Sunday 10 September 2017

AUREN FANSA 43

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS

 _We don't just entertain and educate, we touch the heart of readers_

P.M.L


Dedicated to First Lady 😍

PML You are the best Allah ya bar mu tare👌🏼😉😌

     
                🌹43🌹

Cikin wani irin yanayi yace "What?"
Bilki kuwa k'ara d'aga murya takeyi tana fad'in
"Ke Amina ba mu muka haife ki ba."
Laila tana ta d'an zunguranta akan ta bari ina bata ma saurareta ba. Baba ya sunkuyar da kansa yana mai tsananin jin haushin Bilki, ko kusa bai so Meenah tasan matsayin ta ba, a ganinsa hakan zai iya haifar mata da damuwa sosai, da yawan tunani, duk da yasan sanin matsayintan ba wani abin bane don kuwa cikakiyyar 'yar sunnah ce, hakan yasa ya tattaro nutsuwarsa yana kallon Meenah data tsareshi da ido kamar yau ta fara ganinshi, yace
"Kar ki damu zan sanar da ke komai, Faruk kammala aikinka sai mu tattauna."
Da k'yar Faruk ya tattara nutsuwarsa amma gaba d'aya hankalinsa naga Meenah da kuma son jin in da gaske ne zancen Bilki.
Police guda biyu ke tsaye a waje Faruk ya kirasu suka shigo, da hannu kawai ya basu order wanda su kad'ai suka san me yake nufi, sara masa sukayi sukace
"Yes sir..."
Fita sukayi ba'a jima ba sai gasu sun dawo da matasan maza majiya k'arfi su kusan biyar masu k'iran 'yan daba, ko su Zarah sai da suka tsorata da ganinsu, sai wani huran hanci sukeyi suna zare idanun kamar kura taga nama. Take jikin Laila ya fara 6ari don kaf d'insu ta ganesu, haka zalika ita kanta Bilki sai ta fara salati tana bada hak'uri da neman gafara.
Faruk yace
"Wad'annan sune wad'anda kukayi assigning suka aikata kisan da hannunsu, suka kashe min iyayena..."
Take tsikar jikinsa ta tashi idanunsa suka kawo ruwa, ya kai dubansa ga Anisah yaga tana kuka itama, duk sai ta basa tausayi a ransa yace
"Ke kenan da bakida wayau a lokacin bare kuma ni."
Bilki tace
"Ni dai bansansu ba. Billahi bansan ko su waye ba."
Baba ya daka mata tsawa
"Yi mana shiru a nan! Ko so kike sai na sa an harbe ki ne da bindiga? Ga laifi an kamaki dumu dumu amma kina k'aryatawa?"
D'aya daga cikin 'yan daban suka ce
"Tabbas nine wanda Hajiya Laila ta kira take sanar dani irin aikin da za'ayi musu, sannan sukayi min alk'awarin mak'udan kud'i idan na aikata abinda suka sani, ita kuma Hajiya Bilki ita bani umarnin kisan tace idan ban aikata ba to tabbas ni zatasa a kasheni, haka sukayi min ko wanensu zai bani dubu d'ari biyar biyar idan aikin ya kammala. Don haka na samu abokanan aikina na sanar musu yadda zamuyi aikin. Ko bayan faruwan haka sai da suka mallaka min gida da mota wai a cewarsu farin cikin abinda nayi musu ne."
'Yan sandan suka matso kusa da su Hajiya Laila sukace
"You're under arrest for the murder of Hajiya Reemah and Alhaji Adam, you have the right to remain silent, because anything you said will be used against you in a court of law."
"Don Allah ka gafarce ni, ku yafe min abinda nayi."
Ta matso kusa da Meenah tace
"Ki yafe min irin cin zalin da nayi miki a baya, nasan kin sha wahala a wurina ki yafe min."
Baba yace
"Kamar yaya?"
Zarah ta matso tana share hawaye tace
 "Baba, tunda na taso nake ganin yadda Meenah ke fuskantar wulak'anci, mugunta da kuma zalunci a wurin Mami, bugun yau daban na gobe daban, ga sata aiki kamar jaka, abinci kuwa data gama wannan sai a sata wani, wanke wanke, wanki, wankin toilets, shara, goge goge, duk Meenah ce keyi. Sannan bata cin abinci sai ka kusa dawowa, haka zata wuni da yunwa ga uban aiki, da ka kusa dawowa zata korata tayi wanka taci abinci yadda bazaka gane ba. Ko nayi yunk'ura fad'a maka sai Mami ta hana, ko tace zata zane ni muddin na sanar da kai..."
Baba yace
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Bilki ashe yadda na d'auke ki ke ba haka kika d'auke ni ba? Tun farko dana san haka kike da ban d'auki amanar maraininiyar Allah na baki ba, amma kisani akwai ranar hisabi kuma Allah sai ya mata sakayya..."
"Na tuba Alhaji, ka yafe min..."
"Bilki kije na sake ki saki d'aya..."
Kowa sai da ya zabura jin sakin da Baba ya yiwa Bilki, sannan ya bita da nasiha da fatan zata gane kuskurenta, haka aka saka musu ankwa itada Laila aka jasu suna tirjewa da maganganu suka fice.
Faruk gaba d'aya jikinsa yayi sanyin abinda yaji, wai Meenah marainiya ce?
"Me nayi? Na d'auki alhakin baiwar Allah." Ya fad'i a cikin ransa.
Duk da daurewarsa sai da k'walla suka zubo masa, ya share sannan ya bi bayansu Bilki inda Anisah ma tabi bayansa, suka bar gidan. Suna fita Meenah ta kifa kanta a hannun kujera tayi ta kuka kamar ranta zai fita, Zarah na ta aikin rarrashinta inda itama kukan takeyi, Baba yaja su suka shiga cikin d'aki yana ta faman rarrashinsu.


*****

Daddare kowa ya nutsu a parlor amma daka kalli kowa kasan ba a cikin nutsuwa suke ba.
Baba ya maida dubansa ga Meenah yace
"Dalilin da yasa ban ta6a fad'a miki ba shine, na farko baniso kiyi kukan maraici, na biyu baniso ki shiga damuwar rashin iyaye, don kinsan yawan damuwa ga yaro ba abu bane mai kyau, amma ina mai baki hak'urin 6oye miki da nayi duk da nasan you have the right kisani."
Nan ya kwashe labarin komai ya fad'a mata, su waye iyayenta da kuma yadda akayi ta dawo hannunsu da zama. Sannan ya d'ora da cewa
"Duk da nasan banyi niyyar fad'a miki ba amma wallahi ji nake kamar an sauke min wani nauyi da ke bisa kaina,  Meenah bana fad'a miki maganar nan ba don ki shiga damuwa ba, a'a na fad'a miki ne bisa tirsasawa da akayi min, sai dai ina rok'onki da kada ki d'ora damuwa a ranki don Allah, sannan ki cigaba da yiwa iyayenka addu'ar samu rahama daga Allah, inda suka tafi muma zamu iske su wata rana."
Ya fad'a da guntun k'walla a idanunsa. Meenah ta share hawayenta tace
"Wallahi Baba ban ta6a sanin cewar bakai ka haifeni ba saboda babu alama, duk wani gata ka min shi, sai dai nace Allah ya saka da alkhairi, amma kasani har yanzu bazan daina ganinka a matsayin mahaifina ba saboda kaima mahaifina ne saboda yaya kake ga mahaifiyata don haka duk d'aya ne, kuma insha Allah na maka alk'awarin cire damuwa a raina."
Yace
"Alhamdulillah, ke kuma Fatima kema kar ki shiga damuwar ganin mahafiyarki da aka kama, ki cigaba da yi mata addu'a."
Tace
"Insha Allah Baba."
Faruk da ke zaune jikinsa sanyi k'alau yace
"Baba inada magana idan an bani dama."
Baba yace
"Bismillah mana."
Faruk ya sunkuyar da kansa saboda nauyin maganar amma kuma dole ne ya fad'i, don ya samu su yafe masa.
Yace
"Baba, ka gafarce ni, nayi kuskure babba."
Sai kuma yayi shiru, Baba yace
"Kuskure kuma Faruku? Na me?"
Ya kalli Meenah yaga shi d'in take kallo, sannan ya maida kansa k'asa yana wasa da zoben azurfar da ke hannunsa yace
"Wallahi Baba da zan auri Meenah ba sonta nakeyi ba... daman don na d'auki fansar abinda akayi wa iyayena ne sheyasa na aureta..."
Ras! Ras! Gaban Meenah ya yanke ya fad'i,  ya d'ago ya kalleta yaga idanunta sun kad'a sunyi jawur! Tana masa kallon mamaki had'e da tsana...
"Meenah nasan nayi kuskure a nan amma wallahi..."
Da gudu tayi ciki tana kuka mai sauti...!
Zarah ta bi bayanta da gudun itama tana k'wala mata kira...




MSB💖

No comments: