Wednesday 29 March 2017

KHALEEL Page 69&70

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 March 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻69&70✍🏻✍🏻


A hankali yake taku har ya tako inda take, ganin yadda ta cika tayi fam ya sanya ya kamo ta tsam a jikinsa.
"Dan Allah calm down my princess, kinsan yanzu bake kad'ai bace ki daina tada hankalinki a banza, bana son wani abu ya ta6a mana babynmu"
Ta ture sa iya k'arfinta cikin tsawa tace
"Hankalina bazai kwanta ba har sai ka sanar dani daga ina kake?"
Cikin kwantar da murya ya soma magana
"Kinsan nace miki oga ya kiramu ay ko?"
Ta girgiza kanta alamun eh ya cigaba
"Bayan mun gama sai abokin aikinmu ya kad'e wani yaro a sanadiyar haka muka taimaka masa aka wuce dashi asibiti mun d'an juma a can, sh....sheyasa kika ga nayi dare haka, amma ki cire duk wani mugun tunani a ranki my dear bazan ta6a cin amanar ki ba, you know i love you from the bottom of my heart right?" Ya k'arasa yana shafa mata gefen fuska yana murmushi, kallonsa take kamar bata sanshi ba, irin kallon nan na tuhuma, yace
"Baki yarda dani ba ko?"
Tace
"Bawai ban yarda da kai ba ya Khaleel, yadda ka chanza ne dole idan kayi wannan daren hankalina ya tashi, nafiso idan har wurin wata kake zuwa ka daina 6oye min, ka fito fili ka sanar dani zai fi min sauk'i"
Yace
"Haba Hanifah! KI YARDA DANI mana, maganar dana fad'a miki haka d'inne ya faru"
Ta share hawayenta
"Shikenan na yarda Allah yasa haka d'inne" yace
"Haka ma ne my princess kinji?"
Daga k'arshe dole ta yarda ganin yadda yake kwantar da murya yayi kalar tausayi, tsakanin mata da miji kuma sai Allah take ta mance komai.
A daren ranar sunyi kwanan farin ciki inda Khaleel ya nuna mata tsantsan kulawa marar misaltuwa!


******

Abubuwa sun d'an daidaita tsakaninsu sai dai Khaleel na yawan behaving somehow kamar marar gaskiya misali idan yana waya ta shigo zaiyi saurin katsewa, dah da farko takan tuhume shi sai yace mata Wallahi ba wani abu bane, kawai k'ila sanda take shigowa ya gama wayar ne.  Kallonshi kawai take tana k'yaleshi don bata son tashin hankali ya kuma had'a su, amma deep inside her tana zargin wani abu, dan dai ance zato zunubi koda ya kasance gaskiya sheyasa sai ta daina kawo tunanin komai a ranta yanzu, sai dai damuwar data shiga ba y'ar kad'an bace, amma kuma damuwarta ta ragu don yanzu rayuwarsu ta dawo kamar dah yana bata kulawa fiye da dah ma, itama yanzu ta k'ara himma wajen ganin ta dawo da mijinta na dah.

*****

Wata rana da safe bayan sun tashi daga bacci Hanifah duk aikin da ya kamata tayi ta gama, ta taimaka ma Khaleel ya shirya kamar kullum sukayi breakfast, nan ma kafin ya tafi office sai da ya nuna mata yadda zaiyi missing d'inta itama haka, hakan da yake ba k'aramin dad'i takeji ba zuciyarta fes haka takeji yanzu.
Yana isa office ko minti biyu baiyi da fara aikinsa ba aka shiga knocking, ya d'an dakatar da abinda yakeyi yace
"Come in"
Masingansa ne ya shigo mai suna Garba, rissanawa yayi alamun girmamawa yace
"Ina kwana y'alla6ai?"
Da murmushi a fuskansa yace
"Ah Malam Garba an tashi lafiya?"
Yace
"Lafiya lau"
Khaleel yace
"Yadai?"
Yace
"Kanada bak'uwa a waje, amma ban riga nace mata kana nan ba, nadai ce mata ta jira na dubo"
Khaleel yana ma Garba wani kallo yace
"Wacece?"
Garba yace
"Wallahi bansanta ba, amma daga gani dai budurwa ce tadai ce tana son ganinka da gaggawa"
Khaleel yace
"Ok ka shigo da ita"
Da girmamawa yace
"To" sannan ya fice. Can sai gashi ya dawo tare da ita bayan fitar Garban ne da mamaki Khaleel yace
"Humaira! Mekike yi a office d'ina yau kuma?"
Tana tsaye tace
"Haba yayah! Bazaka bani izinin zama ba tukunna ba?"
Ya dafe kai yace
"Ohh i'm sorry please, zauna bismillah"
Ta zauna sannan tace
"Ina kwana?"
Yace
"Lafiya lau ya karatu?"
Tace
"Alhamdulillah"
Yace
"Meke tafe da ke?"
Tayi murmushi tace
"Dan Allah dama so nake ka ranta min kud'i zanyi wasu hidima ne hannuna ba kud'i, gashi ba'a aiko min saboda account d'ina ya samu matsala sai anjima zanje bank d'in na gyara" tana magana tana wani sunna kai alamun kunya tana kashe murya.
Ya sauke ajiyar zuciya
"Har nawa kike buk'ata ne?"
Tace
"Ko dubu 30 ma ya isa"
Da mamaki yace
"Mezakiyi da dubu 30?"
Ta sunna kai k'asa tace
"Gaba d'aya kayan abinci na sun k'are shine zan siya"
Yace
"Ok kizo gida idan na koma anjima, ko kuma ki bari zan ba Hanifah ta baki ay kuna had'uwa kullum"
Sam ba haka taso ba amma dole tabi a hankali kar yayi saurin gano ta, dan haka sai tace
"Ba damuwa nagode sosai Allah ya saka da alkhairi"
Yace
"Bakomai Amin"
Ta mik'e tana wani yanga tace
"Zan koma sai anjima"
Yace
"Sai anjima"
Sai da fito waje ta soma fitar da hucin bak'in ciki, lallai ma Khaleel ya raina mata wayau yanzu har sai yaba wannan shegiyar matar tasa kud'i ta bata kenan? Lallai da sake dole ta zage damtse idan ba haka ba bazata cimma burinta ba. Da wannan tunanin ta tari Napep ta koma hostel.

Da yamma bayan ya koma gida Hanifah ta taro sa kamar kullum, yayi wanka ta taimaka masa ya shirya suka nufi dinning, suna cikin cin abincin ne yace
"Yau k'awarki tazo office d'ina"
Da mamaki tace
"Wace k'awar tawa?"
Yace
"Kina da k'awa sama da Humaira ne?"
Ta d'aure fuska tace
"Oh hakane, me taje yi maka?"
Yace
"Wai kud'i zan ranta mata...."
Ya bata labarin abinda zatayi dashi, "So nace zan baki ki kai mata idan kun had'u school"
Sai a nan taji sanyi tace
"Ok ba damuwa"

Haka kuwa akayi ranar da Hanifah ta shirya zata school, ya bata kud'in ta kai mata. Tana isa school d'in ta kira Humairar bugu biyu ta d'auka Humaira ta soma magana
"Hanifah ya kike?"
Tace
"Lafiya lau kina ina ne?"
Tace
"Gani nan yanzu na fito daga hostel, kina ina?"
Tace
"Gani nan inda nake parking cikin motata, ki k'araso ina jiranki"
Tace
"Ok gani nan zuwa yanzu insha Allah"
Hanifah tace
"Ok toh"
Suka katse wayar. Bayan minti goma sai ga Humaira ta iso tana zuwa ta bud'e motar ta shiga tana murmushi tace
"Maman d'an baba ya baki fito daga motar ba?"
Hanifah tace
"Wallahi wai dama ke nake jira sai muje tare"
Humaira tace
"Allah sarki ya kike ya babynmu?"
Hanifah tace
"Lafiya lau, ga wannan ma" ta k'arasa tana zage zip d'in jakar ta sannan finally ta fito da wata brown envelope ta mik'a mata
"Ga sak'on ki"
Humaira fa fad'ad'a murmushinta
"Kai nagode sosai, please ki taya ni godiya"
Hanifah tace
"Haba ba komai"
Daga nan suka fito daga motar suka je suka had'o duka handouts d'in da basu dashi, suka kar6i exam card har signing an musu, don next week zasu fara exam.



*******

Tafi kwana biyu tana had'a plan yadda zata jawo ra'ayin Khaleel gareta inda finally tayi coming up with a great idea, bayan dogon bincike ta gano lokacin da yake fita.
Ranar da ta shirya ta fito bakin titin da yake bi idan zaije office, inda ta dad'e tsaye tafi minti talatin kafin finally ta hango motanshi, sai data daidaici ya iso inda take sannan tazo yin crossing road d'in wani burki ya taka ji kake k'uuuuiii! Amma still ba zato sai da ya bige ta, ta fad'i rigib k'asa. Da sauri ya fito daga motar inda ya k'araso a rud'e, tana kwance k'asa rigib tana ihun k'arya, kamar ance d'ago kanki kawai suka had'a ido, muninsa kad'ai ya isa ya bada tsoro take ta kurma ihu, tana k'ok'arin tashi tsaye, tace
"Waye kai?"
Yace
"Kiyi hak'uri na kad'e ki ba da sanina ba kuma ma ay laifinki ne meyasa kika taho kina ganina?"
Yadda takejin haushi ya sanya ta fara masifa
"Da Allah Malam ni bansanka ba kuma ka daina yi min wasu maganganu wanda bana gane makake cewa, ka tafi kawai"
Yace
"Amma ba inda kika ji ciwo ko?"
Ta k'ara kurma uban ihu
"Nace ka tafi haba!"
Tana gama fad'in haka ta ruga a guje tayi hostel tana zuwa ta fad'a bisa katifarta tana hak'i. Room mate d'inta mai suna Rufaida da ke sauke indomie daga wuta ta juyo tana kallonta tace
"Ke Humaira lafiyan ki zaki shigo babu sallama? Sannan zaki shigo a guje kamar an biyo ki?"
Humaira ta galla mata harara tace
"Sa idawa ko ina ruwanki dani kuma?"
Rufaida ta ta6e baki tace
"Meyayi zafi haka? Allah ya baki hak'uri" daga nan bata k'ara magana ba ta cigaba da abinda takeyi. Humaira ta tashi zaune ranta a jagule, abin haushi abin takaici wai duk wannan fad'uwar da tayi ta tashi a banza kenan? Ga rashin nasara ga fad'uwa k'asa, k'asan ma akan titi. Sai kawai taja wani dogon tsaki
"Mtssss" Rufaida ta juyo ta kalleta amma bata tanka ba. Tana kallonta ta tashi a fusace kuma ta fice daga d'akin.
Rufaida tace a fili
"Y'ar wahala ta maida ni banza kamar bansan me take shukawa ba, Allah sarki baiwar Allah Hanifah ta d'auketa mutuniyar arzik'i ashe ashe, sheyasa ma yin k'awa a wannan zamanin sai a hankali, nikam inaga gaskiya wata rana sai na same ta na fad'a mata abinda Humaira ke mata, don bazan zuba ido ina ganin ana cusa wa y'ar mutane bak'in ciki jna gani ba, Hanifah muna mutunci sosai don haka zan same ta kawai na fad'a mata gaskiya dama tun farko kafin abin yafi k'arfinta ta d'auki mataki"
Da wannan tunanin a ranta ta k'arasa cin indomie d'inta.


*******

Ranar da sukayi first paper d'insu bayan sun fito ne Humaira tace ma Hanifah
"Yau gidanki zanje kuwa"
Hanifah tace
"Kinsan kuwa nima daga nan ba gida nayi ba, zan biya gidanmu ne sannan na wuce gida"
Humaira ta ta6e baki tace
"Ok sai yaushe kike gida?"
Hanifah tace
"Ranar da bamuda paper mana"
Humaira tace
"Shikenan dan Allah kinga ke kinfi iya wannan course d'in don in samu ki koya min ne"
Hanifah tace
"Ok ba damuwa zuwa jibi sai kizo"
Humaira tayi murmushin da ita kad'ai tasan ma'anarshi sannan sukayi bankwana, Hanifah ta shige motarta Humaira kuwa ta wuce hostel.

A gida ta iske Ammi tana garden da alama yau iska take sha. Hanifah ta k'arasa da sauri ta rungumota ta baya tace
"Ammi!"
Da sauri Ammi ta juyo baki bud'e tace
"Lallai Amina bakida hankali, wai har yanzu baki hankali ba ko?"
Hanifah ta zagayo ta zauna gefenta tana murmushi tace
"A gabanki ay bana girma Ammi"
Ammi tace
"Zaki girma ne wata rana"
Hanifah tayi dariya
"Ammi ina kwana?"
Ammi tace
"Lafiya lau daga ina kike?"
Hanifah tace
"Makaranta exam mukayi"
Ammi tace
"Au har kun fara kenan?"
Hanifah tace
"Yau muka fara"
Ammi tace
"To ubangiji Allah ya bada sa'a"
Tayi murmushin jin dad'i tace
"Amin Ammi, akwai abinci don yunwa nakeji"
Ammi tayi dariya
"Hala bakiyi kalaci ba kika kama hanyar makaranta?"
Hanifah tace
"Eh banyi ba yau tun 7 da rabi na bar gida saboda k'arfe 8 muke da paper d'in"
Ammi tace
"Lallai ina d'ana?"
Hanifah ta turo baki
"D'anki kuma nifa?"
Ammi tace
"Ohon maki ni Khaleel kawai na sani, da ki tsaya kina surutu kije ki nemi abinda zaki ci, bai kamata kina zama da yunwa ba a wannan yanayin"
Hanifah tace "To"
Ta tashi da sauri tayi ciki, Ammi ta bud'e baki galala tana kallonta fad'i take
"Ki dai bi a hankali kar kije ki 6arar da cikin, ina amfanin rashin nutsuwa?"
Tana juyo dariyarta daga bakin k'ofa tana fad'in
"Kai Ammi"



MSB✍🏼

No comments: