Friday 17 March 2017

KHALEEL Page 57&58

🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀

           🎀🎀🎀🎀🎀🎀


🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀


I dedicated this whole page to you Zainab Bapullo (Zee Bee) you are the best! Thanks alot much luv💖😘



©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               🎀🎀🎀🎀🎀
                  *KHALEEL*
               🎀🎀🎀🎀🎀


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 March 2017💎


              PAGE


✍🏻✍🏻57&58✍🏻✍🏻


Sai da sukayi sallar isha'i sannan suka soma shirin tafiya, a d'aki Ammi tayi ma Hanifah nasiha sosai game da zaman aure duk da ta fuskanci inda d'iyartata ta dosa, kuma dama abinda ta dad'e tana fata kenan. Ammi ta mik'e ta bud'e drawer ta d'auko wata bak'ar leda ta dawo ta zauna tana kallon Hanifah. Wata kwalba ta fiddo mai farin turare a ciki tace
"Kinga wad'annan turaren Humra ne, kullum da safe idan kinyi wanka kafin ki bushe ki tabbatar kin shafe jikinki da shi, haka ma da daddare kar ki bari sai jikinki ye bushe tukunna, idan kika shafa ko wane lungu na jikinki sai ki bari ya bushe, zakiga a hankali zai kama miki jikinki koda yaushe kina k'amshi, sai ki shafa wannan man"
Ta fiddo y'ar kwalba mai fad'i, tana bud'ewa k'amshi mai dad'i ke tashi tace
"Mai ne na shafawa da akayi masa had'i na musamman da turaruka masu dad'i ya kasance shine man shafawanki, ga wannan kuma"
Ta fiddo doguwar kwalba tace
"Wannan a cikin ruwan wankanki zaki dinga d'igawa sai kiyi wanka dashi, idan sun k'are kiyi magana zansa a had'o miki da yawa"
Hanifah tunda Ammi ta fara kanta ke k'asa ta kasa d'agowa. Ammi tayi murmushi tace
"Magana ta k'arshe da zan fad'a miki shine ki rik'e mijinki Amina, ki kama shi duk wata kunya ki cire ta ki aje a gefe, ba'a ce kar ki nuna kunya ba a'a amma dai don ki faranta masa sai kin cire ta, wallahi Hanifah kafin ki samu mai sonki tsakani da Allah kamar Khaleel sai an tona, sheyasa tun tuni naso ki fahimta kika kasa, amma yanzu tunda kin gane to alhamdulillah, idan akwai wata matsala kiyi k'ok'ari ki sanar dani kinji ko? Ki tashi kuyi harama dare nayi Allah ya k'ara tsare ku ya baku zaman lafiya kinji ko?"
Hanifah ta gyad'a kai k'walla taf idonta, da k'yar ta maida su tace
"Nagode Ammi insha Allah zanyi amfani da shawarar da kika bani"
Ammi tace
"Bakomai Amina tashi ku tafi Allah yayi muku albarka kinji?"
Da k'yar tace "Amin" ta kwashi kayan da Ammi ta had'o mata tare da gyalenta ta fito.

A palo ta iske Khaleel da Saif na fira, suna ganin ta fito a shirye suka mik'e, Khaleel ya kalli Saif yace
"Ina zuwa bari nayi sallama da Ammi"
Suka ce "To"
Ba'a jima ba ya fito suka d'unguma waje, a bakin mota ma sun dad'e tsaye shida Saif suna fira sannan sukayi sallama.
Saif na tsaye Khaleel yaja motar ya bar gidan yana d'aga musu hannu.
Kafin suje gida sai da ya tsaya ya siya musu classy burger da ice cream, sai gassassar kaza.

A bakin gate Baba mai gadi ya tsaya yi musu murnar dawowa lafiya, sun jima suna fira saboda dama Baba mutuminsa ne, yakan fita haka nan ma suyi ta fira sannan ya shigo gida.
Bayan yayi parking ya fito da kanshi ya zagaya ya bud'e ma Hanifah ya jawo hannunta suka shiga cikin gida. Suna shiga parlor Khaleel yace
"Welcome home Hanifah.... Home sweet home"
Tayi murmushi tace
"Thanks dear"
Hannunta ya kama suka shige d'aki, sai da suka fara cika cikinsu sannan Hanifah ta tattara wurin ta kai kitchen, sanda ta dawo taji Khaleel na toilet alamun wanka yakeyi, itama d'akinta ta zarce, ta cire kayan jikinta ta d'aura towel, turaren wankan da Ammi ta bata ta fiddo tayi yanda tace sannan ta shiga wankanta, nan ma ta jima kafin ta kammala, duk turarukan da Ammi ta bata tayi amfani dasu, ta gyara gashinta ta tufke shi daga can tsakiyar kanta, sai k'amshi yake zubawa.
Wata rigar bacci ta d'auko ash color, y'ar ciki ce marar hannu iya gwiwa, mai sul6i sai ta saman wadda ita tanada mad'auri, bayan ta gama ta bi jikinta ta turaruka masu matuk'ar dad'i, kallon kanta take ta cikin madubi tana ajiyar zuciya.
Wayarta ce ta fara ruri, tun kafin ta d'auka ta san mai kiran saboda ringtone d'in da aka sa masa na daban ne, murmushi tayi ta d'auka.
"Hello.." Tace a sanyaye
Khaleel ya sauke ajiyar zuciya
"Har kin gama kimtsawa?"
Tace
"Eh"
Yace
"Ok ki zo ina son ganinki"
Tace
"Toh"
Bayan sun gama wayar tayi tsai kamar mai tunani, karo na farko da taji tana jin kunyar Khaleel, can kuma ta tuna maganganun Ammi suna mata yawo akai, batasan lokacin da ta fito daga d'akinta ba ta doshi d'akinsa. Tura k'ofar tayi a hankali had'e da sallama, jin shiru ya sanya ta shigewa ciki ta fara dube dube, ba zato taji an chafko ta daga baya, a tsorace ta juyo ganisa ya sanya ta ajiyar zuciya, kallonta yakeyi cikin ido itama haka, basu san adadin lokacin da suka d'auka a haka ba kafin Hanifah ta sauke idonta k'asa tare da juya masa baya dafe da k'irji, lumshe idanunta tayi tana jin wani abu yana ratsa dukkanin illahirin jikinta da jijiyoyinta, shima kansa Khaleel d'in yanayin da yake ciki baya misaltuwa, da k'yar yace
"Muje muyi sallah"
Tace
"Ay nayi isha'i"
Ya kamo hannunta ta baya ya juyo da ita tana kallonsa, yace
"Nasan kinyi amma zamu k'ara wata"
Ta sunkuyar da kanta sarai ta gane abinda yake nufi yanzu.
Ba 6ata lokaci sukayi alwalla sukayi sallah raka'a biyu bisa koyawar manzo (S.A.W) dafe goshinta yayi yayi ta jero mata addu'a ba iyaka sannan kuma yayi mata tambayoyi kan addini, nan ma ta amsa daidai kuma yaji dad'in hakan.
Kan gado ya baje yana kallonta da har yanzu tana zaune kan abin sallah yace
"Zo kiyi min tausa"
Tayi murmushi, ya d'aga mata gira d'aya yana murmushi, hannuwanta duka biyun tasa ta rufe fuskarta tana murmushi sannan ta taso jiki ba k'wai ta haye gadon. Ya kalleta da mamaki yace
"Malama wannan hijabin fa?"
Tace
"Da ita zan kwana"
Yace
"Kinyi kad'an yarinya dama ki cire ta"
Ta mak'e kafad'a a shagwa6e tace
"Ni a'a da ita zan kwana"
Hannu yasa zai cire mata hijibin ta rik'e ta gam tana dariya, aikuwa suka fara kokowa shi yana k'ok'arin cire mata ita kuma tana hanawa. Cikin kokowar ya janyota ta fad'o masa fuskarsu gab da juna har suna jin bugun numfashin junansu. Da wayau da dabara ya cire mata hijabin sannan ya jawo bargo ya rufe musu har kai tare da kashe fitila.


Asuba ta gari amarsu ta ango.... ****


Asubar fari Khaleel ya fara tashi ya kalli Hanifah dake kwance bisa fad'ad'an k'irjinsa tana bacci, shafar fuskarta yayi tare da janyeta a hankali don kar ya tashe ta, toilet ya fad'a yayi wanka had'e da alwalla, sannan ya cika kwami da ruwa masu zafi, cak ya d'aga ta tana bacci kamar jaririya ya dire ta cikin ruwan zafin nan, zogi da azaba ya sata wani irin ihu, lalla6a ta yayi kamar k'wai har ta gama gasa jikinta, tayi wanka tayi alwalla ta fito. Masallaci ya wuce a yayinda Hanifah ta fara sallarta, har gari ya d'anyi haske sannan ta linke abin sallar ta hau gado, ba'a jima ba bacci yayi awon gaba da ita.


Ba ita ta farka ba sai k'arfe kusan sha d'aya, kwance ta ganta bisa k'irjin Khaleel ya zagaye hannunsa ya rik'e ta gam, janye jikinta ta fara k'ok'arin yi amma ta kasa, fuskarsa take kallo ta ga da gaske bacci yake hankali kwance, sai kuma taji ta kasa daina kallonsa, wani sabon sonsa ke k'ara ratsa ta, ta jima tana kallonsa wanda batasan adadin lokacin data d'auka ba, firgit ta dawo daga duniyar tunani ta fara k'ok'ari d'auke hannunsa daya rik'e ta dashi.
"Idan ma tunanin tashi kike to ki daina"
A shagwa6e tace
"Don Allah ya Khaleei ka sake ni girki fa zan d'ora har rana ta fara fitowa"
Yayi murmushi still idanunsa a rufe
"Bafa inda zakije, ki koma ki kwanta kiyi bacci ki huta"
Zata k'ara magana taji ya k'ara matse ta dole tayi shiru ta rufe idonta.
Haka masoyan sukayi kwance har kusan azahar, sai da Khaleel yaji an fara kiraye kiraye sannan ya mik'e da sauri, wanka ya fara yi tukunna yayi alwalla, kafin ya wuce sai da ya tashi Hanifah itama don tayi tata sallar.


Wanka tayi, tayi sallah, ta gyara gidan tas kamar yadda ta saba. Bayan ta gama ta shirya cikin riga da skirt na english wears black skirt sai light pink top, turare kuwa kamar tayi 6arinsu, pink k'armin veil ta d'aura d'aurin ya mata kyau sosai, wasu y'an kunne masu tsawo kad'an suma pink tasa, lipstick ma pink aka sa, tadai yi kyau ba kad'an ba.
A bakin k'ofar kitchen taji an rungumo ta ta baya.
"Mey kike tunanin zakiyi?"
Tace
"Girki zan d'ora"
Ya juyo da ita suna kallon juna yace
"Ki aje maganar girki tukunna sai kin warke tas"
Tayi murmushi
"Ni na warke fa"
Yaja karan hancinta yace tare da kwaikwayon maganarta
"Ni ban yarda bafa"
Sukayi dariya gaba d'aya. Hannunta ya kamo yace
"Muje na siyo mana abinci muci"
A tare suka jera har kan dinning d'in, yau shi yayi serving d'insu, nan ma feeding juna sukeyi har suka kammala.



MSB✍🏼

No comments: