Saturday 18 February 2017

KHALEEL 19&20

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€



©PERFECT WRITERS FORUM (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻19&20✍🏻✍🏻


Ammi ta dawo hannunta dauke da katon tray, fuskarta dauke da murmushi tace.
"What a surprise? Ban yi tsammanin ganinka yanzu ba Khaleel, meyasa baka sanar dani zaka zo ba?"
Ya dan sosa keya yana dariya
"Wallahi Ammi tafiyar ce nayi ta ba shiri, kawai naji hankalina yayi gida, sannan kuma ai kinsan mun gama tun last week ban dai taho din bane"
Tayi murmushi
"Allah sarki, ai gida daban ne, kuma Allah ya sa anyi sa'a
Yace
"Amin, wallahi Ammi nayi missing girkinki yadda baki tsammani wallahi manegi {manage} nakeyi a can, sai muyi ta fama da na gwangwani"
Tace
"Khaleel kenan, nima nayi kewarka sosai"
Ammi ta aje tray din a gabansa ta shiga zuba masa lemon kwali (exotic), da ka kalle ta kasan tana cikin farin ciki marar misaltuwa, shi kuwa kallonta yakeyi zuciyarsa fes!

Halisa ta shiga dakin Hanifah da kayan guga da aka goge na Hanifah din ta tarar da ita tana sanya kayan bacci, da alama kwanciya zatayi.
Ta girgiza kai kurum ta bude wardrobe dinta tana jera mata kayanta ciki, ta dan dakata da sanya kayan tace.
"Wai nikam Hanifah bakiga yayanki yazo ba? Ai ko yar fira basai kije ki taya sa ba?"
Tayi tsaki a hankali tace
"Banida lokaci"
Halisa ta girgiza kanta ta karasa sanya kayan tare da kulle wardrobe din ta fito.

Tunda Khaleel yazo Hanifah bata fito daga daki ba, a takaice dai yau kwanansa hudu da dawowa amma Hanifah bata fitowa daga daki,
Zuwa yanzu ya kara yarda kiyayyar da Hanifah ke masa a cikin jininta take bata sonsa.
Idan har yana yi mata uzuri a da yanzu fa? Shekaruta goma sha bakwai ta isa ta fara bambance abinda takeso da wanda bataso, basai an tursasa ta ba, shi inda a son ransa ne da Ammi ta bari ta za6esa da kanta baya so ayi mata dole don muddin akayi aurennan akwai matsala.

Washe gari yana dakin Ammi suna fira tace
"In banda shirmen Hanifah da kuruciya ga dan uwanki na jini, wanda yasan darajarki da mutuncinki da kuma ciwonki, amman kirkiri ki nuna bakya sonsa"
Khaleel yayi tsai yana kallonta a nitse, duk da maganar Ammi ta ta6a masa zuciya amma sai ya dake tare da kakalo murmushi yace
"Ammi idan har Hanifah tana da wanda takeso ni sai inga hada mu aure bashida wani amfani..."
Ammi ta katse sa tare da cewa
"Kul na kuma jin kace haka Khaleel, hadin aurenka da Hanifah babu abinda ya kaishi amfani a wurina, da in dauke ta in bada ita ga wani can wanda bansan halinsa ba, gwara kai din da nasani, badai ka kammala karatunka ba, aikin ne kuma shima muna nan muna addu'a, ita kuma ta kammala karatunta na secondary to me ya rage? To bari ma kaji karshen zancen na kira yaya Hamza( yayan Ammi dake zaune a kano) na fada masa zancen auren naku, shima kuma yayi farin ciki sosai da hakan, ya sanar da ni karshen satin nan zasu zo ayi maganar auren naku in ta kama ma a sanya rana za'a sanya a ranar"
Ya rasa me zaiyi farin ciki ko kuwa akasin haka? Nan 6angaren yana fama da soyayyar Hanifah wanda burinsa yaga ya mallake ta, dayan 6abgaren kuwa tsanar da take nuna masa shi yake karya masa gwiwa.


******


Cikin ikon Allah kafin karshen satin takardar list din daukar ma'akaita ta iso ta cikin email dinsa, bai bude ba da wuri ba kasancewar tunda sassafe sakon ya shigo a lokacin kuma bacci yake, sai bayan ya tashi wauraren goman dare yayi arba da sakon, sunanshi ya shiga nema aiko shine layi na biyu a cikin list din, Parah-urbankonsuit-sabon_gari-kaduna, farin cikin da yaji baya misaltuwa, gashi yana tunanin yana kusa da gida baiyi nisa ba, lambar wayarsu suka sanya take ya kira, bugu uku suka dauka, ya sanar masu ya ga sunansa a list din daukar ma'aikata, suka ce masa eh zaizo interview ranar monday, yayi farin cikin sosai, take ya fita don sanar ma Ammi itama tayi farin ciki sosai ta sanya masa albarka, banda Hanifah da ko kallo bai ishe ta, bare ma yasa ran zata sa baki itama, wani mugun kallo Ammi ta watsa mata ba shiri tace.
"Congrats Allah sa alkhairi"
Yayi yalwataccen murmushi yace
"Amin lil sis godiya nake"
Harara ta watsa masa sannan ta tashi tayi dakinta da sauri.


*******

Karfe sha biyun ranar asabar su Yaya Hamza suka iso da shi da kaninsa mai suna Aliyu, dama su kadai ne yan uwan Ammi ita kadai ce mace, sai wani kawunsu wanda shine ya jagoranci tafiyar, bayan an kawo musu ruwa da abinci sunci, nan kuma aka soma tattaunawa da shawarwarin yadda za'a gudanar da shiirin bikin, karshe dai aka tsaida rana wata biyu masu zuwa, a ranar Hanifah batayi bacci ba, taci burin auren Deen wanda shi take so, amma Khaleel yayi mata katanga da hakan, ranar tayi masa Allah ya isa tafi a kirga, sannan tasa kuka, bata rintsa ba har garin Alalh ya waye.


MSB✍🏼

No comments: