Friday 24 February 2017

KHALEEL Page 31&32

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻31&32✍🏻✍🏻


I dedicate this page to all members na Lovely fans❤️❤️❤️


Anty Hassana ce rik'e da ita har suka shigo d'aki, bayan y'an rakiyar amarya sun gama ganin gidan suka sanya alheri kowa ya kama gabansa. D'aki ya rage daga Anty Ikilima sai Anty Hassana suna ta faman lallashin Hanifah suna bata hak'uri, Anty Ikilima ce ta dafa kafad'arta tace.
"Hanifah kiyi hak'uri kada kanki yayi ciwo, kinsan kuwa rayuwar nan ba mattabata bace? Daga lokacin da aka d'aura miki aure aka bud'e miki shafin rubuta lada,  aljannarki na k'akashin tafin k'afar mijinki, yi nayi bari na bari shine zaman aure, kar ki zamo mai tsiwa, rashin biyayya da kuma gadara, manzon Allah (S.W.A) a cikin hadisinsa yace Ku fad'i alkhairi ko kuwa shiru, idan har kinsan bazaki fad'a masa maganar da zata faranta masa rai ba  to fa kiyi shiru" Gaba d'aya maganar Anty Ikilima sun soma gundurar Hanifah don haka da sauri ta d'ago tana dubanta tace
"Insha Allah Anty, nagode da shawarar da kika bani Allah ya saka da khairan"
Tayi murmushi tace
"Yauwa d'iyata, Allah ya baku zaman lafiya"
Anty Hassana ce ta mik'e tsaye tana fad'in
"Bari na d'auko mana abinci kinga har sha biyu ta wuce don ni ko karyawa ma banyi ba"
Haka suka zauna da Hanifah suna ta janta da fira sai da sukayi isha'i sannan sukayi sallama suka tafi.
Tana jinsa da abokanansa a palo suna ta fira harda k'yalk'yata dariya, ganin basuda niyyar kiranta tayi ta jin dad'i, dama itama baso take taje ba.

K'arfe sha daya saura har Hanifah tayi wankanta ta sa kayan bacci tabi lafiyar gado amma sam ta kasa bacci, can wurin k'arfe sha daya taji shigowarsa, gabanta yayi mummunan fad'uwa, tayi kwance lamo kamar mai bacci, ya kalle ta, fuskarsa babu alamun fushi haka ma babu alamun dariya yace
"Hanifah tashi ki dawo nan zanyi magana da ke" ya nuna mata kusa da inda yake zaune ma'ana bakin gado.
Ta taso ba musu sai dai fa fuskarta ba yabo ba fallasa ta zauna d'an nesa da shi, shi da yace zaiyi magana da ita maimakon ta kalle shi a'a, sai ta juya masa k'eya.
Wata tsawa ya daka mata, bata san yadda akayi ba sai dai ta ganta kusa da shi sai kyarma takeyi, kamar wata mai jin sanyi, duk jikinta gaba d'aya kyarma yakeyi, sai kuwa tasa kuka mai sauti, ba wai tsawar da yayi mata kad'ai yasa ta kuka ba illa dai ta tuna wai yau Khaleel ne mijinta, mutumin da ta dad'e tana ma kallon yayanta ciki d'aya, sannan bata sonsa ko kad'an, yau shine mijinta.
Haka ta d'auki tsawon lokaci tana kuka, ko uffan bai ce mata ba har sai da ta gaji  tayi shiru don kanta, jin tayi shiru ya sa yace.
"Har kin gama kukan?"
Ta d'ago tana kallonsa a ranta tace
"Wanann tambayar ta rainin wayau ce ko me?"
Tambayar ta matuk'ar 6ata mata rai.
"Ya kamata dai ki rage kukan da kike kar ki je ki ja ma kanki wani ciwo"
"Jikinka ko nawa?" Ta fad'a hankali, ta d'an ji tsoro don a tunaninta yaji amma abin mamaki sai taga yayi murmushi yace.
"Wallahi idan kina kukan nan jinsa nake har cikin raina, hankalina tashi yake gashi ni bana so kina yawan d'aga hankalinki nafiso ki samu nutsuwa da kwanciyar hankali"
"Ina naga samun nutsuwa da kwanciyar hankali zanyi tarayya da mugu"
Ta fad'a cikin ranta.
Ya dan runtse idanunsa yace
"Da ina iya hak'ura da ke Hanifah na rantse da Allah da tuni na hak'ura don ki samu farin ciki, amma duk da haka ina so ki sani bakiyi kuskuren aurena ba, don na miki alk'awarin nine zan saki farin ciki Hanifah, zan koyar da ke sona, zan baki jin dad'i da farin ciki, fatana Allah ya bani ikon cika alk'awarin dana d'auka"
Ya d'an yi shiru na y'an dak'ikai kafin ya cigaba.
"Hanifah naso ace kinsan irin d'imbin k'aunar da nake miki, tabbas son ki ya wahalar da ni a rayuwa ku duba fa kigani Hanifah tun kina jaririyarki cikin tsumma, sanda nafara ganinki a lokacin Allah ya d'ora min sonki, duk da lokacin ma bansan meye SO d'in ba, don haka ki kwantar fa hankalinki, ni nasan wacece ke, nasan me kike so da wanda bakya so.
Sai magana ta gaba, ina so ki sani ke k'anwata ce ta jini, sannan kiyi la'akkari da ni ba tsaranki bane na girmeki, na aure ki ne don ina sonki ba sadakarki aka bani ba"
Sannan yayi shiru na second biyar zuwa shidda, sannan ya d'ora.
"Bazan d'auki raini ba, sannan bazan yarda ki cigaba da azabtar min da zuciya ba kamar yadda kika saba ba". Sai kuma ya nuna kansa da yatsa
"Yanzu a gidana kike a matsayin matata dole ayi min biyayya, a kuma kyautata min saboda ina da iko kuma a k'arkashina kike.
Sannan ki sani doka ce nasa ba zancen kwana d'aki daban daban ko kiso ko kar kiso a d'akina ko dakinki zamu dinga kwana no matter what. Hanifah! And most importantly maganar girki, bana son mai aiki, ke da kanki zaki shiga ki dinga girka min, bana son k'azanta dole ki tashi ki tsaftace muhallinki. Sannan maganar hakk'inki na aure har abada bazan tilasta miki ba, har sai kin shirya...."
Nan da nan ta saki ajiyar zuciya tare da maida kanta k'asa, dama abinda take fatan ji daga gareshi kenan, wanda tasani cewa har abada kuwa bazata ta6a kai kanta gareshi ba, yama za'ayi hakan ta faru no never!!
Murmushinsa taji sai kuma yace
"Idan kina da abin cewa bismillah, idan kuma babu kiyi baccinki..."
Ko kallo bai ishe ta ba ta mik'e ta koma can k'arshen gado tayi kwanciyarta.

Toilet ya shiga, tana jin fitowarsa kamar ta make shi sai wani shafe yakeyi gaban madubi, da feshe feshen turaruka ya fesa kusan kala biyar, d'akin kuwa ya d'auki k'amshi mai dad'i. Ta d'an yi tsaki yadda ita kad'ai keji tace
"Ko wa zai burge da wani k'amshinsa? Ko da yake yana son k'amshi daman"
Ya rufe musu d'akin tare da kashe fitila, gabanta ya fad'i, tace a ranta
"Yau nice kwance gado d'aya da ya Khaleel?"
"Matso kusa dani Hanifah inji d'uminku"
Ya katse mata tunanin da takeyi.
Ta k'ara takure kanta wuri d'aya kamar mai bacci sai zare ido takeyi kamar tayi laifi, tana jinsa yana addu'ar bacci ya tofa musu addu'a, bifi minti biyu ba bacci yayi awon gaba dashi.
Ta saki wata uwar ajiyar zuciya, a yayinda wasu hawayen bak'in ciki suka biyo baya, ta d'ago kanta kad'an ta kalle shi a hankali tace
"Mugu kawai"
Daga nan batasan lokacin da bacci yayi awon gaba da ita ba.


*********

Da asuba Hanifah ta riga tashi, a hankali ta tura k'ofar ta fice don ma kar ya tashi, d'akinta ta koma tasa key gudun kar ya shigo, toilet ta fad'a ta d'auro alwalla sannan ta fito ta tada sallah, sai da gari ya d'an yi haske sannan ta tashi ta shiga tayi wanka, ta fito ta shafa mai tare da fesa turaren jiki kamar yadda ta saba, ta sanya wata atamfa maroon and ash ta fito tana dariyar mugunta, kitchen ta fad'a, a lokacin k'arfe bakwai da kwata, ta fera doya, tasan Khaleel baya son doya idan ba soyawa akayi ba, yasa ta dafa, bata soya ba kawai ta saka cikin warmers, kan dinning ta d'ora sannan ta dafa masa ruwan tea,  plate da cup kawai ta takwaso ta d'ora kan dinning d'in, ta kamalla a lokacin bakwai da minti hamsin da biyar.
Palo ta fito sai kuma taji tana sha'awar ganin gidan, sai kawai ta fito ta k'ofar kitchen, tsarin gidan yayi kyau don kuwa daga baya lambu ne ba kalar shukar kayan marmarin da babu, hakan ya k'ara k'awata wurin, ga tsuntsaye musamman geese da talo talo sai wasu guda biyu wanda bata sansu ba.
Ta ta6e baki tace "kilbibi kawai"
Ta fito gaban gidan, shima ya k'awatar sosai,  tsakar gidan nada girma sosai, don kuwa harda k'aton swimming pool da aka zagaye da grasses, gidan ma gaba d'aya grasses ne shimfi'de gwanin sha'awa, ga wasu kujerun hutawa nan guda biyu pink and blue da center table d'in rabin table d'in pink rabi blue. Tabbas idan akace wurin baiyi kyau ba anyi k'arya, daga gefen kujerun kuma irin rumfar nan ce zagayayya da akeyi da suminti, tsarin rumfar yayi kyau, can gefen swimming pool din kuwa swing ne (shillo) mai kamar kujera mai kyan gaske. Ta rik'e baki tana kallon gidan galala. Ga shukoki nan kala kala gaskiya gidan yayi kyau....
Sai kuma ta ta6e baki tace
"Wannan wurin dai baiyi kyau ba, kilbibi kawai, mtsw"
Ta fad'a tana k'are ma wurin kallo, wasu flowers ne suka d'auki hankalinta da akayi ma shapes kala kala.
"Yayi miki kyau halan?"
Ta jiyo da sauri tana k'are masa kallo....



MSB✍🏼

No comments: