Monday 27 March 2017

KHALEEL Page 65&66

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 March 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻65&66✍🏻✍🏻

Yau da gobe sai Allah duk da Hanifah batada niyyar yin k'awa ko d'aya amma a department d'insu ta had'u da wata Humaira, budurwa ce y'ar kimanin shekara sha tara, dalilin da yasa Hanifah ta bata fuska taga kamar yarinyan nada mutunci ko ta yanayin shigarta saboda kullum cikin k'atuwar hijabi take, gashi ba ruwanta da kowa ita kad'ai take rayuwa, ganin haka ya sanya Hanifah ta amince da ita har suka k'ulla k'awance.
Haka rayuwar ke gudana, a kwana a tashi ba wuya wurin Ubangiji yau cikin Hanifah har ya tasan ma wata hud'u, Idan har kayi mata kallon sosai zaka fuskanci cewar cikinta ya d'an 6ullo kad'an.


Ranar wata juma'a tafiya ta kama Khaleel zuwa kano duk dai tafiyar daga office d'insu ne bama shi kad'ai zaije ba harda abokan aikinsa su biyu, tun da yake wayar Hanifah dake kwance gefensa ke masa wani irin kallo har ta kai ya tsargu, sai da ya gama wayar ne ya juyo yana kallonta yace
"Yada kallo haka my princess?"
Ta 6ata rai had'e da zum6uro pink lips nata masu k'ara mata kyau tace cikin shagwa6a
"Ina zakaje?"
Yayi murmushi yace
"Wallahi tafiya ce ta kama mu yau d'in nan amma kar ki damu kwana biyu kawai zamuyi mu dawo"
Ta juyar da kanta gefe alamun fushi, yayi murmushi tare da kamo ta ya maido bisa jikinsa yace
"Fushi kuma princess? Meyafaru?"
Idanunta suka kawo ruwa tace
"Naji kana zancen tafiya ka barni, kuma kai kanka kasan tun da muka daidaita baka ta6a tafiya daidai da rana d'aya ba, sannan kasan ban iya bacci idan baka kusa dani"
Yaji ba dad'i saboda shima d'in ba iyawan zaiyi ba sai dai yazama dole ya tafi saboda aiki ne zai kaishi don haka sai ya rungume ta tare da fara aika mata da sak'konin kisses ta ko ina, itama ta biye masa sun d'auki lokaci a haka kafin Khaleel ya sauke ajiyar zuciya yace
"My princess wallahi inda kinsan dauriyar da zanyi muje mu dawo da bakiyi ma  magana ba, wallahi zanyi missing d'inki sosai, kiyi hak'uri kar kice zakiyi kuka don bazan iya jure jin kukanki ba, i love you so much kwana biyu kawai zamuyi mu dawo insha Allah kinji my baby?"
Ta k'ank'ame shi tace
"I love you more my only, insha Allah zanyi manage har ka dawo amma kasani zanyi kewarka sosai"
Yace
"Yes i know my princess nima haka"


Daga nan Hanifah ta tashi ta had'a masa had'ad'en breakfast, ta shirya masa kayansa kafin ya fito wanka had'e da fiddo masa kayan da zai sanya. Tana gamawa itama tayi wanka tasa wata farar loose top marar hannu da red dogon skin tight sai ta d'aura red d'an kwali, ta kimtsa ta fito.
D'akin Khaleel ta lek'a a lokacin yana shafa mai, ganinta yasa ya saki murmushi ta mayar masa, k'arasawa tayi ta taimaka masa ya shirya suka nufi dinning suka karya. Tunda suka fara ci Hanifah ke kallonsa kamar zata cinyesa, ya kalleta yace
"My princess"
Ta sadda kanta k'asa tana murmushi tace
"Na'am my only"
Yace
"Na gama sai tafiya yanzu kuma"
Sai kuma ta 6ata rai duniya ba abinda ta tsana taji zatayi nisa da Khaleel d'inta, yana lura da yanayinta amma sai yayi sauri yace
"Da yaushe da yaushe kike lectures ne?"
Tace
"Sai monday amma gobe inada test k'arfe tara"
Yace
"Ok ga wannan"
Ya mik'a mata kud'i duba goma y'an d'ari biyar biyar yace
"Ki rik'e wannan abinda kike 6ukata kiyi yi amfani dasu har Allah yayi mana dawowa"
Tana dai ta daurewa bataso tayi kuka amma abu yaci tura sai kawai tasa kuka, take hankalin Khaleel ya tashi ya rud'e, hugging nata yayi yana ta aikin lallashi tare da assuring nata cewa kwana biyun zaiyi ya dawo and duk abinda take buk'ata ya aje mata, sai da ya tabbatar ta bar kukan sannan ya tafi.
Bayan tafiyan Khaleel gidan gaba d'aya ya mata fad'i ba dad'i sam, yau batasan ya zatayi bacci ba babu Khaleel a kusa da ita.
Haka ta wuni daga kallo sai karatun test, idan ta gaji ta buga candy crush a wayanta.
Tunda ya isa ya kira ta ya sanar sun isa lfy,


Da daddare Khaleel ya kirata da murmushi
shimfid'e saman fiskokinsu. Hanifah tace
"My only!"
Yace
"My princess! Ya kike?"
Tace
"Lafiya lau ya gajiya?"
Yace
"Akwai ta kam, kinga da ina nan da yanzu kin min tausa, gaskiya Hanifah i missed you so much, yanzu baki kusa da ni, komai ni ke wa kaina, kin riga kin shagwa6a ni"
Yanajin saukar ajiyar zuciyarta, tace
"Nima haka my only gani nan sai tunaninka nake"
Dad'i ya kama shi sosai
Yace
"I love you so much dear, nima ay tunaninki nakeyi"
Suka cigaba da firar soyayya tare da bayyana wa junansu yadda sukayi missing juna. A daren ranar haka suka dad'e suna waya kafin daga k'arshe suyi sallama. Haka ta kwanta lamo tana tunane tunane da k'yar ta samu bacci 6arawo ya sace ta


Washe gari bayan ta gama abinda take tayi wanka ta tafi school, a bakin class ta had'u da Humaira tana karatu, suka gaisa sannan suka d'an ta6a fira kafin su shiga test d'in.
Bayan sun fito cafeteria suka wuce suka ci abinci sannan suka soma yin bankwana inda Humaira ta buk'aci taje gidan Hanifah don Hanifah ta sanar mata yau mijinta baya nan she's lonely. A haka suka wuce gidan Hanifah.
Suna shiga Humaira ta soma yaba gidan first abinda tace shine
"Wow Hanifah gidanki yayi kyau"
Hanifah tayi murmushi kurum batace komai ba, kujera ta bata izinin zama inda Hanifah ta wuce kitchen ta d'auko mata lemo da ruwa.
Bayan sallar la'asar ta soma shirin tafiya.
Hanifah ta mata godiya kuma taji dad'i sosai.
Haka Hanifah ta idasa kwananta d'aya ba Khaleel amma kullum suna nan mak'ale da juna a waya sam basa gajiya da junansu.


*******


Ranar da Khaleel zai dawo murna a wurin Hanifah ba'a magana kwana biyu kacal ji take kamar ta shekara biyu bata gansa ba, shima Khaleel a nasa 6angaren yayi kewarta fiye da tunaninta.
Tun safe Hanifah ta tashi ta soma gyara gidan tas ta kimtsa ko ina. Ta girka masa Farar taliyar da ta sa  karas sai ta yi ta minced meat, tayi masa kunun gyad'a da zo6o, ta kimtsa komai kan dinning. Tayi wanka ta shirya cikin wani matsiyacin material d'inkin fitted gown wanda ya mugun fito mata da surar jikinta, ta feshe jikinta da turare, tana gamawa wayarta ta fara ruri da sauri ta d'auka
"Hello my only"
Yayi murmushi
"My princess ya kike?"
Tace
"Lafiya lau ya hanya har kun iso ne?"
Yace
"My princess bansan ta ina zan fara ba, bamu samu tahowa ba sai jibi wai"
Tayi kasak'e tana sauraronsa, zuciyarta na harbawa ya zaiyi mata haka? Ta gama sa rai sannan yace wai sai jibi? Take ta kashe wayar ta wurgar da ita kan gado tana huci, a yayinda hawaye suka fara kwarara daga idanunta. Ta dad'e zaune k'asa tana kuka yau Khaleel ya 6ata mata rai sosai.
K'wank'wasa k'ofa aka soma yi, da k'yar ta tashi tana share hawaye ta fice wurin k'ofa, tana bud'ewa to her biggest surprise ever Khaleel ne tsaye bakin k'ofa yana dariya, ta had'e rai
"Dama wasa kake min shine kace bazaka dawo ba?"
Yace
"Yes my princess i want to surprise you ne, baza'a bani hug ba?"
Dad'i ya mantar da ita fushinta take tayi saurin basa a big hug tana dariya, a haka yayi ta tsokanarta tana dariya. Ciki suka shiga inda ta had'a masa ruwan wanka ta fiddo masa kayan da zaisa. Bayan ta taimaka masa ya gama shirinsa sai taja hannunsa kan dinning ta zuba masa abinci. Bayan sun gama yace
"I miss you my baby"
Kafin tayi magana ya d'aga ta cak kamar baby yayi d'aki da ita tare da direta kan gado tana ta faman k'yalk'yaltar dariya, a haka ni kuma na basu privacy.



MSB✍🏼

No comments: