Thursday 27 July 2017

AUREN FANSA 31

✨⭐✨⭐✨⭐✨⭐✨
⭐🌹🌹🌹⭐🌹🌹🌹⭐
🌹⭐✨⭐🌹⭐✨⭐🌹
🌹✨⭐✨⭐✨⭐✨🌹
✨🌹✨⭐🌞⭐✨🌹✨
⭐✨🌹✨⭐✨🌹✨⭐
✨⭐✨🌹✨🌹✨⭐✨
⭐✨⭐✨🌹✨⭐✨🌟


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
AUREN FANSA!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

🌹Na🌹

     🌹MARYAM S BELLO🌹
             (MSB)

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

 *_We don't just entertain we touch the heart of readers_*

PML

                 🌹31 🌹


http://MaryamSBello.blogspot.com

Komai tsab tuni ta kammala, ita da gida sun d'auki haske da k'amshi. Ta dafa masa Chinese rice with vegetable soup, sai salad. Bayan ta gama sai ta fad'a wanka ta kammala ta fito, yau ranar farko data bud'e 6angaren English wears, ta fiddo wani shegen tight wando kalar ash gashi marar tsawo da riga dark pink mai k'aramin hannu. Ta dad'e tana shawarar ta saka su, daga k'arshe dai tayi shahada ta sa duk da tana jin kunya amma dole ta yakice ta wuri d'aya. Bayan ta saka kayan sai ta taje kanta da mayuka masu k'amshi tayi parking d'inshi da pink ribbon daga can tsakiya sai jelar ta sauko bisa gdon bayanta. Tabi da turaruka masu dad'i.
Ta gama shiryawa da kusan minti goma idanunta na kan k'ofa har ta gaji da kallo, ta jawo laptop nata da Baba ya siya mata itada Zarah ta soma daddannawa, bata ankara ba sai taji charab an kamo ta. Ta mik'e zumbur cike da tsoro, sai data juyo suka kalli juna yayi murmushi.
"Ashe kinada tsoro haka baby?"
Ta zum6uro baki abinda ke birgesa tace
"A'a ba tsoro naji ba."
Yace
"Tsoro kika ji mana, bayan na gani da ido na."
Tayi dariya tace
"Sannu da zuwa."
Yace
"Yauwa."
K'irr! K'arar door bell ta shiga dodon kunnensu, ya dube ta yace
"Koma ciki Bala direba ne zai shigo da kaya."
Tayi ciki bata k'ara fitowa ba, ta wuce ta had'a masa ruwan wanka, da kanshi ya lek'o yace fito muyi fira. Tayi dariya tace
"Kai dai ka shigo ka watsa ruwa kaji dad'i."
Yace
"Angama baby."
Da taimakonta ta zare masa komai, ya shiga toilet, ta fiddo masa singlet da gajeren wando. Yana fitowa kuma yace
"Zo ki shafa man mai." Da mamaki kuma ya dubi kansa wanda baisan ya furta hakan ba. Ta sunkuyar da kanta k'asa tace
"Uhm bari naje na gyara dinning."
Da sauri ta fice inda shi kuma ya cigaba da kallon k'ofar data bi, ajiyar zuciya ya saki ya shirya tsab ya fito.

Suna tsakar cin abinci wayarsa ta fara ringing, ganin Jidda yasa gabansa ya fad'i, cikin sanyin jiki ya d'auka sannan ya dubi Meenah data tsare shi da idanu. Yace
"He...llo."
"Hello ya Faruk a gaskiya fushi nake da kai."
Yayi yak'e yace
"Menayi?"
Tace
"Har yanzu ko kazo wurina ko? Daman nasan baka sona."
Yace
"Ba haka bane zanzo..."
"To yaushe?"
Ya kalli Meenah har yanzu shi d'in take kallo. Sai ya mik'e sum sum ya shiga kitchen. Zuciyarta ta sosu, ko ba'a fad'a mata ba tasan da mace yake waya. Macen ma wadda zai aura, bata ankara ba hawaye suka zubo mata, jin alamun tafiya yasa tayi saurin goge hawayenta cikin dakewa ta k'ak'alo murmushi tana dubansa a lokacin da yake zama kan kujera. Ya d'an murmusa yana kauda fuska cike da kunya.
Sai da suka gama cin abincin ne ya mik'e yana aduba agogon hannunsa. K'arfe 8:44pm. Kallon Meenah yayi yace
"Zan fita bazan jima ba zan dawo."
Tace
"Yanzu? Ina zakaje?"
Yayi yak'e yace
"Ahh karki damu bawani dad'ewa zanyi ba."
Da sauri ya koma ciki ya sake shiri cikin light brown yadi mai matuk'ar taushi, har hular kansa kalar kayan, yayi kyau sosai. Kiss yayi mata a kumatu yace
"Sai na dawo baby."
Haka tana ji tana gani ya fita, sai k'amshinsa da ya bar mata a hanci, wanda ta tabbatar wurin budurwa zaije. Kuka ya k'wace mata ta yi d'akinta da gudu ta fad'a kan gado. Zuciyarta na tafasa kamar ruwan zafi.


***


Tsaye take a gaban madubi ta ci ado na k'in k'ari kai kace zataje tarbar matar gwamna, sanye take da wani french lace kalar ja da adon silver a jikinshi. Wardrobe nata ta bud'e, ta fiddo wani kwalli da turare da wata laya da k'awarta Luby ta bata.
"Wallahi idan kikayi amfani da kayannan Jidda kin gama da Faruk, sai yadda kikayi dashi, sannan ba abinda zai sa a gaba sai ganin ya mallake ki a matsayin mata, don haka ki tabbatar kinyi amfani dasu a daren da zai zo. Sannan wannan kuma a abinci zaki barbad'a masa ko lemo da zarar yasha yazo hannu!" Wannan shine maganar da Luby ta fad'a mata a lokacin da tazo ta kawo mata kayayyakin.
kwallin ta shafa ta fesa turaren, sai wata laya da akace ta rik'e a hannunta gam kar ta saki har sai ya tafi. Bayan ta kimtsa wayarta ta fara ringing, ganin mai kiran yasa ta saki murmushin mugunta sannan ta d'auka cikin kashe murya tace
"Hello my dear."
Yace
"Gani nan parlon Dada, da mun gama gaisawa zan iso main parlor ki jira ni a can."
Tace
"Angama honey."
Kashe wayar yayi ba tare da ya k'ara magana ba.
Dada ne yake shigowa, bayan ya k'araso ya zauna nan suka gaisa. Dada yace
"Ya gida ya iyali?"
Yace
"Alhamdulillah."
Dada yace
"Tunda nace ka nemi yardar matarka baka k'ara zuwa ba ko?"
Yace
"A'a Dada wallahi aiki ne yasa ni a gaba, nayi magana da ita ay ta yarda ta amince."
Dada yayi murmushi
"To kaga ka sauke nauyi, Allah ya tabbatar da alheri."
Yace
"Amin Dada, yanzu ma wurin Jiddar nazo mu fahimci juna."
Yace
"Madallah, babu matsala."
Daga haka ya mik'e ya fice.

A sadda Jidda ta fito Faruk na zaune kan kujerar zaman mutum biyu yana latsa waya, tun kafin ta k'arasa ya k'ura mata ido har ta iso yana kallonta.
Ta dube shi sosai ta zauna kusa da kujerarsa don ya shak'i k'amshin sosai tace
Sannu da zuwa."
A kasalance ya amsa a take yaji wutar sonta na ruruwa a ransa kamar ana kunna ashana. Ta dube shi sai taga ya tsare ta da idanu tace
"Yaya Faruk ina wuni ya gida?"
Ya kad'a kai tare da lumshe idanu, ji yake kamar ya kamota ya rungume, ita kam sai matsar layar takeyi tare da wani kad'a jiki tana wani fari da ido. Ya sake dubanta sai yaga tayi wani kyau ji yake kamar ba wacce tafita kyau...
Ta katse masa tunani da cewa
"Bari na kawo maka abin motsa baki."
Yace
"A'a da kin barshi ma bana jin yunwa."
Tayi wani fari da ido tace
"Ayi haka? Ay ko ruwa kasha kaida ba bak'o ba?"
Sai wani kashe murya takeyi. Yayi murmushi yace
"To kawo min ruwan dai ya isa, amma kar ki dad'e don ban gaji da kallonki ba."
Tace
"To yanzu zan dawo."
Ta mik'e cike fa yauk'i da yanga ta tafi, shi kuwa sai binta yake da ido har ta shige kitchen. Ya lumshe idanu kafin ya bud'e jira kawai yake yaga ta fito ko zaiji sanyi a ransa....



MSB💖

No comments: