Monday 20 March 2017

KHALEEL Page 59&60

🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀

           🎀🎀🎀🎀🎀🎀


🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀


Ya Allah! I am so blessed to have sisters/friends like you, thank you all Ameemah is feeling so much better and it's because of your du'a! Alhamdulillah ala kulli halin jazakallah khairan❤️❤️❤️❤️


©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               🎀🎀🎀🎀🎀
                  *KHALEEL*
               🎀🎀🎀🎀🎀


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 March 2017💎


              PAGE


✍🏻✍🏻59&60✍🏻✍🏻


Bayan sallar magriba Khaleel da Hanifah na zaune suna kallon wani movie suna fira jefi jefi, Khaleel ya kalleta yace
"Wai nikam Hanifah dama kina so kuwa?"
Da mamaki take kallonsa tace
"Wannan wace irin tambaya ce haka?"
Yayi murmushi yace
"Kawai, da nasan kin tsane ni ta yaya kika fara sona?"
Ta nok'e kai cike kunya, ya gimtse dariyarsa yace cike da zolaya
"Ay duk wannan mayen kallon da kike min ina sane da shi, k'yale ki kawai nayi"
Rufe fuskarta tayi cike da kunya tace
"Uhm"
Yace
"Allah kina son y'an mata?"
Tayi murmushi, yace
"Baki bani amsa ta ba" nan ma shiru tayi yace
"Shikenan idan har baki ce da bakinki ba nasan ba sona kike ba"
Tayi murmushi, yace
"Wai sai murmushi kike malama kiyi magana"
Ta nok'e kai tace
"Allah ina..."
Yace
"Kina mene?"
Tace
"Ina sonka mana"
Dad'i yaji marar misaltuwa ya jawo ta ta fad'o bisa k'irjinsa yace
"Thank you my baby, I love you even more"
Tayi murmushi tace
"Na tambayeka wani abu?"
Yace
"Ina jinki"
Sai kuma tayi shiru, ya jawo hancinta yace
"Fad'i abinda ke ranki ni mijinki ne, you are free to say what ever is in your mind, don't hesitate"
Tace
"Dama... Dama so nake na tambayeka dalilin da yasa kake min wulak'anci kwanakin baya"
Yayi murmushi yana shafa gashinta dake baje bisa bayanta sai k'amshi ke tashi.
"Tabbas ranar dana fara gane kin kamu da sona ranar dana kama ki kina satar kallona, da ban gasgata ba sai da na bi a hankali ina karantar ki, a lokacin dana tabbatar da zargina naji dad'i. Dalilin da yasa nayi miki haka shine ina so na gina garkuwa mai amfani a cikin zuciyarta, i want you to realize just how much you love me, and luckily you did"
Ya k'arasa yana kashe mata ido, kunya ta kamata tayi murmushi kurum. Yace
"Sorry baby nasan kin wahala lokacin amma komai ya wuce ko?"
Ta girgiza kanta tare da k'ara shigewa cikin k'irjinsa tana shak'ar dad'ad'an k'amshin da ke ratsa ta. A haka har bacci yayi awon gaba da ita, ya gyara mata kwanciya har ya k'arasa kallon da yake, sannan ya tashe ta suka je suka kwanta.


*****

Juyi d'aya tayi kan gado wanda yayi sanadiyyar bud'ewar idonta, gefenta ta kalla taga babu Khaleel a kusa da ita, tayi hamma tare da lalubo wayarta ta duba lokaci k'arfe takwas da minti arba'in da takwas 8:48 AM, da hanzari ta mik'e tana salati tayi toilet da sauri tayi brush ta wanke fuskanta ta fito. Bakin k'ofar fita taci karo da wani k'aramin card mai shape d'in heart pink color, an rataya shi a handle d'in k'ofa, anyi  mai design mai matuk'ar kyau, a bangon card d'in an rubuta "OPEN, IT'S A SURPRISE JUST FOR"
Mamaki bayyane a saman fuskanta ta bud'e card d'in taga an rubuta
"Good times become better and bad times become tolerable when shared with a life partner like you" murmushi ya su6uce mata ba shiri, lallai Khaleel sai dai a barshi, wato haka nan ya rubuto mata card lallai tayi sa'a. Ba tare da tunanin komai ba ta fito palo k'amshin turaren wuta ne kawai ke tashi a gidan, tayi tsaye tana k'are ma wurin kallo yayi fes ko ina gwanin kyau. "To waya gyara gidan haka?" Ta fad'a a hankali still tana bin ko ina da kallo, motsin da taji a kitchen ya sanya ta nufo wurin da sauri, turus tayi bakin k'ofa tana k'are masa kallo, sanye yake cikin gajeren wando mai ratsin brown da blue da blue top marar hannu, sai ya d'ora apron saman kayan, kitchen d'in yayi kaca kaca da alama aiki ya ci masa karo, kitchen d'in take bi da kallo cike da mamaki, can gefen cikin tray samosa ce  da spring-rolls sai meat-pie wanda ba'a soya ba, sai can  kaji ne an yayyanka, ta k'ara kallonsa yana yanka albasa yana hawaye, gyaran murya tayi ya kalleta da sauri yayi murmushi
"My princess har kin tashi?"
Sunan ya mata dad'i har wani narkewa tayi, ta daure tace
"Ina kwana ya Khaleel?"
Yace
"Lafiya lau my princess" ta yi murmushi tace
"Me kake yi haka?"
Ya aje wuk'ar dake hannunsa ya kalleta yace
"Mekika ga inayi?"
Tayi murmushi tace
"Aiki mana amma abinda ya bani mamaki ya d'aure min kai shine meya kawo ka nan alhalin ba aikinka bane, aiki nane"
Ya karkace kai yana kallonta yace
"To don aikinki ne sai akayi yaya? Ni nasa kaina don haka kije ki kwanta idan na gama zan kiraki"
Tace
"Wallahi bazan iya ba sai dai nazo muyi tare ko kuma kai ka fita ni zanyi"
Yayi murmushi
"Wane kikeso kiyi?"
Tace
"Nafiso ka fita zanyi"
Yace
"Ay baki isa ba kuma yarinya, amma da kinyi hak'uri na k'arasa na kusa gamawa"
Bata bashi amsa ba kawai sai gani yayi ta  shigo kitchen d'in ta kama masa suka cigaba da yi tare, ba yadda baiyi da ita ba tak'i gashi ba yaso tasan yau ne birthday d'inta, amma yayi alk'warin duk yadda za'ayi surprising nata zaiyi. A tare suka kammala komai suka jera kan dinning, Hanifah tana k'ok'arin gyara wurin tayi tsai tana kallonsa can kuma tace a hankali.
"Ya Khaleel"
Ya d'ago yana dubanta da murmushi a saman fuskansa yace
"Na'am my princess"
Tayi murmushi tace
"Bak'i zamuyi ne?"
Yace
"Eh"
Tace
"Suwaye zasu zo?"
Yace
"Wasu ne?"
Tace
"Su wa..."
"Kinga da ki tsaya kina cika ni da tambayoyi gwara kawai kije kiyi wanka ki shirya kafin su k'araso"
"To" tace bayan ta k'arasa gyara wurin ta shige ciki. Ajiyar zuciya ya sauke tare da shigewa ciki shima yayi wanka, ya shirya cikin farar shirt da ash wando, sai k'amshi yake zubawa. Cards d'in da ya siyo na birthday wishes but also romantically ya aje a saman dinning, sai gift d'in da ya siyo mata na musamman shima ya 6oye. D'akinta ya lek'a tana zaune kan stool din dressing mirror tana sanya y'an kunne, a hankali ya k'arasa tare da rufe mata fuska, k'amshinsa taji wanda ya tabbatar mata da shi d'inne. Murmushi tayi ta d'ora hannayenta bisa nashi tare da zame hannunsa a hankali daga rufe mata idon da yayi, a madubi suka kalli junansu tare da sakar ma juna da wani irin murmushi mai k'ayatarwa. Sun juma a haka, a hankali kafin Khaleel ya k'ar6e d'an kunnen daga hannunta yace
"Kawo na taya ki sawa"
Tayi murmushi bata san lokacin da tace
"Thanks my love" yace
"Me kika ce?"
Ta k'walalo idanu waje tare da rufe fuskarta tace
"Bance komai ba"
Yace
"Bawani nan ay naji ki, ki d'an k'ara maimaitawa sunan yayi dad'i"
Tayi murmushi tace
"Nace thanks my love"
Murmushi yayi ya sanya mata d'an kunnen sannan ya mik'ar da ita tsaye tare da sak'alo hannayensa ya zagaye wuyanta yana kallon cikin idonta. Yace
"I have a surprise just for you"
Tace
"What is it?"
Yace
"It's a surprise just follow my lead"
Tayi murmushi tace
"Ok"

Hannunta ya kamo suka fito daga d'akin, dinning taga ya nufa tare da ja mata kujera ya zaunar da ita, ita dai sai binsa take da kallo, shima zama yayi kan kujera suna fuskantar juna, idanunta ne suka sauka kan card d'in da ya aje mata gabanta, ta kalleshi yayi mata murmushi
"you are free to see"
Murmushi tayi ta d'auka tana karantawa, tsantsan mamaki wai yau birthday d'inta har ta manta sai Khaleel ne zai tuna mata? Ko da yake ba abin mamaki bane dama ya saba mata haka tun kafin suyi aure. Amma dai na yau special yayi mata, ta sauke ajiyar zuciya ta kalleshi yayi murmushi yace
"Happy birthday, Allah ya raya ki da imani, ya baki y'ay'a na gari, Allah ubangiji ya k'aro shekaru masu albarka ya nuna mana y'ay'an mu mahaddatan alk'ur'ani"
Tabbas addu'an nan ta mata dad'i ba kad'an ba, tace
"Amin, Amin ya Allah, thank you so much Ya Khaleel Allah ya saka da alkhairi"
Yace
"Bakomai bana son wannan godiyar, taso kizo nan ki zauna"
Ya nuna mata kan cinyarsa, ba musu ta mik'e tana zuwa ya jawota ta fad'o bisa shi, ya ja hancinta yana dariya, itama dariyar tayi. A haka ya zuba musu abinci ya shiga bata itama ba 6ata lokaci ta soma bashi, a haka suka kammala suna fira da labarai masu dad'i.
Bayan sun gama ya ciro d'an box d'an k'arami tare da bud'ewa, zobe ne silver mai kyau sai shinning yake, tana kallonsa ya zura mata a yatsanta na tsakiya, ya mata daidai kamar don ita akayi shi, ya kalleta yace
"I love you so much Hanifah, wannan zoben tukuicin k'aunar ki a gareni ne, na gode da kika soni kika k'aunace ni, banida abinda ya fiye min wannan jin dad'i a rayuwarta"
Murmushi tayi tace
"Nima haka"
Yayi dariya
"Kema me?"
Ta rufe fuskarta tana dariya tace
"Nima ina sonka"
Hugging nata yayi tsam a jikinsa yana shak'an dad'ad'an k'amshi dake tashi daga ko wane sak'o na jikinta.
She's so lucky to have a husband like KHALEEL, sai a yanzu ta soma ganin wautarta tun farko, meyasa ta k'i KHALEEL? meyasa ta k'i masoyinta na hak'ik'a har tana wulak'antasa, tabbas batada masoyi na gaskiya sama da KHALEEL, kuma ta gode ma Allah da ya nuna mata gaskiya tun kafin akai ko ina.
A haka dai masoyan suka wuni suna nuna ma junansu kulawa ta musamman had'e da soyayya mai ban mamaki.....!



MSB✍🏼

No comments: