Friday 15 September 2017

JAKAR MATA page 01

🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀
     *JAKAR MATA*
🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀🤷🏼‍♀


*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    we don't just educate and entertain but we also touches the hearts of the readers.



Na

*MRS FAWWAZ*
*FARIDAT MUSA(Sweery)*
*JANNART LAMEE'DO*
*MAMAN KHADIJA*
*MARYAM S BELLO (MSB)*

*THE UNTOUCHABLES ARE BACK KEEP FOLLOWING US FOR BETTER STORIES*👌🏼

# *WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
# *IG PML WRITERS*
# *https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
# *http://maryamsbello.blogspot.com*

_wannan sune safikan mu da zakuna ziyarta dan neman nvl d'in mu. Fatan mu Allah ya baku ikon zuwa Ameen_

Page 1 by *Faridat sweeeery*




Bissmillahirrahmanurrahim

Gargad'i

Wannan littafi mai suna Jakar mata k'irk'ira mukayi bamuyishi dan wani ko wata ba,sannan bamu yarda wani ko wata ya juya mana littafi ta wani siga ba duk wanda yayi haka bamu yafe ba,
Fatanmu Allah yasa sak'on da muke k'ok'arin aikawa ya isa ga al'umma musamman masu hali irin na Jakar mata.


Wannan shafin naki ne sukutum d'insa *FATIMA MAMYN JIDDAH* natayaki murnan bupday d'inki Allah ya k'aro shekaru masu albarka.



Zaune take a gaban dressing mirrow tana chab'a kwalliya kaman wata amarya da alama dai wani waje zataje mai matuk'ar muhimmanci daga ganin kwalliyar da takeyi, ta shafe nan ta fente nan sai datayi kusan 1 hour tana abu d'aya nidai sake baki nayi ina kallon kwalliya, bayanta kammala ne ta dawo wedrobe neman kayan sawa ta gwada wannan ta canja wannan ita da kanta ta rasa wanda zata d'auka.

Sai data gama ruwan idonta sannan ta d'auko wata atamfa mai ruwan shud'i wanda akaci mutuncin sa da wani lalataccen d'inki duk wanda ya kalli kayan zaiyi zaton bazai shigeta ba tsabar k'ank'antar d'inki.


Da k'yar rigar ta shigeta ballantana skirt d'in sai data had'a zufa kafin tasa Jannart dake gefe sai dariya take Mrs Fawwaz ta toshe mata baki dan karta tona mana asiri aga lab'e mukeyi, sake baki nayi ina kallonta saboda tsabar had'uwar da tayi jaka da takalmi ta d'auko ta mak'ala gyale a kafad'arta sannan ta fito tana chewing gum,batare da tunanin sanar da Mahaifiyarta yanda zataje ba tayi waje a dai-dai gate sukaci karo da Maman kallonta tayi daga sama har zuwa k'asa sannan ta girgiza kai tace "Yanzu fisabilillahi Jalilah haka zaki fita kaman ba 'yar musulmai ba ki duba kiga irin shigan da kikayi?".
Zunburo baki tayi sannan tace "Haba Mama wai meyasa kullum sai kin fad'a mun magana ne in zan fita?, yaci ashe kin gane da banbanci tsakanin zamanin da dana yanzu, da kanku a duhu yake amma yanzu an waye" tsayawa tayi kawai tana kallonta dan ta rasa me mazata ce mata lamarinJalilah sai ita, "Ni na wuce kawai mama" tana fad'a tasa kanta tayi gaba tana karkad'a jiki kaman macijiya,
"Allah ya shirya munke Jalilah ki gane Annabi ya faku".
🤷


Tana fita ta hango wanda yake jiranta a bakin titi yayi parking k'arasawa tayi ta bud'e motar ta shiga peck ya manna mata a kumatu sannan yaja motar suka hau hanya "Bebe ina zamuje ne?" .

Wani fari tayi da ido sannan tace gidansu "Zee-Zee mana kasan sai mun d'aukota kafin mu wuce Vanillah" "ok ba yawa" kid'a ya sake musu kaman zasu tashi sama , chaiii wa'yannan basu san annabi ya faku ba.


A daidai k'ofar gidansu Zee-Zee sukayi parking Jalilah ta fito ta nufi gidan cikin takunta na isa da k'asaita, direct d'akin Zee tayi batare da ta tankawa mutanen data gani a tsakar gidan ba.


A gaban mirrow ta sameta tana rolling gyale a kanta da alama ta gama shiryawa dubanta tayi sannan tace "Ai da nad'auka baki shirya bane wallahi da mun tafi mun barki ina Zuhura take?" Hmmmm ajiyar zuciya ta sake sannan tace "Ai kinsan Zuhura da African time ba tasamu k'arasowa ba" "ai kuwa tafiya zamuyi ba abunda ya shallen…" . kafinta k'arasa maganan Zuhura ta katseta "To marar mutunci basai ku tafin ba".

"Allah yayi saving d'inki 'Yan mata " ha ka suka ringa tad'i harta gama shiryawanta sannan suka fito itama ko kallon arziki batayiwa 'Yan gidansu ba balle su samu jin furucin bankinta Allah ya shirya.













*Untouchables*🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀🏃🏻‍♀

No comments: