Thursday 16 February 2017

KHALEEL Page 17&18

🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀

           🎀🎀🎀🎀🎀🎀


🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️
   ♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀♥️🌀




 ®TALENTED WRITER'S GROUP(TWG)✍🏻
©PERFECT WRITERS FORUM (P.W.F)❤️

           
               🎀🎀🎀🎀🎀
                  *KHALEEL*
               🎀🎀🎀🎀🎀


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


This page is dedicated to all my fans, nagode da kaunar book dinnan da kukeyi much love 😍❤️


 February 2017💎


              PAGE


✍🏻✍🏻17&18✍🏻✍🏻


Hanifah tana kuka tana ba Saif hakuri, amma ina bai ma san tanayi ba, don ya riga yayi mugun fushi, Saif nada hakuri amma idan ransa ya 6aci ba kyau.
Kwarai tayi dana sanin abinda Deen yayi mata,
Sai dai ko kadan bataji ta tsane sa ba, tun daga bakin kofa kukan Hanifah ya karu, tana tsoron haduwarta da Ammi, tasan idan taji kashinta ya bushe. Da Khaleel suka fara cin karo ya fito da alama fita yake shirin yi, ganin haka ya rude yana tambayar abinda ya sami Hanifah haka, cikin fushi Saif yace.
"Bar yar iskar nan mana..."
"Subhanalillah! Haba Saif dena ce mata yar iska mana"
Cewar Khaleel a dan rude.
Saif yana huci yace
"Bakasan me tayi bane ba da baka ce komai ba..."
"Me tayi haka Saif? Meyafaru?"
Cewar Ammi tana karasowa a rude.
Saif ya soma basu labarin abinda ya ga Deen nayi mata a mota, salati Ammi tasa tana tafa hannuwanta, a yayinda da Khaleel yayi mutuwar tsaye, ga wani irin mugun kishi da yaji yana taso masa lokaci guda, kasa tsayuwa yayi ya koma baya ya zube kan kujera dafe da kai.
Saif na shirin kai ma Hanifah bugu da wayar
Cd Ammi tayi saurin hana sa, itama kanta ranta yayi mugun 6aci. Tace
"Kar kayi saurin bugunta Saif, ka barni da ita kawai idan tasan wata ai batasan wata ba"
Hanifah cikin murya kuka tace
"Kiyi hakuri Ammi na tuba bazan sake ba..."
Ammi ta doke mata baki tace
"Taso ki biyo ni"
Ta mike da kyar tana shasheka tana share hawayen fuskarta tabi bayan Ammi, kan kujera Ammi ta zauna, Hanifah da Saif suka zauna kasa. Khaleel ma a hankali ya zamo kasa ya kasa koda kwakwaran motsi.
Ammi ta numfasa tace
"Hanifah"
Ta dago da jajayen idanunta tace
"Na'am"
Ammi ta cigaba
"Keda waye Saif ya gani a mota?"
Tayi shiru
Ammi ta daka mata tsawa
"Nace waye?!"
Tace
"Deen sunansa, ya...yace yana so...na"
Da mamaki Ammi tace
"Saurayinki ne kenan?"
Bako kunya ta gyada kai a hankali tana zubda ruwan hawaye.
Khaleel ji yake kamar kirjinsa zai huje tsabar kishi, lallai Hanifah bata kaunata. Ya fada cikin ransa.
Ammi tace
"To kinyi daidai, amma idan kina tunanin auren wancan dan iskan bada yawu na ba, kin ta6a ganin saurayin arziki yana ta6a budurwarsa ba tare da an daura aure ba, wallahi dama da kinga irin haka to ba don Allah suke son mutum ba, yanzu ba islamiyya muka tura ki ba ? Dama ba zuwa kike ba Hanifah?"
Tayi shiru
"Kinsan Allah tun wuri dama ki fidda shi daga cikin ranki, don na yanke shawarar aura miki da uwanki dana yarda da shi Khaleel, zan fi samu kwanciyar hankali da nutsuwa idan shi ya aure ki, dama an dade ana 6oye miki kuma Saif ya sanar dani cewar shi da kansa Khaleel ya sanar da ke dangantar ku, to kinji kisa a ranki bakida miji sama da Khaleel..."
"Don Allah Ammi kar ki...." Cewar Khaleel
Ammi ta daga masa hannu
"Bana son jin komai daga gareka Khaleel, na riga na yanke hukunci kuma banida niyyar janyewa"
Daga haka ta mike tayi ciki, Hanifah kuka take na fitar rai, kafin ta tashi tayi dakinta da gudu tana kuka sosai.
Saif kuwa wani murmushin farin ciki yayi a yayinda Khaleel ya dafe kai, yana jin wani iri. Saif ya dafa shi, ya dago da idanunsa da suka kada sukayi ja. Saif yace
"Kar ka karaya yaya..."
Khaleel yace
"Ban karaya ba Saif, duk abinda Hanifah keyi yarinta ke dibar ta, nan gaba ko ance tayi bazatayi ba, amma kasan Allah banso Ammi ta yanke wannan hukunci ba haka da sauri ba"
Saif yayi murmushi
"Nikam na so hakan kuma naji dadi"
Khaleel yace
"Kayya Saif, Hanifah bata sona ko kadan"
Saif yayi murmushinsa mai kyau yace
"Zataso ka ne nan gaba, bakiji bature na cewa time heels ba?"
Khaleel yace
"Haka ne, Allah ya za6a mana abinda yafi alkhairi"
Saif yace
"Ko kaifa yaya, haka ya kamata kace, yaushe zaka tafi masters?"
Ya gyara zama yace
"Ina sa ran nan da sati biyu insha Allah"
Saif yace
"Allah ya kaimu"
Yace
"Amin"
Tare suka mike suka fice daga gidan gaba daya.



*******


A karshen wata takardar admission nashi ta kuma fitowa ta cikin email suka aiko mashi, inda yayi applying ya samu kuma, kuma a lokacin, kowa ya taya Khaleel murna banda Hanifah da ko digon farin ciki babu a digon farin ciki a cikin ranta, Shima kuma ya share ta saboda baya so yana yawan matsa mata, ya dan bata space.
Khaleel ya soma karatunsa cikin kwanciyar hankali.
Ita kuwa Hanifah tuni ta maida hankali kan karatunta kasancewar sun kusa fara zana jarabawarsu ta karshe, tun faruwar wannan abu bata kara ganin Deen ba, abin yana damunta sosai, ga koda wasa Ammi ta dena bata wayarta ba halin kuma ta kirashi taji ko lafiya.
Sannan yanzu ko Khaleel ya kira Ammi bai cika tambayar Hanifah ba kamar da, kuma bai cewa a bashi ita su gaisa, sai dai kawai yace a gaishe ta, banda haka ma abubuwa sun mashi yawa, karatu yakeyi bana wasa ba, ya kyaleta har lokacin da yake ganin ta mallaki hankalin kanta, itama ta soma fahimtar cewa Khaleel din ya share ta ba kadan ba, kenan yana nufin fushi yakeyi da ita?


*******



SOME TIME LATER! (Bayan wani lokaci)


A cikin jerinn masu saukowa daga matattakalar jirgi ciki harda Architect Khaleel  Usman, sanye yake da jibgegiyar dark blue din coat har gwiwa, idanunsa cikin bakin space, ya sanya dogon wando baki, saukarsu kenan a airpot din Ireland inda a yawancin passengers din a nan zasu sauka, sannan kuma a sake lodi masu tashi zuwa Nigeria.
Khaleel bai sanar da kowa zaizo ba.

Ammi na kicin itada Halisa suna fama da girki suka jiyo muryar mai gadi yana ma Khaleel sannu da zuwa. Da sauri ta fito adaidai lokacin da Yusuf mai gadi yake aje manyan manyan jikuna da Khaleel din yazo dasu
Yar mulkin na kwance a falo kan kujera da littafi a hannunta, wani irin sanyin kamshi da mutum daya tasani dashi a duniya, turarensa da yake so, a lokacin ya russuna daidai saitinta ya zare littafin.
Ta dago tana kare masa kallo da idanuwanta da suka kawo ruwa, don a ganinta mai takurawa rayuwarta ya dawo, shi kuwa murmushi yayi yadda Hanifah ta kara girma, ta kara kyau, Tsawo, da gogewa a tsayin watanni goma da yayi bai ganta ba, baiji muryarta ba.
Ammi ta shigo tana kallonsu, basu san ta shigo ba sai kawai ta koma kicin tana hamdallah, bata ta6a ganin miji da macen da suka dace da juna ba irin KHALEEL da HANIFAH ba, gashi dai kamar su daya haske kawai ya dan fita, Hanifah ce ta fara kauda tata fuskar sannan ta hade fuska kamar bata ta6a dariya ba ko sannu da zuwa da take mishi da, yau bai samu ba, karshe ma mikewa tayi ta bar masa falon.
Yayi dariya ganin yadda take hade rai kiris take jira ta fashe.






MSB✍🏼

No comments: