Monday 3 July 2017

AUREN FANSA 14

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹


Dedicated to Susu, thank you for everything!❤️


          🌹14 🌹

http://MaryamSBello.blogspot.com

Bakajin komai a d'akin sai k'yalk'yatar dariya, da k'yar suka dakata, Laila ce ta soma magana.
"Shegiyar gari, wato kina nan kina facaka cikin dukiya, kina nan kina taka matsayin da kika d'ad'e kina burin takawa, kina nan kina hawa kud'i ki taka kud'i ki yadda kikeso a cikinsu, lallai shawara d'aukar d'aki yau gashi mun da'auka tayi mana amfani!"
Suka sake sa dariya, Bilki tace
"A da na bijirewa shawararki, kuma da farko na tsorata amma yanzu abin sai wanda ya gani."
Suka sake sa dariya gami da tafa hannu. Laila ta kuma cewa tana dariya
"Yayi daidai kin birgeni! Yanzu keda talauci sai dai ko a lahira..."
Bilki tace
"Kada Allah ya had'ani da shi koda a lahirar ne ma. Yanzu tsoro na kada wata rana a gano mu ya zamuyi kenan?"
Laila tace
"Daman ay ke bugun Abuja ce, daman ke kalarki bata k'auye bace ba..."
Bilki tayi dariya
"To kin dai gani, rabona da k'auye har na manta, tunda muka dawo Abuja idan kin ganni k'auye sai dole..."
"Assalamu Alaikum..."
Ta shigo d'auke da tray d'in lemo da glass cups guda biyu sai plate d'in cincin da dambun nama. Ta ajiye tray d'in sannan ta gaishe su, sai da suka watsa mata harara sannan suka ce "Lafiya."
Bilki tace
"Kin d'ora abincin rana?"
Tace
"A'a yanzu zan d'ora."
Bilki tace
"Aikin me kike da tun d'azu baki d'ora ba har kusan k'arfe sha biyu?"
Tace
"Wanke wanke ya taru da yawa shine na..."
"Yi min shiru a nan!" Ta daka mata tsawa.
"Duka duka wanke wanken guda nawa ne da har zaki ce yayi yawa? Sai anyi magana ki dinga rissina kai kamar wata yarinyar kirki, zaki wuce ki d'ora ko sai na san me zan miki!"
"Uhm... me za'a dafa?"
Tayi tsaki
"Ki dafa mana fried rice da peppered chicken, sai ki had'a coleslaw, akwai kaji a freezer ki d'auki guda biyu kiyi amfani dashi. Sai kinsan halin babanku yafison tuwo, kiyi masa tuwo miyar busassar ku6ewa."
Da k'yar tace "To." Ta fice idanunta cike da hawaye!
"Anya bataji mu ba d'azu?" Cewar Laila cike da damuwa.
"Ko taji me za'ayi? Ah babu ay."
Sukayi dariya Laila tace
"Haka ne fa."


Tana kitchen tana yanka kaji Zarah ta shigo tana sanye da wando jeans sky blue sai light pink shirt marar hannu.
"Meenah zo ki ga..."
Da mamaki take kallonta tana d'aga mata fuska don taga idan idanunta ba k'arya suke nuna mata ba.
"Meenah kukan me kike? Hala Mami ce? Me tayi miki?"
Ta k'ak'alo murmushin dole tace
"Babu komai, wani abu ya fad'a min ido ne."
Zarah tayi murmushi
"Uhm baki iya k'arya ba Meenah, ni nasan wani abu Mami tayi miki."
Meenah tace
"Bakomai amma don Allah Zarah zan miki tambaya inaso ki fad'i man gaskiyar abinda kika sani."
Zarah tace
"Ina jinki."
Meenah tace
"Don Allah a iya zamanki a gidannan kin ta6a ji koda a wurin wani ne cewar tsintso ni akayi?"
Zarah ta k'yalk'yale da dariya harda duk'ewa, Meenah ta kalleta galala cike da mamaki tace
"Meye haka wai Zarah? Ya ina tambayarki kin tsaya kina min dariya?"
Har yanzu dariya takeyi, da k'yar ta tsagaita tana duban Meenah tace
"Anya baki buk'atar ganin likita Meenah? Kanki d'aya kuwa?"
Meenah ta k'ule tace
"Shikenan sai kije kiyi ta dariyar, gani kike kamar wasa nakeyi ko?"
Zarah tace
"Daman ay wasan kikeyi, ta yaya ma zaki fara irin wannan tunanin?"
Meenah tayi murmushi mai ciwo tace
"Dole nayi tunanin haka Zarah, na rasa meyasa Mami bata sona..."
Da sauri Zarah ta rufe mata baki
"Kar kice haka, ay indai zaki kula halinta ne haka, koni tana min."
Meenah tace
"Eh amma ba kamar yadda take min ba, dole ne na fara tunanin duk yadda akayi ko tsinto ni akayi ba'a san asali na ba, ko kuma ni 'yar rik'o ce."
Zarah ta 6ata rai
"To yayi miki kyau, ki cigaba da fad'in haka ni kuma daga yau na daina miki magana a gidannan."
Meenah ta juyo da sauri
"Haba dai?"
Zarah tace
"Ki cigaba ki gani."
Da sauri Meenah tace
"La na bari, ya za'ayi na bari mu 6ata?"
Zarah tayi murmushi
"Yawwa sweet sis bara na taya ki aikin don ayi sauri, kuma idan kika hanani yi sai na daina miki magana a gidannan."
Ta fad'a cike da shagwa6a, Meenah tasa dariya ta kwaikwaiye ta
"To bazakiyi ba wuce ki tafi ki kwanta."
Zarah tace
"Nak'i"
Haka suka k'arasa aikin suna zolayar juna, wasu abubuwan sai da Meenah ta dinga koya mata, kuma ba laifi tana fahimta.


***

"Wai bazakuyi sauri ku fito ba Jidda? Kodai a tura driver ya d'auko su ne?"
Da sauri Anisah ta fito cikin shigar atamfa d'inkin doguwar riga kalar blue and purple sa ta d'ora purple mayafi.
"A'a Mama mu zamu d'auko su, nifa na gama shiri su ya Jidda ne tun d'azu basu gama ba."
Mama tayi dariya.
"Au kin k'agu kiga yayan naki hala? Wannan irin zakwad'i haka?"
Anisah dariya, daidai nan sauran 'yan matan suka fito sun sha ado sunyi kyau inda dukansu suke cikin shiga iri d'aya.
Yusra tayi dariya
"Kai Mama duk kin k'osa a dauko miki yaranki ne haka?"
Mama tayi dariya
"Ke ni ba kakarki bace, ku wuce ku tafi haka nan."
Da sauri suka tafi suna dariya...

Jidda ta dubi agogon dake mak'ale a hannunta, k'arfe sha biyu harda rabi ta wuce.
"La Ibrahim kayi sauri sun kusa sauka."
Ibrahim yayi murmushi
"To ranki ya dad'e."
Tunda suka dira a airport hankalinsu ya kwanta ganin har yanzu basu sauka ba, amma daga inda suke suna hango jirgin yana niyyar sauka k'asa. Duk sukayi ajiyar zuciya.
A hankali jama'a suka fara fitowa daga jirgin, haka ma duk wanda ya hango d'an uwansa sai ya ruga ya taro sa.
Tsaye suke kusa da kujerar zama wato (waiting chair) idonsu k'yam saitin k'ofar jira kawai suke suga ta inda zasu 6ullo.


MSB💖

No comments: