Sunday 2 July 2017

AUREN FANSA 13

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹



          🌹13 🌹

http://MaryamSBello.blogspot.com

Duk'e take tana faman wanke toilet Zarah ta lek'o, cikin muryar rad'a rad'a tace.
"Meenah bari na taya ki."
Meenah ta d'ago tana duban Zarah tace
"A'a ki rufa man asiri Zarah, yanzu da Mami tazo zata dake ni."
Zarah tayi murmushi
"Ay dana ji ta taho zan bari..."
"Nidai gaskiya ina tsoro ki bari kawai..."
Da sauri Bilki ta shigo d'akin, tana zuwa ta jawo Meenah.
"Ke maza kije kiyi wanka ga babanku nan dawowa, bar wankin toilet d'in zan k'arasa..."
Halin maman tasu na basu mamaki, sun rasa meyasa da babansu ya kusa dawowa sai ta hana Meenah yin ko wane aiki.
Sum sum Meenah ta fice daga d'akin.
"Mami meyasa kike sa Meenah aiki ni baki sani? Kuma meyasa idan Baba ya kusa dawowa kike kora Meenah tayi wanka ko
taci abinci?"
Bilki ta daka mata tsawa
"Ke! Kar ki k'ara min ko wace irin tamaya a nan kina jina? Kema fita ki bani wuri."
 Sum sum ta fita tana jinjina hali irin na uwarta.

Ba'a jima ba ya shigo gidan a gajiye, Bilki ta tasa yaran gaba suna kallo ya shigo da ledoji a hannunsa, da sauri Zarah da Meenah suka mik'e suka kar6a kayan hannunsa.
Bayan ya zauna yana murmushi yace
"Kaza ce da ice cream na siyo maku kuje kuci." Da murna suka shige ciki. Bilki tana murmushi tace
"Yaran nan na shan gata Alhaji, kana tunanin baiyi yawa ba kuwa?"
Alhaji yayi murmushi yace
"Bilki kenan, ay ba wani abu nake musu na gatanci ba, bana sangarta su, haka ma bana 6ata su da kud'i ko wani abin duniya, abinci ne nake basu wanda kuma yin hakan ba laifi bane."
Tayi murmushi
"Bakayi laifi ba kam nima dama wasa nake maka."
Sai kuma yayi ajiyar zuciya
"Kinsan abinda ke damuna?"
Tace
"Sai ka fad'a."
Yace
"Mutuwar Alhaji Adam, su waye marassa imanin da suka bishi har gidanshi suka kashe shi dashi da matarsa?"
Bilki ta had'iye miyau da k'yar tace
"Nima abinda yake damuna kenan kullum Alhaji, nasan mahassada ne kawai."
Ya numfasa
"Wai me duniyar nan keso ta zama ne? Mutane akan kud'i ba abinda bazasuyi ba?"
"Uhm...uhm Alhaji bari na kawo maka ruwa kasha."
Bai kawo komai a ransa ba yace
"To."

Aikuwa da daddare Meenah bata samu abincin dare ba, wai ay taci kaza ta k'oshi bataga dalilin da yasa za'a bata abinci ba.
Da safe Baban na fita aiki ta jibga mata uban wankinta dana Zarah, duk da suna da mai wanki amma tsabar mugun hali irin na Bilki sai da ta jibga mata wankin daya fi k'arfinta. Tana gama bata wankin ta shigo daidai bakin k'ofa taci karo da Zarah tana fad'in.
"Mami idan Baba ya dawo sai na fad'a masa abinda kike ma Meenah idan baya nan..."
Finciko ta taji anyi, tayi d'aki da ita tana zuwa ta shiga tsula mata bulala, sai data zane ta tas sannan tace
"Wannan kad'an nayi miki akan bayan kin fad'a masa, sai jikinki ya gaya musu, zaki fad'a ko kuwa?"
Da sauri ta girgiza kanta tana kuka.

Haka dai kwanaki sukayi ta tafiya cike da wahala a gurin Meenah, sam batada lokacin kanta sai aikin gida, bata samun lokacin karatu sai can cikin dare, sheyasa gata nan wata 'yar ficit sai tsawo amma ba kumari, Zarah kuwa wata 'yar duma duma ga ta fara sol fatar jikinta irin ta 'yan hutun nan ce da basu san wahala ba, ita kuwa Meenah batada k'iba sai tsawo.

***

A haka rayuwar tayi ta mirginawa, har Meenah ta kai SS3 a yayinda Zarah ke SS2, yaran sun girma sun zama 'yan mata, daka gansu tare sai ka k'ara kallonsu don kuwa ko a makaranta tare sukeyin komai, shiga aji kawai ke raba su.
Halayen nasu ne kawai ya banbanta, ita Meenah tana da wani calm attitude, tanada nutsuwa komai nata a hankali takeyinsa, ko
maganarta wani a hankali takeyi, ba kamar Zarah da take abu kazar kazar ba, ita tsaye take kamar ba mace ba, she's too lousy dai tana da hayaniya....
Sannan uwa uba Meenah ba irin girkin da bata iya ba, da kuma ko wane irin aiki yi take irin su shara wanke wanke, wanki da sauransu, kuma bata gajiya da gyara wuri koda za'a shekara ana 6ata shi, Meenah bata damu da abin duniya ko wayar da take rik'ewa batada komai na social media a ciki, ita dai kawai tayi waya idan ta kama shikenan, amma Zarah akwai son harkar social media, ga yin hoto kamar hauka, to a wannan fannin ne halayensu suka banbanta, ga son jiki bata iya ta6uka komai na aikin gidan saboda haka ta taso ba'a sata tayi, sheyasa ko gyaran d'akin bata iya ba, sai Meenah tazo ta gyara mata...



MSB💖

No comments: