Tuesday 21 February 2017

KHALEL Page 27&28

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


Na sadaukar da page dinnan ga masu kaunar novel dinnan, me love you all so much....!!! 😘


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻27&28✍🏻✍🏻



            BAYAN SATI D'AYA


A k'arshen sati aka turo ma Khaleel da takardar shaidar aikinsa, dama kuwa yafara k'ananan zane, kowa ya taya Khaleel murna, ya shiga office d'insa cike da d'imbin nasara, da fatan alkhairi daga bakin Ammi da sauran y'an uwansa da duk wani mai k'aunarsa.
Khaleel ya soma aikinsa cikin k'warewa da kuma himma.
Aikin da ya fara ya d'an samu sauk'i a zuciyarsa, at least dai yanzu ya rage ganin Hanifah, amma koda yaushe tana nan mak'ale acikin zuciyarsa, ko laptop d'insa wani makaken hotonta ne da tasha kyau har ta gaji, office d'insa gaba d'aya ya k'awata shi da hotunan SANYIN IDANIYARSA.



*******


Hanifah ta gama yanke shawarar tayi wayar k'arya don ta k'ular da Khaleel, tasan muddin yaji to fa dole ranshi ya sosu, dan haka sai ta fito palo, tasan weekend ne Khaleel d'in na gida, hakan ya sanya ta gama tsara yadda zata k'ular dashi.
Kujera ta samu ta zauna na tsawon minti biyu, ba alamun Khaleel, amma still ta k'udiri niyyar 6ata masa rai kamar yadda ya watsa mata miyau rannan!
Tana nan zaune taji alamun mutum, bata san ko waye ba amma ta tabbatar baya wuce Khaleel don zuwa wannan lokacin Ammi na d'akinta tana hutawa.
Sai kawai ta kara wayar a kunne tayi ta zuba zance, tana kashe murya tana soyayyar k'arya. Ba zato ba tsammani taji saukar mari a kuncinta, a razane ta k'wala ihu, fizgo ta Ammi tayi ta shiga tsula mata wayar tv ta ko ina a jikinta. Tana tsula mata tana cewa
"Yanzu Hanifah tarbiyar da na baki kenan? Da ubanwa kike waya? Na ce da uban wa kike waya?"
Cikin kuka Hanifah tace
"Wallahi babu kowa Ammi"
Ina Ammi bata ma tsaya sauraronta ba ta cigaba da tsula mata wayar nan a jikinta.

Khaleel na kwance yana wasu ayyuka a laptop d'insa bacci ya fara surarsa, can cikin bacci ya jiyo kuka da ihu, a razane ya m'ike a tunaninsa ma ko mafarki yakeyi, sai da ya ji muryar Hanifah, zumbur ya mik'ke ya fito da gudu ganin ko lafiya?
Yana fitowa yaga aika aikar da Ammi keyi wa abar sonsa, da sauri ya k'araso ya tsaye a gaban Ammi yana fad'in.
"Ammi dake ni a madadinta, kalla kiga na fita k'wari Ammi"
Ammi tayi dariya ba shiri tace
"Kauce ko na had'a da kai Khaleel"
Ya'ki kaucewa dole Ammi ta dakata tana huci.
Jikin Hanifah yayi rud'u rud'u, abinka ga farin mutum!
Khaleel da k'walla taf idonsa yace
"Ammi meyayi zafi haka? Me tayi miki kikayi mata irin wannan duka haka?"
Ammi tace
"Khaleel Hanifah bataji, na rasa yadda zanyi da ita ta nutsu, duk yadda mutum yake da ita sai ta so ta 6ata masa rai haba!"
Khaleel ya sassauta murya yace
"Don Allah me tayi miki haka Ammi?"
Nan Ammi ta zayyano mishi abinda taji da kunnenta Hanifah nayi, Khaleel yayi shiru jikinsa yayi sanyi k'alau! Yace
"Hanifah bani wayarki"
Ba musu ta mik'a masa wayar ya shiga dubawa, amma kaf baiga komai ba, duk da baya da tabbacin ko gogewa tayi, amma ya duba babu lambar namiji sai shi da Saif, k'arewa ma batada lambar ko wane mahaluk'i sai su kad'ai, ya kalli Ammi yace
"Ammi anya da wani take waya? Banga lambar kowa ba a wayar"
Ammi ta harare shi tace
"To sarkin tausayi, ka manta wacece Hanifah ne?"
Sai kuma ta karkata kanta zuwa inda Hanifah ke kwance tana kuka sosai tace mata
"Daga yau koda wasa na k'ara kama ki kina waya da koma waye jikinki ne zai gaya miki"
Daga haka ta mik'e ta nufi d'akinta.

Ta dakinnata ya ya lek'a, a lokacin Halisa ta cikawa Hanifah ruwan zafi a bath ta sanya, wani magani ta d'iga mata mai yaji, ta dawo tace mata.
"Jeki gasa jikin ki ko zaki ji d'ad'i"
Hanifah wadda har lokacin kuka take, ta mik'e ta nufi toilet, Halisa ta fiddo mata doguwar riga ta material marar nauyi.
Ta dad'e a kwamin ruwan zafi na ratsa jikinta yana kuma rage zogi da rad'ad'i, bayan ta gama ta bud'e ruwan ya tafi, sannan ta tara wasu ruwan zafi tayi wanka da sabulu ta fito. Ta shafa mai a duka jikinta sannan ta sanya rigar da Halisa ta aje mata.
Halisa ta murza mata mantheleta a k'afufunta da hannunta inda bulalar da Ammi tayi mata ta kwanta, Khaleel ya kuma lek'owa yana kallonsu, sai ta bashi dariya, ya koma baya yayi dariya mai isarsa sannan ya shigo yana kallon Hanifah wacce idonta kamar an zuba yaji ko tarugu a ciki, ya sark'e hannayensa guda biyu tare yace.
"Haka kawai kinsa Ammi ta zabgar min ke?"
Hararasa tayi sannan ta kawar da fuskarta gefe, ya kai dubansa inda Halisa ke shafa mata a dogayen yatsunta na hannu, inda shatin ya tashi sosai, ya toshe bakinsa da hannu kada dariyar da yake rik'ewa ta fito, yace
"Hanifah ta Khaleel, kina zaman zamanki kin jawo wa kanki shan bulala, wai ke nan kina waya da sabon saurayinki da wani hancinki kamar tumaturi"
Sai da Halisa tayi dariya sosai har tana duk'ewa.
Haka yayi ta tsokanarta bata ce komai ba, cikin ran Hanifah kuwa cewa take
~<<"Nima dai waya kaini yin wayar k'arya a palo? Nima dai nayi wauta">>~


*****

Ana sauran sati biyu bikin su Khaleel Saif ya diro Nigeria, hidima tasha kansu duk basu zauna ba, Ammi na ta fama da jama'a, y'an uwanta na kusa da nesa duk sun zo, dama wad'anda ba'a samu kai masu katin gayya ba ta waya tasa Khaleel ya rubuta musu, gida ya cika tun ba'a soma sha'anin bikin ba, ga y'ayan y'an uwan Hanifah da k'awayenta suma duk sun fara zuwa. Su Khaleel baki har kunne, kullum cikin fara'a yake.
Dama lefe Saif ya hado wanda Khaleel ya dinga tura masa kudi yana siya a hankali, akwati shidda da d'an kit ya kawo, Ammi sun yaba masa da k'ok'arin da yayi, d'inki kuwa Ammi ce ta d'auki nauyin yin komai, tayi nata, Saif dana amarya da ango, sannan Halisa ma kala biyu aka yi mata.

Tun ana saura sati d'aya a fara biki aka soma jere a can gwamna road, gida ne flat mai d'akuna uku, palo biyu, kitchen da dinning area, tabbas Ammi tayi k'ok'ari don gidan ba k'aramin kyau yayi ba.
Kwakwata Hanifah bata nuna wata alama ta 6acin rai ko kuma ana tursasa ta ba, domin Ammi tayi mata warning mai tsoratarwa akan ta saki jiki ayi bikinnan lafiya, ba tare da wani tashin hankali ba.

Ranar asabar d'in k'arshe ta February dubban  jama'a suka shida auren KHALEEL DA HANIFAH, akan sadaki dubu hamsin, daga nan ango da tawagarsa suka zarce da walimar da Saif ya had'a a gidan saukar bak'i, a can unguwar jabi road!




      Ranar Dinner....!!!




MSB✍🏼

No comments: