Monday 10 July 2017

AUREN FANSA 21

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹



          🌹21 🌹

http://MaryamSBello.blogspot.com


Bayan kwana biyu da safe sai ga Baba ya diro garin wai da niyyar d'aukar su Meenah, hanakalin Meenah ya tashi don tasan da k'yar idan Mami zata barta tayi soyayya ba, tasan dai Baba baida matsala, amma Mami take ji. Aikuwa tana sanar da Faruk cewar gobe zasu koma Abuja yace shima zai tattara ya koma daman ya gama abinda ya kawo shi, sai ya koma zai cigaba da kawo mata ziyara.
Washe gari kuwa suka tattaro suka dawo gida.
Duk da hankalinta a tashe yake hakan baisa taji ko d'ar a zuciyarta game da son da takeyi wa Faruk Adam ba. A ganinta shi d'in yasan menene so, yasan darajar abinda yakeson, ya kuma iya tafiyar da shi ta hanyoyi daban daban, ya iya tarairaiyar mace da bata kulawa yadda ya kamata. Sheyasa son da take masa shi yake k'ara bata k'warin gwiwar fuskantar Mami.
Suna dawowa kuwa kusan kullum sai yazo, har dai ya zama d'an gida, yadda taga Baba ya amshi Faruk hannu bibbiyu ya sanya dole taja bakinta tayi tsit, kuma kullum yazo Zarah ke raka Meenah fira, hakan yasa ita kanta Mamin ta rasa gane wurin wa yake zuwa, amma tana fatan wurin Zarah yake zuwa, don a yadda take gani mutum ne mai kud'i sosai.


*

K'arfe takwas na dare kamar kullum Faruk ya isa gidansu Meenah, kasancewar ya zama d'an gida tsakanin Baba da Mami.
Bayan sun gaisa da Baba, a lokacin Baba yana da niyyar fita, haka ma Mami tana sama tana fama da lissafin kud'in kasuwancinta.
Yana nan zaune yana jiran Meenah. Aikuwa sai gata ta fito tayi kyau kamar kullum cikin material mai taushi silver da ratsin bak'i a jikinshi, d'inkin doguwar riga, d'inkin bai kama jikinta ba. Tun daga nesa suke sakarma da junansu murmushi mai sanyi. Ta zauna a kujerar dake fuskantarsa, centre table ne mai bak'in glass a tsakiya wanda aka d'aura kayan marmari cikin tray kala kala a cikinsa, irinsu Apple, grapes, banana, orange, pear da sauransu. Zamewa yayi ya zauna k'asa gami da rausayar da kai yace.
"Barka da hutu!".
Dariya ya bata sosai saboda yadda yayi maganar, tace
"Alhamdulillah, muna ta sha kam."
Yayi shiru zuwa wani lokaci sannan yace.
"Zuwa yaushe kike ganin za'a aurar da ke?"
Ita dariya ma ya bata tace
"Aure ay lokaci ne... sai lokaci yayi sannan."
Ya langa6ar da kai yace
"Haka ne, amma ni ko yanzu aka bani ke zan kar6a hannu bibbiyu, zan nuna maki k'auna ta ban mamaki, sai dai bansani ba ko ke zaki so ni kamar yadda nake son ki... sannan ina so idan Allah ya kaimu zan sanar da iyayenki cewar aurenki zanyi..."
Ta lumshe idanu cikin wata sabuwar k'auna dake k'ara mamayarta, ta kuma k'ara lallu6e mata zuciyarta, tace
"Kar kayi tantama a kaina ya Faruk, soyayyarmu had'in Allah ce, i respect you  and your values.. Faruk d'in da nake so bana ganin kowa sai shi, bana jin k'aunar kowa sai shi... haka ma banida buri a yanzu sama da mallakarka a matsayin mijin aurena na har abada..."
Sai bayan ta furta hakan kuma kunya ta kamata had'e da mamaki, yadda ta zauna tayi ta zuba kamar pampo, amma daga baya sai take ganin kamar su6utar baki tayi. Sai tayi saurin cewa
"Nidai fatana ka rik'e soyayya ta, kada kaci amanata, ka yarda dani, idan kayi min wannan to ni kuma nayi maka alk'awarin baka dukkan kulawa."
Sai ya rasa abin cewa kuma, murmushi tayi ta sauko k'asa ta shiga yanka masa kayan marmarin yana sha.


***

Bilki ta soma tsarguwa da yawan zuwan Faruk cikin gidansu, da yawan ke6ewa da sukeyi shida Meenah akan Zarah suna fira. Ga wata sabuwar al'ada da Meenah ta 6ullo da ita na yawan kwalliya wadda ta gama lura don Faruk take yinta. Ta gigice ta shiga damuwa sosai, neman k'arin bayani takeyi  tasan Zarah bazata ta6a fad'a mata ba saboda an ta6o 'yar uwarta haka bata ganin aibunta, su koda wani abin ne ba'ajin ta cikinsu kashewa sukeyi su rufe babu mai ji. Ko fad'a sukayi baya wuce yini d'aya idan kuwa sun dad'e to kwana d'aya ne sun shirya sun kuma manta komai. Don haka taga babu mafita illa ta tunkari Meenah tayi mata bayanin abinda take zargi.


K'arfe tara na dare ta raka Faruk ya tafi, tana dawowa ta taradda Mami tsaye gefen gadonta ta hard'e hanyayyenta wuri d'aya tana huci.
"Mami....?"
Ta dube ta sosai daga sama har k'asa tace
"Amina....!"
Bata amsa ba illa ta dube ta a yadda take kiranta cikin wata irin murya. Sai kawai ta jeho mata tambaya
"Meke tsakaninki da Faruk?"
Ta sunkuyar da kanta k'asa, batayi magana ba, sai da Bilkin ta daka mata uwar tsawa mai gigita k'wala.
"Bada ke nake magana ba?!"
Cikin sark'ewar murya tace
"Da...ma yace yana...so...na tun muna Katsina, kuma daman gobe ne Faruk d'in yake niyyar sanar daku muna son junanmu... mun yanke shawarar yin au..."
Ji kake tassa!!! Mami ta d'auke ta da wani irin wawan marin da har sai data ga giftawar wuta, ta nemi ji da ganinta ta rasa!



MSB💖

No comments: