Sunday 19 February 2017

KHALEEL Page 23&24

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻23&24✍🏻✍🏻


Ammi sai yamma ta dawo yadda tayi alkawari, a falo tayi kaci6us da Halisa tana dauke da kwanukan wanke wanke, tana ganin Ammi tayi saurin ajewa ta russina ta gaishe ta gami da yi mata sannu, Ammi ta amsa tana murmushi, sannan tace
"Ina mutan gidan? Naji gidan tsit"
Halisa tace
"Hanifah na dakinta, Khaleel kuma ya fita bayan sallar la'asar"
Tace
"To ga wannan a sanya fridge"
Halisa tace to tana mai amsar ledar daga hannun Ammi, sannan ta juya tayi kitchen.
Ammi ta nufi dakin Hanifah taji shi a rufe, ta kwankwasa, tazo ta bude, tana sanye da wata shirt ta polo pink color sai dogon wando baki wulik, ta matse gashin kanta daga tsakiya.
Ammi ta kalle ta tace
"Meye na rufe kofa da mukulli?"
Tace
"Haka nan"
Ammi tace
"To fito ki taya ni aiki, Gobe Halisa zata je ganin gida in ta tafi kuma dole ke zaki dinga taya ni, koma kiyi da kanki"
Tayi narai narai da idanu kamar zatayi kuka, tace
"Kai Ammi ni bana taya ki ne?"
Ammi ta galla mata harara tace
"Da yaushe kike taya ni? Kinga bana son dogon bayani muje kawai"
Ammi ta tasa ta gaba har kitchen tana cewa
"Idan ba Khaleel ba waye zai iya zama da ke, ga kuya ga shegen son jiki, bakida aiki sai kallo sai kuma karance karace litattafai, idan ma zaki gyara halinki tun wuri ki gyara kinji na gaya maki"
Ta rausaya da kai tace
"Kiyi hakuri Ammi"
Ammi tace
"Da anyi magana sai ki kwantar da kai kamar wata mutuniyar arziki, kina ma mutane kalar tausayi"
Tayi murmushi tace
"To Ammi kiyi hakuri dai"
Ta taimaka ma Ammi suka hada abincin dare mai rai da lafiya, suka jera kan dinning, sai zuba sauri take kar Khaleel ya dawo ya same ta a nan, dan halak din kuwa sai gashi kamar an jefo shi, ya shigo cikin takunshi na nutsuwa, ya shigo kitchen din.
Daga bakin kofa yaja ya tsaya yana kallonta kamar bai santa ba, sai kuma yayi gyaran murya yace
"Ammi me kuke dafa mana haka sai kamshi ke tashi a gidan, tun daga bakin kofa fa"
Tayi murmushi
"Duk naka ne Khaleel, nasan halinka da shiririta baka son ci abinci kwananan"
Yayi dariya kadan yana fadin
"Kin sangarta ni Ammi, kar fa na tafi inda banida gata inyi ta kewar ki..."
Tace
"Gashi kuwa Allah zai hada ka da makiwaciyar mata ya zakayi kenan?"
Ya dubi inda take tsaye, ta hade fuska kamar hadari sai wani hura hanci take.
Ya girgiza kansa yace
"Ya kuwa zanyi Ammi? A haka zanyi maneji (manage) ay, bahaushi yace da babu gwara"
Ta karasa masa
"Gara babu"
Hanifah bata tanka ba, ko inda yake bata kalla ba, ta kuma tsallake su zata wuce.
Ya sassauta murya, murya mai matukar sautin tausayi yace
"Kingani ko Ammi? Kingani zata koma daki ta kulle saboda aljaninta yazo"
Itama Ammi ranta babu dadi, tace
"Kar ka damu Khaleel, duk wani girman kan da takeyi zata aje shi ne tsab, kuma wallahi idan batayi a sannu ba sai na koya mata hankali"
Bai ce komai ba, ya shiga taya ta daukar coolers/warmers, har lokacin sallar magriba ta gabato, kai tsaye masallaci ya wuce don sauke farali.


*******

Bayan sallar isha'i Khaleel na tsakar tattara mahimman takardunsa da zai tafi dasu wurin daukar aiki gobe wayarsa ta fara ruri, ya dakatar da abinda yakeyi ya isa kan dressing mirror ya duba screen din wayar, ganin Saif yasa yayi murmushi gami da dagawa hade da yin sallama, Saif ya amsa yana dariya yace
"Yaya...!
Suka gaisa tare da tambayarsa karatu yace
"Alhamdulillah muna ta fama"
Khaleel yace
"Allah ya taimaka"
Yace
"Amin"
Saif ya gyara murya yace
"Yaya mutuniyar?"
Ya gane Hanifah yake nufi, Khaleel yace
"Alhamdulillah... "
Kamar ba Khaleel ba yadda muryarsa tayi kasa sosai, tabbas kowa da tasa kaddarar, in banda kaddara ma ace kamar Hanifah tana juya Khaleel son ranta?
Khaleel ya katse masa tunani yace
"Don Allah Saif a matsayinka na dan uwa na kuma kanina, na tabbata bazaka gaya min karya ba don inji dadi ba, kar ka 6oye min ka fito ga gaya min gaskiya tsakaninka da Allah, shin ina da wani aibu ko wani mummunar hali marar kyau ne da Hanifah ta kasa yarda ta so ni?"
Tausayin dan uwansa ya kama shi, yace
"Wallahi tallahi, kaji rantsuwar musulmi ko? Bakada ko daya daka lissafa min"
Saif ya runtse idanunsa tare da fito da sassanyar numfashi yace
"Ya Khaleel, shi So ba'a nan yake ba, kalli dai dan iskan yaron nan Deen da tace tana so, meya fika da shi? Amma tace tana sonsa, kawai dai Hanifah kanta na cikin duhu har yanzu, sannan tasan gaskiya take rufe ido ta take ta, wallahi yaya in banda kai ma da ka nace mata da nine kai da tuni na hakura da Hanifah, yarinya sai kace mai aljannu, haba!"
Ya karasa yana huci
Khaleel yayi murmushi mai sauti yace
"Kar ka damu Saif, yanzu idan har nace maka ina son wata mace a fadin duniyar nan, to nayi maka karya, Saif, So daban Kauna daban, ina kaunar Hanifah kuma zan cigaba har karshen rayuwata, ita wanda take ganin yana kaunar ta sonta yake hade da sha'awa, ta kasa ganewa, yanzu wahalarta mu kasance tare a matsayin ma'aurata, nidai a yanzu bazan tsaya ina lallashinta ba ta soni, ai sai ta raina ni"
Saif yayi dariya
"Ho! Ya khaleel! Son girma ko wane raini kuma tsakanin miji da mata?"
Khaleel yayi dariya, Saif ma dariyar yayi yace
"Kasan matsalar Hanifah? Batada nutsuwa, ma'ana taki nutsuwa ta fahimci ZAHIRIN KAUNAR da kake mata, ni na tabbata Hanifah tana sonka yaya, sai dai taki ta kwantar da hankalinta ta gane hakan, amma ina sa ran idan kukayi aure zata gane din, kasan mace da raini, sannan kasan halin mata basu iya nuna suna son namiji saboda sunanganin kamar zamu raina su, sunfi so namiji yafi nuna musu so fiye da yadda suke nunawa"
Khaleel yayi murmushi yana mamakin yadda akayi Saif yasan wadannan maganganun.
Haka sukayi sallama, zuciyar Khaleel babu dadi sam, ya ajiye wayar ya karasa hada takardunsa tsab.
Ya gama ya dan kishingida saman gado ya jawo wayarsa ya hau whatsapp, lambar Hanifah ya lalubo ya danna mata.
"Salam Beautiful"
A lokacin ta fito daga wanka tana taje gashinta taji shigowar message, ta dauka ta gane Khaleel ne sarai amma don ta kular da shi sai tayi masa reply da.
"Who is this please? Bansan mai number din ba"
Ya gyara kwanciyarsa yayi murmushi ya tura mata reply
"Kuma kina son sanin ko waye ko?"
Tace
"Yes of course mana!"
Da alama a kafule tayi masa reply din, yayi murmushi ya kai hannu cikin sumar gashinsa yana cakudewa, a yayinda numfashinsa ke harbawa da sauri sauri.
Ya dake ya kai hannu zaiyi reply amma sai yaji ya kasa, da kyar ya samu ya rubuta mata
"Ok"
Taga nema yake ya raina mata hankali sai ta kashe wayar gaba daya.

*****

Washe gari yayi wanka ya sanya wata orange  shirt mai ratsin baki, mai dogon hannu, da bakin bakin wando na jeans, ya taje sumarsa ta kwanta tayi luf luf, ya kammala shirinsa tsab, ya fito yana rataye da bakar jakar da mahimman takardunsa ke ciki, Ammi na palo, ya gaisheta, ta amsa tana murmushi, sun jima suna fira, daga karshe tayi masa fatan alkhairi da sa'a ya fito, motarsa ya tada, mai gadi ya bude masa gate ya fice.
Ammi tabi ta kofar dakin Hanifah, kamar kullum taji shi a rufe da mukulli, a zuciye ta shiga kwala mata kira.
"Amina! Ke Aminatu!!! Ki fito nan"
Tana budewa Ammi ta hau ta da masifa.
"Wai Hanifah wane irin hali ne da ke? Kashe kanki kike so kiyi? Ace mutum baida aiki sai zaman daki, gaba daya kin dena zama cikin mu ana firar arziki ina ma amfani?"
Bata amsa ba ta dai sunkuyar da kanta kasa
Ammai ta cigaba
"Ayi mutum sai shegen taurin kan tsiya da rashin tawwakali? So kike ki samu hawan jini haka kawai, me akayi miki? Yanzu ke Hanifah idan ma baki gode ma Allah ba,  bansan me zakiyi ba, ki dubi irin kaunar da Khaleel bawan Allah ke miki, ko wane irin wulakanci kikayi masa ya juri saboda yana sonki, duk wanda ya nuna yana son ka ay ya gama maka komai, to ki bude kunnenki da kyau kiji, auren da bakiso sai anyi shi, ko zaku mutu kuwa, in banda ma Khaleel din da ya nace ina zai kai halinki da bakar zuciyar nan taki, to idan kin ga dama ki gyara nidai na fita hakkinki"
Daga haka ta wuce ta barta nan tsaye, ta dade kafin ta koma daki ta haye gado ta fara kuka.
Khaleel yayi interview dinsa, sunce zasu neme shi idan lokaci yayi.
Bai tsaya ko ina ba, gida ya zarce yana cike da farin ciki.



MSB✍🏼