, "Dole ce tasa na tafi Abba, ina ji ina gani aka rabani da Hoodah duk da kunsan irin kaunar da nake mata, how do you expect me to stay and witness her wedding? Kuma ni Abba ka daina bani hakuri abinda ya riga da wuce tun tuni wallahi ni ban kullace ba, you are like a father to me, ya za'ayi d'a ya kullaci mahaifinsa?" Ya fada yana janyewa daga hug din, Abba kuka yake bana wasa ba, kukan farin ciki, takaici hade da dana sani marar adadi, da sauri Sultan ya shiga goge masa hawayensa yana fadin "Ka daina kuka Abba, ba gashi na dawo ba?" Abba yayi murmushi sosai ya kamo hannunsa yana fadin, "Muje kaga Kaka tana can kwance tsufa ya kawo kai bata ma jin dadi sosai." Da sauri Ashraf yace "Kaka batada lafiya?" Abba yace "Kasan jikin tsufa yau da dadi gobe babu, amma dai muje ka ganta yau jikin da sauki ay." Ya fada suka ficewa daga fada. Saida Ashraf ya natsu yaci abinci, yayi wanka yayi sallah ya huta sannan suka kebe shiga Abba cikin parlor suna zaune Abba yace, "Ashraf ina ka tafi tsawon wannan lokacin baka dawo ba?" Ashraf yayi murmushi "Abba ina gidansu abokina Yasir wannan dan makarantar mu dinnan?" Abba ya ware idanu "Dama wai can ka tafi? kaji rashin sani kuma ni kwatakwata ban kawo ma raina ba." Ashraf yace "Abba ay banida aboki sama da shi, nasan xai karbeni hannu biyu biyu sheyasa ma na tafi can, kuma alhamdulillah sun bani kyakkywar kulawa." Abba yace "Alhamdulillah, ay da yake mutanen kirki ne." Ashraf ya gyara zama "Abba ina Umma?" Abba ya numfasa "Na rabu da ita Ashraf." Ashraf da wani tsantsan farin ciki and also shocked yace "Ka rabu da ita? alhamdulillah finally it has happened, na dade ina jiran wannan ranar Abba, alhamdulillah." Abba yace "Am sorry Ashraf bansan da wace kalar mace nake tare ba sai ranar da Allah ya kamata na gane komai, and that's when it hit me, na gano gaskiya da kuma halinta gaba daya, nayi da nasanin haduwata da ita, ta rabani da kowa nawa, ta rabani da matata, ta rabani da kai, ta rabani da yata, da yake banida hakki a kanta tana can asibiti rai a hannun Allah," Ashraf a sanyaye yace "Umma ay she's evil and heartless, bakomai Abba dama komai na duniya mukaddari ne haka Allah ya kaddara," sai kuma yayi shiru na yan seconds kafin yace "Abba Hoodah fa? How is she? How did she take the news that Umma killed her mother?" Abba ya numfasa "She's fine Ashraf, naje ay har Niamey nayi magana da ita, I apologize for my actions, kuma ta fahimceni amma abinda yafi bani mamaki shine Hoodah knew all along Umma ce ta kashe mahaifiyarta bata fada wa kowa ba, tace Umma ce ta mata gargadi mai tsoratarwa akan idan ta sake ta fada sai ta kasheni nida kai da kaka kamar yadda ta kashe mamanta haka zata kashe mu muma, I was so heartbroken that my own daughter endured all this pain alone." Ya numfasa "Anyways, wannan duk ya zama past InshaAllah..." Ashraf ya share hawayensa yace "Allah sarki Hoodah she endured alot, how is she now Abba?" Ya kuma tambaya out of curiosity gaba daya ya kasa hana kansa yiwa Abba wannan tambayar, Abba yayi murmushi "She's fine Ashraf, she's now a queen and soon to be mother InshaAllah." Da sauri ya kalli Abba "Mahaifin Sultan ya rasu ne?" Abba yayi murmushi "A'a, alot has happened Ashraf, he was sick I mean shida matarsa they were both attacked and almost killed, amma Allah cikin ikonsa sun dawo suna samun sauki, he just decided to step down ya bar ma dansa," Ashraf yace "Ikon Allah, su waye sukayi attacking dinsa?" Abba ya numfasa "His own blood Ashraf." Ashraf yayi salati "Wai me duniyar nan ta zama ne? Ace jininka shine yake son ganin bayanka, Allah shi kyauta." Abba yace "Ameen, so ya mutanen gida?" Ashraf yayi murmushi "Lafiya lau Abba, yanzu ma wani dalili ne ya dawo dani." Abba yace "Dama ba dawowa kayi ba kenan? Dalili ya kawo ka?" Ashraf yayi murmushi "Dawowa nayi Abba, amma kuma akwai wata magana kuma." Abba yace "Maganar mey?" Ashraf yace "Maganar aurena...." abba ya juyo da mamaki saman fusakansa da farin ciki kuma "Aure Ashraf? Who is the lucky girl?" Ashraf ya sadda kansa kasa "Abba sunanta Zarah, kanwar Yasir ce a can gidansu muka hadu, mun fahimci juna dama shine nazo maganar aurenmu." Farin cikin da Abba ya shiga ma bata baki ne, nan ya jawoshi ya rungume cike da murna "Alhamdulillah, me ake jira a fara shirye shirye? Kuma yaushe ya kamata a tura? Sai maganar lefe ya kamata azo a fara hadawa! Ya kamata na kira Hoodah a sanar mata ka dawo alhamdulillah alhamdulillah Allah yasa albarka!" Da murmushi shimfide saman fuskansa yace "Ameen thank you Abba."

-----

Khadija ce a dakin Mummy lokacin Mummy din na kasa ta sanya ta gyaren daki da wankin bathroom, bathroom din ta fara wankewa, sai ta fara tattara wasu hijabs na Mummy zata sanya mata a wardrobe, tou ita kuma tana budewa by mistake sai wani katon album da wani diary suka biyota suka watse kasa, dukawa tayi ta fara tattarawa kawai sai ta dauko wani picture tsohon hoto ne na wata mata rike da baby, sai kuma ta dauko wani hoton na same matar nan da Mummy kamar su daya kamar an tsaga kara an karya, sai ta dinga bin hotunan da kallo tana kuma dauko wasu a razane take ta dinga ganin hotunan matar nan da Mummy yawanci kamar ranar suna ne, matar na dauke da baby wanda Khadija ta fahimci kamar itace a hoton, tou amma me takeyi hannun matar kuma ya tagansu tare da Mummy? Diary din ta dauko dake yashe kasa ta fara budewa a razane ta mike tsaye tana karanta shi hawayen na sauko mata, hoton take bi da kallo kasa tsayuwa tayi ta zube bisa gado tare da fashewa da wani irin kuka, Kuka take kamar ranta zai fita kafin ta mike a fusace ta sauka kasa, Mummy na kitchen tana hada drinks tana sawa a fridge kawai sai ganin Khadija tayi rike da secret diary dinta da kuma album din da take boyewa shekara da shekaru, shocked Mummy ta zama ta nufi inda Khadija ke tsaye tana kokarin tabata, ja baya tayi da sauri tana cigaba da kuka kafin tace "Karki tabani! So dama all this while you are hiding this away from me? Mummy why?!" Mummy ta fara kuka tace "Calm down Khadija I can explain...." kuka Khadija ta fashe da shi tare da fasa wata irin razananniyar kara ta zube kasa, itama Mummy binta kasan tayi cikin karaji ta dafata, "Mummy ashe bake kika haifeni ba? And on top of that ni ba yar sunna bace? Am your niece? How is that all positive?" Mummy ta dafata wata uwar kara ta fasa tana mikewa tsaye da sauri, "Nace karki tabani Mummy you betrayed me!" Mummy ta girgiza kai "Ba haka bane Khadija, kema kinsan I have loved you more than my own children, na kula dake fiye da yadda na kula da yayan cikina, na fifita ki daban da yadda na fifita na cikina, I took special care of you, and I make sure na baki soyayyar uwa da kika rasa shekarun baya da suka shude!" Ta fada tana goge hawayen idonta, "Ni da Nafisah mun kasance tagwaye, haka muka tashi ba iskanci tayi ta sameki ba fyade akayi mata, ta rasu bayan sunanki da kwana takwas, nikuma sai na dauke ki na cigaba da baki kulawa," karar fashewar abu sukaji dukkansu suka juya suna kallon Zarah data zubar da glass cup din dake hannunta da tray, Hawaye take zubarwa kamar da bakin kwarya tana kallon Khadija da wani irin shock, "Khadija ba yar sunna bace?" Ta tambaya tana bin Mummy da kallon mamaki, a fusace Khadija ta juyo tana kallon Mummy! "This woman here betrayed me! Ta boye man gaskiya sai dana gano da kaina and now she's trying to explain things to me! I don't wanna hear anything I feel betrayed!" Ta fada tana ja baya kafin tayi sama da gudu tana kuka, Zarah ta juya zata bi bayanta Mummy ta tsaida ta "Let her be for now Zarah, bazata saurareki ba, I didn't betrayed her i am just waiting for the right time to tell her, she's my daughter too she's just angry for now but she will understand am sure, Ina sonta kamar yadda nakesonku, the reason I hide it from her is because she's too young to know her status, it's gonna ruin her entire life, she will be distracted and not to focus on anything...." hugging dinta Zarah "It's fine Mummy please stop crying, na maki alkawari xan dawo maki da yarki kamar yadda kuke da, kawai she's angry and heartbroken now, but I will fix everything inshaAllah, stop crying." Ta fada tana goge mata hawayen fuskanta....

-------

Tunda abinnan ya faru Khadija ta kulle kanta cikin daki babu abinda takeyi sai aikin kuka, kuka take razga kamar ranta xai bar jikinta, Mummy sun buga kofa sunyi magiyar, sunyi roko, sunyi lallashin amma duk a banxa, har dai Yasir babu irin magiyar da bai mata ba amma duk a banza kuma tana jinsu sarai, har spare key suka dauko amma unlucky for them ta bar key ta jikin kofar sun kasa budewa, Mummy da hankalinta ya fara tashi tace tou ko a balle kofar aga ko kalau take, jin haka yasa Khadija ta fara magana cikin dakusashiyar muryarta "Kada wanda ya balla man kofa, nace maku bazan fito ba dole ne wai? Am no longer part of your family so please leave me alone I beg all of you!" Mummy ta dafa kofar ta dora kanta bisa tana kuka tace "Ki daina cewa haka Khadija, you are my niece so kar ki sake cewa you are no longer part of our family! Khadija abinda yasa na boye maki saboda banaso ki shiga damuwa Khadija! I want you to be happy and live a normal life Khadija, Khadija you are my daughter and I love you as well, kiyi hakuri idan boye maki da nayi yayi hurting dinki it was never my intention, inda nasan haka zakiyi feeling da ban boye maki ba Khadija da tun tuni zan fada maki, amma kiyi hakuri kuma yanzu da kikasani I don't want you to feel left out mu cigaba da rayuwa kamar da! Don Allah ki bude man kofar nan yata, indai har kin daukeni a matsayin mahaifiyarki kizo kibude man kofar nan Khadija...." shiru Mummy tayi kirjinta na dukan tara tara ba zato kawai sai ji sukayi ta murda key a hankali ta bude kofar, tsaye tayi fuskar nan duk ta kumbura taci kukanta ta koshi, a hankali Mummy tayi hugging dinta tare da fashewa da wani irin kuka itama haka Khadija, "Mummy am sorry kiyi hakuri da munanan kalaman da na fada maki I didn't mean any of them, I know bake kika haifeni ba but the love I have for you is strong, I still love you Mummy!" Kara hugging dinta Mummy tayi "It's okay my daughter, komai ya wuce kinji ko?" Ta gyada kai nan tayi hugging Yasir da Zarah sannan ta juyo tana kallon Mummy, "Mummy alfarma daya nake nema a wurinki..." da murmushi fuskar mummy tace "Anything sweetheart?" Khadija tace "Inason in karasa karatuna a nan I don't want to go back to Uk anymore please Mummy." Mummy ta gyada mata kai tana gyara mata gashin kanta "It's okay, I will see what I can do okay? Muje kiyi wanka kizo kici abinci." Hannunta Mummy ta kamo suka shiga ciki tare...

********

Haka rayuwar ta cigaba da gudana, wanda aka fara harkar shirye shiryen biki babu kama hannun yaro, Abba ya tura anje sa biki don gaba daya akayi da gaisuwa da sa biki, inda aka saka bikin sati biyu kacal masu zuwa, nan kuwa Ashraf babu abinda yake hadawa sai lefe sai kuma gyaran gida akeyi bangaren da zasu zauna shida amaryarsa, su Hoodah ma nan da sati daya zasu iso, shi Sultan shida Abbi sai ranar daurin aure zasu zo. Daga Nigeria Mummy tayi hiring wata mata a maiduguri ta fara gyara mata yarta, dilka, halawa da tauren wutan jiki ake mata ba kama hannun yaro, tunda kurarren lokaci ne na kwana goma kacal ake mata, siyayya kuwa mummy take ta mata na kayan gida da decoration da sauransu don har ta kammala na kitchen kaf, saboda nisa so take sai an kusa bikin a fidda rana daya aje ayi jere. Khadija ita kadai tasan bakin cikin da take ciki amma ta dake baka taba gane komai da ita ake shirye shiryen biki ba kama hannun yaro. 

------

BUDAN KAI! 

Mutane an taru kowa kagani yasha kyau ba kadan ba, kawayen Zarah anko suka sha, hall din ya sha decoration amarya Zarah basu iso ba itada kawayenta amma mutanen yawancin sun iso, wakar kujerar tsakar gida ke tashi ga wurin sai kyalli yakeyi yasha kyau ga fitilu sai walwal sukeyi, ba'a dau lokaci ba Zarah ta iso itada kawayenta da ango da abokansa, nan mc yace kowa ya zauna amarya ta iso nan da nan mai hoto da video suka zama ready, wata wakar larabawa akasa mai shegen dadi a hankali aka fiddo Zarah daga cikin motar woooo tayi bala'in kyau tasha white bridal gown komai in white tayi amma gaba daya fuskarta a rufe take, bayan sun jera in line Khadija ce a gaba sai Zarah tsakiya sai kawayenta suka jera a baya nan aka kara sautin wakar masu hoto na gaba, suna daukarta nan suka fara shigowa ciki har suka rakata inda zata zauna wurin yasha decoration, bayan ta zauna nan mai video da hotunan sukayi nasu aikin har finally mc ya kira wata ta bude taron da addu'a, nan kuma aka fara shagulgulan biki ba hannun yaro. Khadija ce wayarta ta fara ringing can ta fita waje tana waige waige alamun marar gaskiya, saida tayi nisa inda babu kowa a wurin sannan ta daga wayar ta kai kunne ta fara magana a hankali, "Inata kiran number ka bata shiga Fahad, wani taimako nake nema da gaggawa!" Yace "You are my best friend remember in school? So ko meye just ki fada man kai tsaye zan maki inshaAllah." Kwantar da murya tayi tace "I want you to kidnap my sister!"

No comments: