Wednesday 12 July 2017

AUREN FANSA 22

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

🌟🌹Pure Moment Of Life Writers🌟🌹

Dedicated to Mrs Fawwaz, Sadnaf, Momyn Sultan, my sakwara, Maman Khady, Jannatuwa, Faridat Musa, Rufaida Yusuf. One luv guys❤️😍

          🌹22 🌹

http://MaryamSBello.blogspot.com

Bilki ta soma magana cikin fushi.
"Kin bani mamaki Meenah, yanzu har yaushe idonki ya bud'e da kike neman k'wace ma 'yar uwarki saurayi? Ke ko kunya bakiji ace 'yar uwarki tana son wani kema kina sonsa? Fatima fa k'anwarki ce Amina, ay na d'auka ke mai d'auka ce ki sadaukar mata da wani idan ta kama, amma wai ke! Kece mai k'wacewa Meenah."!
Ta share hawayenta cikin tsantsan mamakin Mamin tasu, muryarta na rawa ta soma magana.
"Mami Faruk bai ta6a cewa yana son Zarah ba, ni yake so tun asali, ko ita Fatiman ba sonsa take ba, ni bansan ina kika ji cewar saurayin Fatima ne ba, idan ma kina tunanin cewar saurayin Fatima ne to ki daina tun wuri." Sai kuma ta juya mata baya gami da had'e hannayenta wuri d'aya tace
"A baya kinsha k'wace min kyauta a makaranta, amma gaskiya yanzu bazan yarda a k'wace min Faruk ba, hak'uri zakiyi ki sa mana albarka!"
Sai kawai Bilki tasa salati, yau tana fad'a Meenah na fad'a.
"Lallai wuyanki yayi k'wari ya isa yanka, akan nace kin k'wace wa 'yar uwarki saurayi kike neman ki fad'a min magana Meenah."
Ta fad'a tana nuna kanta.
"Bafa saurayi na bane Mami."
Duk suka d'aga ido tana tsaye bakin k'ofa idanunta sun kad'a daga fari zuwa ja! A hankali ta k'araso cikin d'akin tana share hawaye tace
"Akan me zaki mare ta akan maganar da bakida tabbas a kanta?  Mami! Ki sani Meenah 'yar uwata ce ta jini, ta yaya kike tunanin zata k'wace min saurayi? To bari kiji abinda baki sani ba, Faruk saurayin Meenah ne bani ba, ko don kinga ina zuwa muna fira dashi kikayi tunanin saurayina ne?" Tayi murmushi tace
"To ba haka bane, ni kawai mun saba ne sheyasa kikaga ina fita amma lokuta da dama ay tare da Meenah muke zuwa, duk randa kika ga naje ni kad'ai to Meenah ta tura ni akan in je kafin tazo." Ta kalli Meenah dake hawaye wani na bin wani, tasa hannu ta share mata tace
"Daina kuka 'yar uwata, kiyi hak'uri da abinda Mami tayi miki, sannan kisa a ranki Faruk naki ne ke kad'ai kinji?"
Suka rungume juna suna kuka.
Haushi ya kashe Bilku kafin kuma sum sum ta fice daga d'akin cike da kunya!
A wannan daren Bilki batayi bacci ba, yadda taga rana haka taga dare.

Washe gari Meenah taga fushin Bilki fiye da yadda ta saba gani, da Zarah take sabgoginta, itama sai ta kama kanta a d'aki tak'i fitowa tana karance-karancenta. Sai dai zuciyarta cike take da tsoron Mamin, data tuna marin da tasha jiya sai gabanta ya fad'i.


*

K'arfe goma na safe Faruk yazo, Bilki na zaune parlor tana chanza channel, tun daga jin sallamarsa tabi ta d'aure fuska yadda bata ta6a yi masa ba. Yana zuwa ya zube k'asa yana gaishe ta, sai kawai ta kafa masa ido bata amsa ba, k'arshe ma sai ta mik'e ta haye bene zuwa d'akinta ba tare da tace komai ba. Meenah na daga bak'in k'ofar kitchen tana ganin komai, ita kunya ma ta kamata ta kuma kasa k'arasowa ciki. Sai da ta d'auki akalla minti biyu sannan tayi ta maza ta shigo parlon kanta a k'asa. Dukkansu sunyi shiru aka rasa mai fara yin magana a cikinsu.
Da k'yar Faruk ya daure yayi murmushi cikin basarwa yace
"Munyi ma Mami laifi ko?"
Ta d'an d'ago suka had'a ido, ta lumshe idanu tace.
"Tun jiya take haka, mun rasa gane mata."
Yayi shiru cikin tunani, can kuma yace
"K'ila bata amince dani ba..."
Tayi saurin cewa
"Bakomai zata huce ne."

Baba ne ya ke saukowa daga mattakalar bene Bilkin na biye da shi tana rik'e da briefcase d'insa, ya hango shi a parlor zaune, da sauri ya mik'e cikin girmamawa yabi bayansa don yaga kamar parlonsa ya nufa daga can 6angarensa.
Baba nakan kujera Faruk na gefensa daga k'asa. Bayan sun gaisa kamar kullum cikin mutunci da girmama juna, can Baba yace
"Umar Faruk."
Ya d'ago da fararen idanunsa ya dube shi yace
"Na'am Baba."
"Meke tsakaninka da Amina?"
Faruk ya rud'e ya shiga inda inda saboda yadda yaga Baban ya masa kwarjini, take kuma ya sadda kansa k'asa.


MSB💗

No comments: