Friday 25 June 2021

YAR AGADEZ PAGE 25

YAR AGADEZ

 

 

              {Page 25}



To read all my books click the link below👇🏻

Maryamsbello.blogspot.com



A hankali yayi knocking kofar dakin  amma ga mamakinsa akayi shiru, tun yana sa ran xata bude har ya hakura ya daina knocking din, sam Hoodah bata nuna cewar ma taji knocking dinnan ba, yafi minti goma a haka har dai ya gaji, ajiyar zuciya ya sauke ya fice don tafiya masallaci don yaji ana kiraye kirayen sallar azahar, yana gamawa a hanyarsa ta dawowa ne yake ayyanawa a ransa cewar shifa ya gaji da zaman gabannan da takeyi dashi sai kace wasu enemies? All he knows is that he loves her yana sonta yana kaunarta har cikin ruhin zuciyarsa, saidai ya kudiri a ransa tilas yau zasuyi magana no matter what, dole zata kulashi kuma dole zai nuna mata yana kaunarta don haka dolenta ta yarda, idan ma ta kama ya balle kofar tou babu makawa zai balle ta. Yana dawowa ya shiga ya watsa ruwan dole don ba karamin zafi akeyi ba, dama dai kusan 2 weeks kenan bai tashi wanka sai azahar ta wuce, shin dama haka damuwa take? Shi tunda yake baisan meye damuwa ba sai yanzu da soyayya ta sako shi a gaba yasan ma'anar damuwa. Abinci ya fita waje yasa akayi masa order, daga can yayi tafiyarsa haraba shine bai dawo gida sai bayan sallar isha'i, sashen su Abbi yaje ya tafi dakinsu ya kwanta a nan ya samu yayi bacci, sai goma da kusan minti sha biyar ya farka tunda suka dawo daga agadez dama dai haka yakeyi kullum don indai sashensu ne toh fa bai iya baccin kirki saboda tunanin Hoodah dake sakashi a gaba. Yana shigowa sashen nasu dakin Hoodah direct ya nufa nan ya fara knocking don har yanzu rufe take kofar, tun yana yi a hankali har ya fara bubbugata da karfin bala'i wane zai balle kofan "Hoodah kizo ki bude kofar nan! Idan ba haka ba wallahi I will break it! Haba Hoodah wai ya kikeso inyi da raina? Sonki nakeyi kamar zan mutu tou wallahi kin wahalar dani enough, nace kizo ki bude min kofa Hoodah!" Shiru kakeji Hoodah batada niyyar tasowa ta bude, nan ya dinga magiya, yayi masifar da bala'in, yayi rarrashin ya bada hakuri amma duk a banza. A hankali ya silale a gurin ya dafe kai ya kai tsawon minti talatin a haka ya rasa meke masa dadi, ji yake kamar sonta zai halaka shi baki daya don wani iri bugu zuciyarsa keyi kamar zata huda kirjinsa ta fito, sai da ya gaji da xama a nan ya mike da kyar ya nufi kitchen, custard ya hada mata ya dawo dakinsa ya fara duba spare keys, dukkansu ya kwaso dan shidai baisan wane bane a ciki, daya bayan daya ya dinga saka su babu wanda ya dace dan babu key din a ciki, duk wanda yayi trying bai bude ba sai yasa hannu ya buga kofar da karfi akan tazo ta bude amma yadda kukasan yana magana da bango haka Hoodah ta koma, duka bayan ya gama tying ya rage saura key daya "Hoodah wallahi ko kizo ki bude man kofar nan ko kuma wallahi in balleta, kuma kika bari na balla duk bazamu kwasheta da dadi ba a cikin daren nan! Haba wai me kike maidani?" Yana fadan haka ya zura key din ciki sai gata ta bude! Wata uwar ajiyar zuciya ya sauke, ya buga kofar a zuciye ta bude da karfi daidai lokacin ne Hoodah ta taso zata bude don a tsorace take yadda yake buga kofar ya kuma bata tausayi matuka, yadda ya turo kofar shi yayi sanadin tunkudeta da yayi tayi baya zata fadi yayi sauri ya riko ta, ajiye cup din yayi kan drawer bai damu da masifar da zatayi masa ba...

Kokarin kwace kanta ta farayi daga rikon da ya mata, amma abin mamaki kanshi dake bisa wuyanta sai da taji kamar yana digar hawaye, hankalinta bai kara tashi ba saida taji yana sheshekar kuka yana magiya akan kar ta sake masa irin wannan ya horu horuwa mafi muni, "Hoodah nasan nayi maki babban laifi na aikata kuskure, na maki promises din babu wanda nayi fulfilling, but believe me I do love you so much! Bana tunanin akwai namijin da zai tsinci kanshi a halin dana tsinci kaina Hoodah, abinda nayi is uncalled for I shouldn't have did what I did the anger and everything! Ki yafe mun Hoodah... Hoodah bansan ina sonki har haka ba saida bakya tare dani, it was the worst days of my life, ki dauki duk abinda ya faru a matsayin kaddara mu sake bude sabon page na rayuwarmu, can you love me and trust once again?" Kuka yake har can kasan zuciyarsa, a nan sunfi minti sha biyar a haka while they hugged each other gaba daya zuciyar Hoodah ta kare tausayinsa ne ya cika ta, can tayi karfin halin goge nata hawayen kafin ta dago shi ta fara share masa nasa hawayen, "It's okay ka daina kuka, duk kukan na meye? Ba dan Habibty ta yafe maka bane? Ka manta ranar da ka ajiye ni a kofar gidanmu? Me nace maka? Na fada maka ranar nace zaka dawo kana rokona gafara akan na yafe maka what did I tell you? Ba nace zan yafe maka ba kuma zan fahimce ka ba? Nasan inda ace nice kai zan aikata fiye da abinda ka aikata ma because abubuwan ne gasu nan kala kala ance nayi, amma abinda duk yafi hurting dina da kaki tsayawa ka saurareni, karshe ma Sultan ka daukeni daga gidannan saboda extent din tsanar da kayi mun, shin wai dama haka zaman aure yake? Dama haka soyayyar take?" Hawayenta ta dakata ta share ta kirkiro murmushi tana kallonsa don ta kwantar mashi da hankali don da alama yau kukan nashi baida niyyar karewa, "Yes na taba soyayya I loved my cousin long ago, but bayan munyi aure komai ya chanza, soyayyarka ta shigeni, ba shigar sauki ta mun ba ko tausayi, inata denying amma I couldn't hold it, tausayinka a da sheyasa mun sonka a cikin raina, amma bayan ka chaza halayenka ka rikide ka koma monster nazo har shakkar ka nakeyi bana gabanka saboda kawai anaso a hadamu, amma kamar yadda na fada maka na yafe maka kuma na fahimce ka. Duk abinda na maka bayan mun dawo daga agadez ba'a san raina nake maka ba amma yaya zanyi? Inaso ka dandana abinda na dandana koda kadan ne, inaso kayi realizing how important I am in your life, so ka daina kuka komai ya wuce." Hugging dinsa tayi a hankali tana kuka mai ratsa zuciya, saida suka sha kuka suka gode ma Allah kafin ya saketa gaba daya dole sukaje suka hada wani sabon custard din suka sha sannan suka dawo daki. A hankali ta fara bashi labarin rayuwarta tun yarinta duk abinda tayi going through, da azabar da Umma ke gana mata har kawo yanzu da take a gabanshi, tana kuka yana kuka saboda dana sanin da yayi "Hoodah Habibty, I am truly sorry bansan haka kika taso ba cikin rashin mahaifiya yanzu Abba yana zaune da ita a haka? Anya haka ta barshi? She even killed your mom! Kai innalillahi wa inna ilahir rajioon, am sorry am sorry am sorry Hoodah this shouldn't have happen to you...." Girgiza kai takeyi tuna mata da wannan wound din na kisan Amminta ya dawo mata kamar yanzu take gani, hawayenta ya share mata yayi scooping fuskarta da hannuwansa biyu, "Hoodah look at me, today I am going make you a promise, zan daukar maki fansa she must be brought to justice she can't be roaming around scot free, you don't have to worry, zan daukar maki fansa I promise you Umma will regret ever been born!" Gyada kai takeyi tana gunjin kuka da sauri tayi hugging dinsa tana cigaba da kuka "Thank you thank you so much...." ya dago ta yana share mata hawaye "So where is this your cousin?" Ta share hawaye "Bansan ina yake ba, he left after Umma ta fada mana maganar aurena har yau maganar da nake maka ban sake ji daga garesa ba, ya kashe wayoyinsa ba'a samunshi." Ya share mata hawaye "It's okay, Umma is a cruel woman, amma karki damu sannan inaso kisa ma ranki kinga shifa komai mukaddari ne daga Allah, komai da kikaga ya faru a rubuce yake bawa bai isa ya guje wa kaddararshi ba, sai kiga abinda ka kwallafa wa rai kanaso ba shi bane alkhairi sai wanda bakaso, I even realized I have never loved Khairy before, sai da kika shigo rayuwata sannan nasan menene asalin so, Hoodah I love you so much,". Batasan lokacin datace "I love you too." ba... wani irin daukarta yayi ya dinga juyata tsakar daki sannan yayi hugging dinta ya dinga aika mata da sakonnin kisses ta ko ina yana nuna mata how much she means to him....

***

"Malam wallahi bazata sa6u ba! Kaji na rantse ko? To wallahi ko sama da kasa zata hade sai Ummalkhairy ta fita ta toya min awarar nan, ubana ne kai? jimun mutum kai! Sai ji kake kamar kai ka haifeni tou bazai yuwu ba! Na rantse maka da Allah ko? Tou ka fita idona tun ban maka rashin mutunci ba!" Yayi murmushi "Turai kenan, yanzu ni ban isa in fada maki magana ba kiji? A matsayina na uban Ummalkhairy nace kar ta fita toya awara kince sai tayi? Wai baki tausayinta ne? Ki duba fa halin da take ciki?" Tayi shewa da dariya "Aiko ya zama tilas sai tayi shi nima a matsayina na uwarta na kuma isa da ita nace sai tayi!" Juyowa tayi ta jefi Khairy da wani irin mugun kallo wacce duk ta lalace ta rame anya ma babu wani abu dake damunta banda ciki? Raku6e take gefe sai kukan fitan rai takeyi "Zaki daina wannan kukan munafuncin ko kuwa? Bari kiji in fada maki wallahi ko jini zai ringa zubowa daga idanunki sai kinyi tuyar awarar nan a kofar gidannan ko uban wa ya tsaya maki kuwa! Wannan shine horonki da dauko mana abun kunya don ubanki!" Sautin kukanta ne ya karu, Baba ya sa kai ya fita yana girgiza kai, wata irin mangara ta kai mata har saida ta kife kasa sannan ta kai mata kwanya "Zaki matsa ki bani wuri ko sai na kara mauje ki? Wallahi tallahi ki kiyayeni! Shi kuma uban naki sarkin tausayi ko tausayin uban wa ga yar iska irinki! Daga kawai zaki nema ma kanki sana'ar kanki? Tou kisani rayuwarki fa ta riga ta sauya, uban wa zai dinga biya maki kudin antenatal? Dama fita kikayi daga gidannan kisan nayi ki fara hura wuta, ke dan ubanki inda kinada hankali yaci ace kina taimaka man bakida aiki sai shegen yawo, yanzu yar suyar awara ce don ance kiyi kika bi kika tada hankalinki toh wallahi tallahi sai kinyi shi!" Tana gama fadan haka ta ja uban tsaki ta wuce ciki ta bar Khairy na gunjin kuka.

Tafi minti talatin a zaune tana kukan fitar rai, can dai ta mike da kyar ta dauko kaskon suya dama ta riga ta hada awararta ta dauko ashana da komai da zata bukata da kujerar zaman kasa, tana fitowa mutane suka fara binta da kallo wasu harda nunata, toh wai a haka zatayi cinikin awarar ma mutane na gudunta? Nan da nan ta zauna ta fara hada wuta mai yayi zafi, tafi awa zaune ko kallon arziki babu wanda yayi mata balle ma ta sa ran za'a siya, babu mai siya in ba almajirai ba suma bata wuce ta biyar ta goma, har bayan Isha'i tana zaune a wurin gaba daya cinikin da tayi na naira dari biyu da ashiri kacal, ita tsoron shiga gida ma takeyi. Can wurin karfe tara dai tayi shahada ta mike ta soma kwashe kayan, a bisa verandar tsakar gida ta iske Mama ta aje kujera tana azkhar, har kasa ta tsuguna ta mika mata kudin "Mama ga cinikin yau..." warce kudin tayi kamar zata balla mata hannu ta dubi kudin shekeke, "Me nake gani haka? Dan ubanki tun safe dari biyu da ashirin kadai kikayi? Kai amma anyi yal banza!" Hawaye Khairy ta kuma sharewa "Mama ina laifin dari biyun? da ban kawo ko sisi bafa?" Wani irin gigitaccen mari Mama ta dauke ta dashi fuskar nan daure murtuk! "Ni kike fadawa haka dan ubanki? Tou wallahi gobe kikawo man kasa da dari biyar sai na lahira yafiki jin dadi dan ubanki shegiya! Tashi ki bace man da gani! Kuma ki shiga ki fito ki zo kiman wanke wanke gashi nan ya taru!" Tashi tayi jiki na rawa ta shiga ciki tana kuka, kan gadonta ta fada ta dinga rera kuka ta mugun gajiya aikin da Mama ke sata ko yar aiki ta aje bazata dinga sanya ta irinsa ba. Numfashinta har wani sarkewa yakeyi kuka take kamar ranta zai fito, ji take gaba daya rayuwar ta fitan mata daga kai, gaba daya ji take a duniya babu wanda ya kaita shiga kunci da tsananin damuwa..

Washe gari tun karfe goma Mama ta hankado ta waje ta zaune kan kujera, ta hada komai da komai na suyar awara gaba daya kallon da ake mata cikin unguwar nan bata sonshi gani suke kamar wata dodo ce ta fito, a hankali ta fara tuya awarar nan don tanaso ta gama taje asibiti yau ne ranar farko da zata fara ganin likitan dan cikinta yanzu watansa biyu harda wani abu, har karfe biyu ta samu da kyar tayi dari bakwai, haka nan ta tashi ta kwashe kayan Mama na tsakar gida tana jiranta tace "Ke zo nan dan ubanki! Nawa kikayi yau?" Jiki na kyarma ta mika ma Mama kudin "Naira dari bakwai." Wata irin kwanya Mama ta sakar mata akai, wani irin ihu ta kurma kwanyar ta kuma ratsa mata kai "Sa'ar ki daya asibiti zakije yau da sai naci ubanki cikin gidannan! Tashi muje!" Da sauri ta mike har tana hada hanya suka fito tare karshe Mama saidai ta tasa niqab don saboda yadda ake binsu da kallo cikin unguwa. Da kyar suka samu mai adaidaita suka tafi asibiti, da isar su suka biya kudi suka fiddo kati nan suka bi layi don itace ta hamsin da hudu (54). Nan suka fara bin layi basu aka kira su ba sai karfe biyar na yamma, a gajiya suka shiga dakin likitan, yana zaune sanye da farin glass ya basu izinin zama, suka gaishe shi ya bude file dinta yana murmushi yace "Ummalkhairy right?" Ta gyada kai yace "Ok." Kwanciya yace tayi ta bude cikin ya daddana sannan ya kunna scan machine yayi mata scan saida ya gama ya kalli Mama yace "Akwai general test din da zatayi zata kawo mana idan an gama." Nan ya rubuta masu suka tashi suka fita suka nufi Lab, ba bata lokaci duk aka gidanar da duka tests din aka kammala suka basu results, nan suka koma wajen Doctor, yana duba wasu yace su dan jirashi minti kadan, sai bayan kusan minti biyar yace su shiga, bude paper din yayi ya fara dubawa "Your sugar level is normal, Bp is normal, no malaria...." shiru yayi yana kallonsu Mama gabanta ya fadi yace "But there's something...." Mama ta dafe kirji "Doctor mey?" Ya numfasa "Zan iya ganin mijinta, don dole shima sai an gwada shi aga ko bai dauke da kwayoyin wannan cuta..." a razane Mama tace "Wai wace irin cuta ce Doctor dan Allah ka fada mana!" Numfasawa yayi cike da alhini yace "Wato ummalkhairy tana dauke da cutar hiv aids!" Ay wani irin salati Mama ta rafka ta fashe da matsanancin kuka, ita kuwa Khairy gaba daya duniyar juya mata ta dunga yi kwalwarta ta tsaya cak da aiki, kallon likitan take ba kakkautawa daga bisani ta fasa wata razananniyar kara kawai sai gani sukayi ta fadi tim kasa!

No comments: