Monday 13 February 2017

KHALEEL Page 13&14

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€



This page is for you Aunty Yar Mitsia and Kdey❤️😍❤️one loveπŸ’ž



 ®TALENTED WRITER'S GROUP(TWG)✍🏻

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻13&14&✍🏻✍🏻


Saif yace
"Babban yaya yadai?"
Khaleel yayi dariya yace
"Meka gani ne?"
Saif yace
"Babu komai"
Daga haka bai kara ce masa komai ba, haka kuma Khaleel ya basar da zancen, aka cigaba da sabgar graduation.
Hanifah kuwa tunda tayi sababbin kawaye larabawa bata kara bi ta kansu ba.


******

Washe gari da misalin karfe tara da rabi na safe Khaleel yayi wanka ya shirya cikin bakin jeans da riga ruwan toka mai ratsin fari, ya fesa turare ya fito falon, Ammi da Saif  suna kan dinning suna kalaci, amma babu Hanifah a cikinsu, ya gaida Ammi yaja kujera gefenta ya zauna, flask ya jawo ya zuba ruwan tea, Ammi da kanta ta zuba masa plantain da dankali da soyayyen kwai, tana shirin zuba masa madara a shayin yace.
"Ammi don Allah ki bari na sa da kaina, wannan abubuwan fa mu ya kamata mu dinga yi muku shi"
Tayi murmushi
"Kar ka damu Khaleel, kome uwa tayi wa danta bata fadi ba"
Zata cigaba ya hanata
"Nidai dan Allah Ammi ki bari, wallahi kunya nakeji idan kina sa min"
Tayi murmushi kurum, ta zauna tana kallon dannanta. Ya juya da zagaye kwayar idonsa farare tas yabi table din da kallo, yana kallon Saif yace.
"Saif ina Hanifah?"
Yace
"Assignment takeyi a cikin dakinta"
Yace
"Saboda Assignment sai takiyin breakfast?"
Saif yayi murmushi kawai
"Ina zuwa"
Khaleel yace yana kokarin mikewa tsaye, babu wanda ya tanka masa sun dai bishi da ido. Ya doshi dakinta. Gaba daya kallon tausayi suka bishi da shi don zuwa yanzu sun fahimci abinda yake kokarin 6oyewa ya soma fitowa fili, Ammi har cikin ranta tausayin Khaleel takeji, ya akayi ya bari zuciyarsa ta kamu da son wannan kafaffiyar yarinyar da bata son ciwon kanta ba?"

Zaune take kan study table da katon dictionary, sai wasu manyan text books guda uku a gefe, ta bude daya tana rubutu bisa dogon exercise book, tana ta rubutu. A bakin kofa yaja ya tsaya yana kallonta, ko wane motsinta akan idonsa, bata ma san da mutum a nan ba, bazai iya cewa ga iya adadin lokutan da ya dauka a nan ba, kila jikinta ne ya bata ana kallonta, a hankali ta dago ta dube shi, bata ce uffan ba ta maida kanta kasa ta cigaba da abinda takeyi.
"Sorry... Na katse miki abinda kikeyi ko? Ki ajiye wannan aikin sai kinyi breakfast tukunna"
Ta yamutsa fuska ba tare data kalle shi ba tace
"Na koshi"
Bai ce komai ba yaja kujera kusa da ita ya zauna yace
"Shikenan nima bazan ci ba, kawo in taya ki"
Tayi banza dashi ta cigaba da abinda takeyi.
Ya numfasa yana kallonta a nutse yace
"Ki kawo na taya ki nace"
Wannan karon bata musa ba ta mika masa, aikuwa sai ya hada gaba daya ya rufe ya aje gefe, yana kallonta sosai a yayin da ta kawar da tata fuskar gefe.
"Oya ki tashi ki karya ba kyau mutum yana zama da yunwa"
Yayi maganar duniyar nan amma taki dagowa bare ma yasa ran zata kalle shi, ga ta turnike fuska kiris take jira tayi kuka, ransa yayi matukar 6aci, duk duniya babu mai yi mashi wulakancin da Hanifah ke masa, baisan lokacin da ya fizgo hannunta yana kokarin jawo ta daga kan kujerar.
"Zaka karya ni fa"
Yace
"Ai gara na karya ki in huta da wannan wulakancin da kikeyi min, Hanifah nifa yayanki ne, jininki, ko Saif dana girmeshi bakiyi masa wulakancin da kikeyi min, why Hanifah?"
Batasan lokacin da tace
"Kai yaya takura min kake, gaka mugu..."
Tayi saurin yin shiru tare da sa hannunta ta rufe idanuwanta tana jiran saukar bugu.
Murmushi yayi da yafi kuka ciwo yace
"Hanifah duk abuwan da kika ga ina yi miki is for your own good, taimakon rayuwarki nakeyi..."
Cikin muryar kuka tace
"Nidai ka sake ni"
Ya sake ta ba musu tare da fita daga dakin.
Allah sarki so! Dawowa yayi dauke da tray din kalacin ya aje mata har bisa table dinta hade da tsugunnawa gabanta, kukan da takeyi shi ya fi komai daga masa hankali, cikin murya mai rauni yace.
"Kisha ba don ni ba, kuma ba don na isa nasa ki din ba, kiyi hakuri kisha kinji yar kanwa ta?"
Ta dago ta dube shi duk sai ya bata tausayi kuma, wai ita me ke damunta ne? Meyasa kike wulakanta yayanki? Jininki ne fa, uwa daya uba daya ai ya wuce wasa. Wani 6angare na zuciyarta ya ce da ita.
Sai kawai ta mika hannu ta dauki cup din ta kai bakinta.
Ganin haka yasa ya mike ya fita zuciyarsa cike da tunani kala kala.

Wai sai yaushe zaka sanar da ita cewar bafa iyaye daya suka jefo ku duniya ba. Kara gyara kwanciyarsa yayi tare da juyawa gefe guda yana tunani mai yawa.
Sallamar Saif ce ta katse masa tunaninsa. Ya tako a hankali ya zauna kusa dashi yace.
"Yaya wata magana nazo muyi da kai idan bazaka damu ba"
Ba musu Khaleel ya mike zaune daga kwanciyar da yayi, ya janyo filo daya ya rungume yace
"Ina jinka Saif"
Saif ya gyara zama ya soma magana cike da damuwa.
"Yaya, kwana biyu naga kamar kana cikin damuwa, ya kamata ka sanar da ni koda akwai shawarar da zan iya baka"
Khaleel yayi shiru kawai. Saif ya numfasa yace
"Dana so nasa maka ido yaya, amma gaskiya naga hakan bamai yiwuwa bane, na san menene damuwar ka ba tun yau ba kallonka kawai nakeyi...!"
A razane Khaleel ya ce
"Ya...ya akayi kasani?"
Saif yayi murmushi
"Yaya kenan, ai sirrin da kake 6oyewa ne ya soma fitowa fili, soyayya ce mai matukar wahala take wahalar da ke, soyayyar wacce batasan kanayi ba, soyayyar yar uwarka kuma jininka HANIFAH....!"
Sunan har cikin kwalwarsa haka yaji shi, ya runtse idanunsa gam yana mamakin yadda akayi Saif har ya gano haka da wuri.
Saif ya cigaba da magana
"Yaya ya kamata tun wuri ka fito fili ka sanar da ita, idan ba haka ba nan gaba zakayi dana sani, a bari ya wuce shike sa da rabon wani..."
Khaleel ya katse shi
"Saif bana kin bin shawarka bane, a'a kai kasan halin Hanifah wata irin yarinya ce, yanzu ma bakaga irin tsanar da tayi min ba inaga idan na furta mata kalmar so, inajin tsoron rasa ta, idan na rasa Hanifah kamar na rasa rayuwata ne, besides yarinayar nan har yanzu batsan matsayina ba a wurinta"
Saif yace
"Haka ne, amma dai yaya kayi kokari ganin ka sanar da ita kota wane hali ne, ina guje maka gaba ne, saboda idan ka bari tayi maka nisa har abada bazaka iya kamo ta ba, amma yanzu da take kusa da kai ya kamata kasan me kuke ciki"
Khaleel ya girgiza kansa alamun gamsuwa da shawarar Saif.


******


Kwanansu biyar a Dubai suka dawo Nigeria, tun dawowarsu Hanifah bata kara bari sun hadu ba, shima bai matsa ba, amma ya kudiri a ransa cewar kota halin yaya ne zai sanar da ita matsayinsa a gareta, sannan ya fada mata irin dinbin kaunar da yake mata.

******

Karfe hudu da minti sha biyar ta fito sanye da kayan islamiya kalar toka, hijabin har kasa, sai jakar litattafanta da ta rataya a kafada, sauri takeyi kasancewar zata bada hadda a yau din, har ta kusa kaiwa wata mota kirar honda baka wulik, ta faka ta gabanta, hakan ya tsaida ta daga tafiyar da takeyi, cike da jin haushi ta bude baki zata fara masifa, aka bude kofar motar, matashin saurayi ne da bazai haura shekara asharin da hudu zuwa da biyar ba, ba fari bane, kalarshi chocolate color, yana da tsayi sosai, haka ma siriri ne sosai. Sanye yake da kananan kaya bakin wando da farar t shirt marar hannu.
Takowa yayi dab da ita yana fadin.
"Yan mata islamiyya za'a je haka?"
Tayi tsaki kadan tace
"Waye kai da zakazo ka wani sha gabana haka?"
Yayi dariya yana sosa sumar gashin kansa yace.
"Wani bawan Allah ne, dan Allah idan bazaki damu ba ara min lokacinki minti daya yayi yawa"
Tayi shiru alamun tunani, can kuma ta numfasa tace
"Yi sauri saboda na riga na makara"
Yayi dariya yace
"Nagode sosai Beauty"
Suka tsaya daga jikin motar yace
"Wallahi na jima ina ganinki kullum idan zaki wuce ta nan hanyar, wato idan zakije islamiyya, alfarma nake nema wurinki"
Ta dan zaro ido tace
"Ta me fa?"
Yace
"Yauwa, kamar yadda na fada miki nasha haduwa da ke ta nan hanyar, na juma da kamuwa da sonki, kuma komai sai dana gano game da ke tukunna kikaga na miki magana"
Tace
"Kamar yaya?"
Yace
"Ma'ana nasan gidanku da makantar da kike zuwa"
Ta dan saki fuska kadan tace
"Gaskiya ni yanzu bana soyayya har sai na kammala karatuna tukunna"
Yayi murmushi yana mata wani irin mayen kallo yace
"Naji baki soyayya, amma ya kamata ki fada min idan na samu kar6uwa yadda hankalina zai kwanta"
Tadan yi shiru tana kare masa kallo batace komai ba
Yace
"Wannan kallon ya tabbatar min da cewar na samu shiga kenan?"
Tayi murmushi a lokacin da ta gyada kanta alamun eh.
Wani irin tsalle yayi yace
"Yes!"
Ta kalle shi shekeke tana mamaki
Yayi dariya yace
"Nagode sosai ko zan samu number wayarki?"
Tace
"Kayi hakuri banida waya a halin yanzu, amma kana iya bani taka duk sadda na tashi zan kiraka"
Littafin makarantarta ta ta ciro daga jaka da biro ta mika masa, ya rubuta mata number din sannan yace
"Ina jiran kiranki"
To kawai tace tare da wucewa tayi hanyar makaranta, yayi saurin kiranta, juyowa kawai tayi.
Yace
"Baki fada min sunanki ba princess"
Tayi murmushi
"Sunana Aminatu, but you can call Hanifah"
Yace
"Nice name, ni sunana Zaharadeen, amma zaki iya kirani da Deen"
Tayi murmushi tace
"Ok Deen"
Daga haka ta wuce da sauri zuciyarta cike da tunani kala kala!
Kallonta yake har ta 6ace kafin yayi murmushin da shi kadai yasan ma'anarsa, sannan ya bude motarsa ya tafi.

Da daddare haka Hanifah tayi ta saka da warwarewa, ta yarda ta amince tana son Deen, sai kace wanda yayi mata asiri cikin rana daya har ta amince da shi ba tare da tasan ko wanene ba....?
Ta yanke shawarar aro wayar Ammi ta kirashi.
Ammi ma zaune tana zaune tana lazumi ta shiga da sallama, bayan ta gaishe ta tace
"Ammi dan Allah ara min wayarki zan kira wata yar ajinmu"
Ba tare da tunanin komai ba ta mika mata wayar.
Ta koma dakinta ta 6oye number din tare da kira, bugu biyu aka dauka.
Tace
"Hello?"
Daga kwance yace zumbur ya mike yace
"Hanifah kece?"
Tace
"Nice, Deen ne?"
Yace
"Nine my princess ya kike?"
Ta lumshe idanu tace
"Lafiya lau"
Yace
"Naji dadin kirana da kikayi, amma meyasa kika 6oye lambar?"
Tace
"Wayar mamana ce na ara zan dinga kiranka kafin a siya min wayata"
Yace
"Ok my princess menene labari?


Khaleel ne kwance a dakinsa ya kasa sukuni, tunanin Hanifah ya ishe shi, hakan yasa ya mike bayan ya yanke shawarar sanar da ita abinda ke zuciyarsa game da ita.
Jallabiyarsa doguwa ya zura ya fito da dakin.


(Sorry pls akwai inda nace Khaleel is 29 is a mistake he's 22 years😊)


MSB✍🏼

No comments: