Saturday 18 February 2017

KHALEEL Page 21&22

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥


©PERFECT WRITERS FORUM
                (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻21&22✍🏻✍🏻


Washe gari koda Ammi ta kula da Hanifah tayi kuka sai kawai ta shareta ta cigaba da sabgoginta, zuwa yanzu abin nata ya zama rainin hankali, bayan sunyi kalaci da safe Ammi ta sauko cikin shiri da alama fita zatayi, Halisa ta iske a kitchen tana wanke cooker ta shaida mata zata je wata barka ta dora girkin rana, zata kai yamma bata dawo ba.
Haka ta sauko ko kula Hanifah batayi ba da ke zaune kan dinning tana hada tea, a bakin kofa ta hadu da Khaleel yana sanye da gajeren wando da riga marar hannu da alama jogging yaje, dama duk safiya ya kan fita yayi exercise, ya gaida Ammi yana murmushi yace
"Fita zakiyi Ammi?"
Tace
"Eh zan fita ne direba zai aje ni anjima zaizo ya daukeni"
Yace
"Ko na zo na kaiki?"
Tace
"A'a kayi zamanka Khaleel"
Yace
"To a dawo lafiya Ammi, dama nace zan siya ma Hanifah waya tunda waccan da na siya mata Saif ya ansa yana amfani da ita"
Ammi tayi shiru kamar mai tunani tace
"Anya Khaleel ka siya mata waya kuwa? Baka gudun ta koma tana waya da wannan tsohon saurayin nata?"
Yace
"Bazatayi ba Ammi, don zansa ido sosai insha Allah, gara a bata wayar saboda zama haka nan bai da dadi, don kinga yanzu ba makaranta take zuwa ba sannan kuma sai next year zata sake zana jamb ko"
Ammi ta girgiza kanta tace
"Shikenan amma don Allah kar kaje ka siyo mata irin masu tsadar nan wanda idan yaro yana rike irinsu sai ya dinga daukar kansa wata tsiya"
Khaleel yayi murmushi
"Insha Allah"
Daga haka sukayi sallama ta wuce mota shi kuma ya shige ciki, Hanifah na nan inda Ammi ta barta tana zaune kurum, ganin Khaleel zai wuce yasa ta hade rai tare da juya fuskarta gefe, murmushi yayi kawai ya wuce yana kallonta, kallon da yake mata ya sanya ta sakin tsaki mai kara har sai da Khaleel ya ji, ya juyo ya kalle ta sai bai nuna yaji ba sai ma yace mata
"Yan mata aje ayi wanka zamu fita"
Ta kalle shi tare da yi masa harara sannan tace
"Bazani ba"
Yana dariya yace
"Saboda me?"
Tace
"Bansani ba"
Yace
"To tunda baki sani ba kije ki shirya zamu fita"
Wannan karon sai baiyi dariya ba, ya daure fuska don ma kar ta dauki abin wasa.
Ta kalle shi haushi duk ya turnike ta tace
"Naji"
Yace
"Good girl"

Minti talatin ya shirya cikin wani dan karan yadi ruwan toka mai matukar santsi ta taushi, kamshi duk ya gauraye palon, tsaye yake bakin kofa hannunsa daya cikin aljihu, dayan kuma yana latsa wayarsa, ya gaji da jiranta hakan ya sa ya dawo saman kujera tare da kunne tv, ya sani sarai da gangan taki fitowa da wuri don dai yaji haushi, yayi dariya mai sauti yace
"Hanifah kenan"
Sai da ta kara 6ata akalla wata minti ashirin din sannan ta fito cikin doguwar hijabin da ta kusa kai mata kasa, kana hango dagon wando kalar baki ta kasan hijabin, fuskarta kuwa kamar an mata wahayi da gidan wuta, ko kallonsa batayi ba ta fice waje don bazata iya koda yi masa magana ba, girgiza kansa yayi tare da mikewa tsaye, ya kashe tv din da wutar gidan, sannan yasa key ya kulle gidan, sarai ta san ya hana ta zaman baya sheyasa ma ta bude gidan gaba ta zauna tana kallon taga, tana jin sadda ya bude kofar motar ya shigo amma bata ko kalle shi ba, shima kuma bai yi magana ba har ya murza key ya tada motar, sai da suka harba titi sannan ya kara gudu kadan.

 A tare suka jera cikin mall din, shima sai da yayi da gaske dan cewa tayi bazata shigo ba, kansa tsaye wurin saida electronics suka shiga, ita dai binsa kawai take da ido, wurin saida wayoyi taga sun tsaya, ya kalle ta yana murmushi yace
"Gimbiyata, gafa wayoyi nan ki za6i wadda tayi miki"
Ta daure fuska
"Wacece gimbiyarka?"
Yace
"Ke mana"
Ta harare shi tace
"Allah ya sauwake min na zama gimbiyarka"
Yayi dariya mai bayyana hakora yace
"To naji, ke gimbiyar wacece?"
Tace
"Ya Khaleel wai meye baka ne? Baka ganin cikin mutane muke?"
Yace
"Ina ruwana dasu, ni ke kadai nake gani"
Tayi tsaki
Yace
"Yanzu dai ki za6a da wuri idan ba haka ba zan cigaba da kiranki sunaye masu sanyaya zuciya"
Ta kalle shi tace
"Wai waye zai siya min waya?"
Yace
"Ina ruwanki? Kedai ki dauka mu tafi"
Tace
"Banso gaskiya"
Ya kyalkyale da dariya yace
"So kike idanu su dawo kanmu kenan?"
Tayi shiru cike da jin haushi, ta fara dubawa, can taci karo da wata waya fara kal mai suna HTC, ta nuna wayar, Khaleel yayi murmushi yasa aka ciro wayar yana dubawa a tsanake.
Ya kalleta yace
"Wannan tayi miki?"
Ta girgiza kanta a hankali.
Ya biya kudin wayar, har cover mai kyau ya siya mata, sannan ya biya ya siya mata kayan sawa, suka fito, basu dawo gida ba sai da ya tsaya ya siya mata layin MTN, sannan suka wuce gida, yana yin pakin ta fito da sauri tayi ciki, yayi murmushi bayan ya fito da ledar wayarta, yana zuwa ya iske ta bakin kofa tsaye, saboda mukullin gidan na hannunsa, yayi dariya ciki ciki, yana zuwa ya kalleta tare da sakar mata murmushi, ya bude gidan ya shige abinsa sannan tabi bayansa.
Dakinsa ya wuce ya jona mata charge, sannan ya shiga bayi don ya watsa ruwa.

Saida wayar ta cika sannan ya ciro harda charger din gaba daya, ya sanya mata lambar Ammi, data Saif, sannan ya sanya masa tata tare da saving sunansa don yasan ko ya sanya wani sunan chanja shi zatayi. Ya dauki tata sanann ya tura ma su Saif cewar wayar Hanifah ce.

Ya fito a lokacin tana kitchen tana dafa indomie, daga bakin kofa ya tsaya yana kallonta, sannan yayi sallama, ta amsa masa ciki ciki, ya matso dab da ita yace
"Ga wayarki nan"
Bata kalle shi ba tace
"Nagode"
Yaji dadin hakan, ya aje mata sannan ya fice, ta kura masa ido har ya 6ace sannan ta saki tsaki kadan tace.
"Zaka gane kurenka, wallahi sai ka gwammace dama baka sanni ba, sai kayi dana sanin aurena, na maka wanann alkwarin"
Ta karasa dafa indomie ta fito ta zauna kan dinning ta fara ci.
Wayar ta dauko tana juyawa tana murmushin da ita kadai tasan manufarsa.



MSB✍🏼

No comments: