Tuesday 14 February 2017

KHALEEL page 15&16

🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀

           🎀🎀🎀🎀🎀🎀


🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀



 ®TALENTED WRITER'S GROUP(TWG)✍🏻


Dedicated to Cutie, Tafisuu, Xara bb, T.j auta, Faty Batagarawa, Sumy, Chuchu dear, Zainab Omar, Dainty, Ayusher, Zee bee, Xarah muhd, Suby and my pals Kiddies frnds forever one love ❤️😍❤️ {Ban manta da ku ba members na Hausa novels thanks for the love}😍😍😍

           
               🎀🎀🎀🎀🎀
                  *KHALEEL*
               🎀🎀🎀🎀🎀


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017💎


              PAGE


✍🏻✍🏻15&16✍🏻✍🏻


Kwakwasa kofar yayi hade da sallama, a razane ta mike zumbur gabanta na dukan tara tara, idanuwanta a waje alamar tsoro, tace
"Wa... waye?"
Yace
"Hanifa nine kizo ina son magana da ke"
Ta ce
"To" bayan ta kashe wayar da sauri ta dauko hijabinta da ta gama sallar isha'i ta fito, yana tsaye bakin kofar dakinta ya kalle ta yace
"Ina babban falo, ki zo ki same ni"
Bata tanka ba, sai ma harara da ta watsa masa bayan ya juya, sai da ya shiga falon tace
"Ko wace jarabar kuma zai kwaso min?"
Dakin Ammi ta fara shiga, bata dakin amma taji alamun watsa ruwa, hakan ya tabbatar mata da wanka take, sai kawai ta aje mata kan drawer ta kullo mata dakin ta wuce kiran Khaleel, sallama tayi ya amsa yana murmushi yace.
"Zo ki zauna mana"
Ba musu ta zauna dan nesa da shi. Ya numfasa yace
"Hanifah"
Bata amsa ba amma ta dago tana dubansa. Bai damu ba ya cigaba da magana.
"Akwai wani al'amari mai girma da bakisan dashi ba, ina ganin lokaci yayi da ya kamata ki sani"
Gabanta ya fadi uhm kawai tace
Yayi shiru ya rasa ta ina zai fara ma. Karfin hali yayi yace.
"Hanifah, a yadda kika dauke ni a matsayin yayanki ciki daya ba haka maganar take ba, ni ba Ammi ce haife ni ba, illa dai da mahaifinki da mahaifina sune suka fito a ciki daya"
A razane ta dago tana zubansa cikin rashin fahimta tace
"Ban...gane ba"
Yace "ma'ana dai ni cousin dinki ne, Hanifah ina so kisani ba tun yau ba nake miki son da bazaki ta6a iya sani ba, tun kina jaririyarki har kawo yanzu, don Allah Hanifah kar ki watsa min kasa a ido ki amshi kokon barata kar kice zaki juya min baya, kar ki kini zan iya rasa rayuwata"
Tunda ya fara magana take shatatar hawaye, jikinta har wani 6ari yakeyi, a hankali ta zamo daga kan kujera ta zube kasa tana cigaba da kuka, ganin haka yasa hankalin Khaleel ya tashi matuka, ba abinda yake ambato sai innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yace
"Nasan baki sona tun bakisan ainahin alakar mu da ke ba..."
Bata san lokacin da tace
"Dan Allah ya Khaleel ya isa haka! Kasheni kakeso kayi ne? Na roke ka kar kace zakayi min dole wallahi bana sonka, bana kaunar ka, nagode da fada min dangantakar mu da kayi, dama na dade ina ji a jikina akwai wani 6oyayen al'amarin da ba'a sanar da ni ba, ya Khaleel ina ganin girmanka to ka kama shi tun kafin ya zube kasa"
Da mamaki yake kallonta
"Hanifah yau ni kike fada ma magana haka? Menene laifina don nace ina sonki Hanifah?"
Bata tanka ba ta kara fashewa da kuka sosai.
Khaleel ya mike jikinsa yayi mugun sanyi yace
"Wallahi bazan ta6a miki dole ba Hanifah, zan baki lokaci kiyi shawara, idan kikace bakisona na miki alkawarin bazan tilaska ki ba, amma kisani bazan ta6a dena sonki ba"
Daga haka ya fice daga falon idanunsa sun kada sunyi ja! Dama abinda yake gudu kenan, gashi nan ya riga faru, ya yadda ya amince Hanifah bata kaunarsa, amma zai bata lokaci wata kila ta chanza ra'ayinta, ji yayi bazai iya tsayuwa ba, ya zauna gefen gado tare da dafe kansa dake sara masa, kirjinsa har wani bugawa yakeyi da sauri, duk yadda yaso daurewa, ya kasa, hannunsa yasa ya share hawayen fuskarsa yana jin wani irin radadi da daci a zuciyarsa, yau Hanifah ke fada masa magana son ranta?
Yafi minti goma zaune ya rasa meke masa dadi, karshe tashi yayi ya shiga ya watsa ruwa mai sanyin sosai, sannan ya dauro alwalla don baya jin zai iya bacci a wannan daren.

Hanifah kuwa da gudu ta shige dakin ta kullo, ta fada kan gado tana kuka sosai, duk da batasan meye so amma tanaji a jikinta babu wanda takeso a halin yanzu sama da Deen, ya riga ya sace zuciyarta lokaci guda!
Khaleel kuwa har gobe kallon dan uwa na jini take masa, amma babu ko digon soyayyarsa a zuciyarta, kwarai taso ta fada masa tana da wanda takeso amma bazata iya fada masa haka ba, ai ya zama cin fuska.
Haka ta kwana tana tunani kala kala.

Washe gari ta tashi da matsanancin ciwon kai, ga idanunta sun kumbura sunyi ja, koda Ammi ta tambayeta cewa tayi batayi bacci da wuri bane.
Suna kalaci Khaleel yaki fitowa, Ammi duk ta damu ta kalli Hanifah.
"Ina yayanki meyasa bai fito ba?"
Ta dan yamutsa fuska
"Wallahi bansani ba Ammi"
Ammi ta kalle ta tace
"Je ki kirashi"
Haushi ya turnike ta, ta mike a fusace tayi dakinnasa ta kwankwasa hade da sallama. Cikin wata irin murya yace
"Waye?"
Tace
"Hanifah ce kazo inji Ammi"
To kawai yace, ita kuma ta fice tana tsaki cikin ranta, mutum sai wani ji da kansa yake.
Sai da ya dauki tsawon minti uku sannan ya fito fuskarsa ba alamun annuri ko kadan, ya gaida Ammi, ta amsa tana mai kallonsa, kallo na kurilla tace
"Lafiya dai? Meyasame ka?"
Yace
"Bakomai Ammi, gani"
Tace
"Zo kayi kalaci"
Ya dan yamutsa fuska yace
"Bana jin yunwa"
Tace
"Me kaci da zakace bakajin yunwa?"
Yayi shiru
Tace
"Zo ka zauna nace"
Bai musa ba ya ja kujera yana fuskantar Hanifah ya zauna, ganin haka yasa ta mike, Ammi ta kalle ta
"Ina zakije?"
Tace
"Zan shiga wanka ne"
Ammi tace
"Ai baki gama ba"
Tace
"Na koshi ne"
Daga haka ta fice da sauri, Ammi da kanta ta zuba masa farfesun yan ciki da soyayyar doya. Da kyar yake hadewa, kamar yana cin madaci, duk akan idon Ammi, ta numfasa tace
"Khaleel"
Cikin wata dakusashiyar murya yace
"Na'am Ammi"
Tace
"Wai meke damunka?"
Ya kakalo murmushin dole yace
"Babu komai"
Tace
"Idan har baka fada min damuwarka ba, wa kake da shi da zaka fada masa?"
Yayi shiru
Tace
"Ina jinka"
Yace
"Da gaske Ammi babu komai"
Tayi murmushi
"Shikenan duk ranar da ka shirya ka sanar da ni ina jiranka"
Ta mike tana maganar zuci, tabbas tasan damuwarsa, kawai bazai fito fili ya fada ba, amma tana tausayin sa sosai.
Kasa cin abincin yayi, sai kawai ya hada ruwan tea ya koma dakinsa.



*******


Kullum da daddare sai Hanifah tayi waya da Deen a 6oye, tun Ammi na bata har ta fara hanata tace sai ta fadi mata wa take kira haka kullum, sai tayi karya tace ai yar ajinsu ce, ita dai Ammi tace ta gaji bata kara bata, gashi sun shaku sosai, Deen irin mazan ne da suka iya kalallame mace da kalaman soyayya,  da tilas budurwa sai ta nitse a kogin sonsa, Hanifah ta riga ta sallama masa zuciyarta.
Khaleel kuwa duk ya fita cikin hayyacinsa, tunanin yau daban na gobe daban, daka ganshi kasan yana cikin mawuyacin hali, shi kadai yasan meyake ji a cikin ransa.
Ammi kam abin ya ishe ta, hankalinta duk ya tashi ganin yadda Khaleel ya koma abin tausayi.

Ranar wata juma'a Ammi ta yanke shawarar samun Khaleel don ta nuna masa ta son damuwarsa, don bazata zuba ido tana ji yana ganin Khaleel dinta ya lalace a banza ba, bayan ga maganin matsalarsa nan cikin gida a kusa da shi.
Yana zaune falo ya kura ma katuwar tv din da ke makale a bangon falon ido, amma a zahiri sam hankalinsa baya wurin, Ammi tayi sallama a karo na uku, a lokacin yayi firgit ya dago yana dubanta bayan ya amsa tare da gyara zamansa. Zama tayi kan kujera, ganin haka yasa Khaleel ya zamo kasa ya zauna, tana kallonsa kallo mai cike da tausayawa tace.
"Khaleel"
Bai dago ba yace
"Na'am Ammi"
Tace
"Meke damunka? Kar kaso kaga yadda ka koma duk wanda ya kalle ka yasan ba lafiya ba"
Yayi shiru
Tace
"Ina jinka"
Yace
"Babu ko..."
Tace
"Kar kace min haka Khaleel, a matsayina na uwa na riga na fahimci matsalarka Khaleel, amma naga kamar baka dauke ni a matsayin mahaifiyarka ba..."
Khaleel ya dago a razane yace
"Ammi meyasa kika ce haka? Duk duniya banida mahaifiya sama da ke"
Tace
"Ban yarda ba inda ka dauke ni haka ai da ka fada min matsalarka"
Yayi shiru zuciyarsa ta raunana.
Tace
"Ni nasan Hanifah ce damuwarka Khaleel, ba tun yau ba na fahimci komai, bansan meyasa kake 6oye abinda ke cikin ranka ba, bakasan sai nafi kowa farin ciki idan hakan ta faru ba?"
Yayi murmushi kadan yace
"Nasani Ammi, amma don Allah kar kice zaki tilasta mata, nafiso ta amince da bakinta"
Ammi tayi tsai, can kuma ta numfasa tace
"Shikenan, ka nemi amincewarta ni kuma zan tsaya maka kai da fata har burinka ya cika insha Allah"
Yayi murmushi mai bayyana hakora. Koba komai ya dan samu sauki tunda Ammi ta bashi go ahead, kawai babbar matsalar yanzu Hanifah ta ina zai fara?
Har Ammi ta mike ta shiga ciki bai sani ba, don ya kara tsunduma cikin kogin tunani.


Saif sun shiga hutu don haka gida ya taho don ya jima rabonsa da gida, kowa yayi murna da ganinsa.
A cikin kwana biyu ya fahimci yadda Hanifah kema Khaleel, kuma ko kadan baiji dadi ba, amma yayi alkawarin shawo kan matsalar kafin ya koma.


*******


Yau ma kamar kullum bayan Hanifah tayi shirin islamiyya, ta leka tace ma Ammi ta tafi, tayi mata nasiha da addu'a kamar yadda ta saba, ta fito a falo tayi kaci6us da Khaleel yana shirin shiga ciki, ko kallonsa batayi ba ta fice, har cikin ransa bai ji dadi ba, wannan irin tsana haka?

Kamar kullum yayi fakin motarsa inda ya saba fakin yana jiranta, minti ashirin ta iso tana murmushi, ya kalle ta yana sosa sumar gefen bakinsa yace.
"Princess sai yanzu?"
Ta karaso tana kallonsa tace
"Sorry Deen wallahi na tsaya biya karatu ne"
Yace
"Its ok, zo ki zauna" ya nuna mata gefen kujerar motar, ba musu ta zagaya ta bude, nan hira ta 6arke tsakaninsu, Hanifah ta gama yadda da Deen, ta aminta da shi, shima din wani irin shu'umin murmushi yayi ya karkato da fuskarsa yana kallonta.
A hankali ya kamo hannuwanta cikin nasa yana murzawa, ta kasa hanasa duk da batason abinda yake mata amma gaba daya ta kasa kwakwaran motsi. Lumshe idanunta tayi kafin ta bude, ya shafi gefen fuskarta yace
"I love you Hanifah"
Tana shirin yin magana ta hango Saif wanda tsananin razana yasa ta kasa motsi, sai na shiga uku take kira, Deen yace
"Mekika gani haka da kika rude lokaci daya?"
Bata iya bashi amsa saboda tsananin rudanain da ta shiga ya sa ta rushewa da kuka, yadda Saif ya taho kamar kura taga nama, haka ya karaso yana huci ya bude inda Hanifah ke zaune tare da finciko ta, wata irin razananiyar kara ta fasa da tasa Deen ya rude.
"Dama wannan dan iskan ke hure miki kunne? Islamiyar kenan Hanifah?"
Kuka take sosai tana bashi hakuri. Ya juya yana kallon Deen da yake zaune babu alamun damuwa a tattare da shi, Saif cikin zafin nama ya finciko Deen.
"Dama kaine dan iskan da ke hure mata kunne?"
Ya dago hannu ya wanke Deen da mari, ya kara masa daya a 6angaren hagu, sannan ya soma naushinsa ta ko ina. Yana bugunsa yana masifa.
"Kai har ka isa Ammi ta dauki tsawon shekaru ba iyaka tana gina tarbiyyar diyarta, rana daya kace zaka rusa shi?"
Wani naushi ya kai masa da sai da bakinsa ya zudda jini, ga unguwar ba mutane sosai bare wani ya kawo dauki.
Sai da yayi masa jina jina a fuska, sannan ya finciko Hanifah dake kukan fitar rai yayi gida da ita.



MSB✍🏼

1 comment:

Zainab Adamu Garba said...

Momcyna kina kokari Allah ya qara basira wlh inajin dadin novel din.