Tuesday 14 March 2017

KHALEEL Page 51&52

🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀

           🎀🎀🎀🎀🎀🎀


🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀


Wannan page d'in naku ne members na HAUSA NOVELS na CHUCHU, RAFF and FATIMA MANSUR thanks for the love... Masu k'orafi bana typing da wuri suma suyi hak'uri kunsan Dan Adam ajizi ne bayan haka akwai hidimar da ta sha mana kai bako da yaushe muke samun time ba, a dinga yi mana uzuri please❣❣❣



©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               🎀🎀🎀🎀🎀
                  *KHALEEL*
               🎀🎀🎀🎀🎀


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 March 2017💎


              PAGE


✍🏻✍🏻51&52✍🏻✍🏻


Haka ya cigaba da tafiya yana k'wala mata kira amma shiru kakeji, k'ark'ashin wata bishiya ya zauna don ya huta, idanunsa suka sauka kan wani zobe na Diamond mai kyau sai shinning yake, d'auke zoben yayi yana jujjaya shi yana tuno ranar tun kafin suyi aure ya siyo ma Hanifah shi ranar ya gama karatunshi da zai dawo ya tsaya ya siyo mata, amma da k'yar ya samu ta sashi a hannunta cewa tayi bataso ashe har yanzu yana hannunta bata cire ba? Hakan ya tabbatar masa da cewar Hanifah na kusa da shi.
Murmushi yayi ya damk'e zoben gami da turawa cikin aljhun gaban rigarsa. Sai da ya d'an huta na kamar minti d'aya sannan ya mik'e ya soma tafiya yana kiran sunanta da k'arfi.
Haka yayi ta tafiya yana kiranta har rana ta kusa fad'uwa, wata irin yunwa yakeji marar misali, haka nan dai yake daurewa, da yayi nisa sai ya huta haka yakeyi.

Hanifah kuwa tafiya tayi tafiya, tun tana ganin biyu biyu har tazo ta fara ganin duhu, duniyar gaba d'aya juya mata takeyi, daga k'arshe ta zube nan ji kake tim!

*****

Gari har ya d'an fara yin duhu alamun magriba ta gabato, Khaleel ba inda bai bi ba, ko wace hanya ya hango sai ya bi kozai dace amma bai ganta ba, Khaleel ya rasa inda zai sa ransa yaji dad'i, ya kira Saif ba iyaka ko an dace amma amsa d'aya ce BA'A GANTA BA.
A gajiye ya soma tafiya inda ya ajiye motarsa don zai gwada wani wurin kuma tunda nan d'in bai ganta ba, sam yama fidda ransa da ganinsa a nan kusa shidai fatanshi Allah yasa tana raye kuma lafiya lau.

Daga nesa nesa ya dinga hango mutum kwance k'asa, da kamar ba zaije ba amma wata zuciyar tace masa yaje yaga ko menene, addu'a yayi ya doshi wurin gab da ita ya tsaya tare da lek'awa a razane yayi baya not believing what he saw, yama kasa k'wak'waran motsi, sai dai yayi gathering courage nasa tukunna ya matsa gabanta ya k'ara tabbatar da abinda idanunsa suka gane masa, tabbas ita d'in ce Hanifansa ce kwance! Farin ciki marar misaltuwa yaji, zubewa yayi bisa gwiwowinsa tare da jawota bisa cinyarsa, yana fad'in
"Hanifah! Tashi nine Khaleel, bud'e idonki ki ganni nine a kusa da ke"
Still ko motsi batayi ba, kallonta yakeyi a d'an tsorace yana fad'in
"Kar dai kin mutu Hanifah! No! Insha Allah baki mutu ba"
Yana fad'in haka yana shafa fuskanta cike da So da K'auna! Rungumeta yayi k'yam a jikinsa kamar za'a k'wace masa ita yana ta wasu surutai wanda bana gane meyake fad'i.
Daga k'arshe ya mik'e tsaye, cak! Ya d'auke ta kamar jaririya ya soma tafiya, tafiya yayi mai d'an nisa sannan ya iso inda motarsa take, bud'ewa yayi gami da bud'e bayan motar ya shimfid'e ta ya rufe, mazaunin driver ya zauna ya d'auko wayarsa ya kira Saif, bugu d'aya ya d'auka
"Ya Khaleel har yanzu baka dace ba? Ka hak'ura ka dawo gida in yaso na maka alk'awari gobe zan raka ka mu duba..."
"Saif na ganta!" Khaleel ya katse sa
Saif yace
"Me kace?"
Yace
"Na ganta Saif naga Hanifah yanzu"
Ya fad'a cike da farin ciki, Shima Saif cike da farin ciki yace
"Da gaske Ya Khaleel? A ina ka ganta? Bani ita muyi ma..."
"Hello Khaleel anga Aminatu wai?"
Cewar Ammi wadda ta k'wace wayar daga hannun Saif, k'walla yaji yana neman zubo masa yadda yaji muryar Ammi har rawa takeyi, daurewa yayi yace
"Na ganta Ammi, amma don Allah ki kwantar da hankali zan kawo miki ita gida kar ki tada hankalinki..."
"Bani ita Khaleel, bani inyi magana da ita shine kad'ai zan samu kwanciyar hankali"
Cewar Ammi
Khaleel yace
"Ammi ki kwantar da hankalinki tunda nace an ganta an ganta d'in, sai na kawo ta"
Daga haka ya kashe wayar gaba d'aya saboda yasan muddin bai kashe ba to zasu sake kiransa, tunda yanzu yasan babu ta yadda za'ayi suyi magana da Hanifah.
Tada motar yayi a hankali ya soma tafiya, yana tafe motsi kad'an zai lek'a yaga da gaske dai tana nan kuma bata tashi ba, a haka ya d'anyi tafiya mai nisa, wata asibiti ya hango daga bakin hanya ba 6ata lokaci yayi parking ya fito, bud'e baya yayi ya fito da Hanifah sannan yayi ciki da ita da sauri, k'aramar asibiti ce, wata nurse ya gani inda ya sanar da ita yana neman taimako, itama ba 6ata lokaci suka anshi Hanifah sukayi ciki da ita da sauri, Khaleel yaso shiga suka hana dole yaja ya tsaya.
Yana tsaye ya had'a tagumi wani doctor yazo ya wuce da nurse biye dashi a baya, duk yadda Khaleel yaso yayi magana dasu ya kasa, dole ya hak'ura ya zauna.

Bayan minti goma likitan ya fito inda Khaleel ke zaune, da sauri Khaleel ya mik'e ya fara tambayarsa ya Hanifah, doctor d'in yayi murmushi tare da ba Khaleel hannu suka gaisa, sannan yace masa
"Sunana Doctor Ahmad, na duba patient d'inka yanzu, well kar ka tada hankalinka she will be fine, kawai dai is like she is dehydrated ma'ana tana buk'atar alot of fluid a jikinta, banda wannan ma tana buk'atar abinci gaskiya is like tayi days ba abinci, so zan aje ta a nan for observation just drip d'aya ya isheta sai kayi k'ok'ari ka bata alot of fluid kamar su fruits da ruwa sosai, amma bayan nan babu wata matsala. So tana nan mun bata d'aki ga wannan"
Ya mik'a masa wata paper
"Magungunan da take buk'ata ne da drip d'in da za'a sa mata ka hanzarta ka kawo don a fara sa mata"
Khaleel ya maida numfashi
"Mun gode doctor amma yaushe kake ganin zata farka?"
Doctor Ahmad yayi murmushi
"I can't say gaskiya koda yaushe ma zata iya tashi ay she's alright, kai dai kawai ka tabbatar kana bata ruwa yadda ya kamata, and idan ta farka ta samu ta ci wani abu ko yaya ne"
Khaleel yace
"Insha Allah mun gode doctor"
Sukayi musabaha Khaleel ya wuce pharmacy ya siyo magungunan da ake buk'ata, sannan ya biya kud'in d'akin da aka kwantar da ita, luckily ma akwai y'an kud'ad'e a tare da shi da baisan yadda zaiyi ba.
Bayan nurse d'in ta jona mata drip d'in Khaleel ya tambaya ina ne masallaci, aka nuna masa kai tsaye can ya wuce yayi alwalla yayi sallolin da ake binsa ya dad'e yana addu'a.
Bayan ya fito zarcewa yayi ya nemo inda ake siyar da fruits, kankana ya siyo mata da lemo (orange) sai ayaba. A lokacin da ya koma k'arfe tara da kwata 9:15 PM.

Tura k'ofar d'akin yayi a hankali ya shiga, tana nan kwance yadda take bata motsa ba, ajiye kayan yayi cikin d'an k'aramin fridge d'in da ke d'akin sannan ya jawo wata kujerar roba da aka ajiye musamman saboda mai jinya, k'ura mata ido yayi kamar bai ta6a ganinta ba, kafin ya jawo hannunta ya rik'e cikin nasa gam, kayan jikinta tun wanda ta saka ranar da abin ya faru ne wata doguwar riga ta material sai hijabi kalar kayan.
Ya sauke ajiyar zuciya yana cigaba da kallonta, gashi ga Hanifanshi a kusa dashi, a hankali ya furta
"I missed you so much my baby"
Kwantar da kansa yayi gefen gadon still hannunsa cikin nata, ya jima a haka kafin bacci ya sace sa...




MSB✍🏼

No comments: