Thursday 23 February 2017

KHALEEL 29&30

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️


Wannan page d'in naku ne members na PWF, babu abinda zance muku sai dai nace Allah ya saka muku da alkhairi akan yadda kuke bada had'in kai don cigabanmu tare da taimakon juna, Allah ubangiji ya k'ara muku basira da zak'in hannu, i love you all so much❣πŸ’™❣


           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻29&30✍🏻✍🏻


K'arfe bakwai da kusan rabi aka shirya amarya cikin wani d'an ubansu fari da blue d'in bridal gown, sai dai bisa tarbiya ta Ammi baka cewa rigar amare ce, don kuwa ta rufe mata jikinta ruf, babu inda wani 6angare na jikinta ya bayyana irin na y'an matan zamani yadda zakaga an d'inka riga amma duk jiki a waje kamar ba y'ay'an musulmai ba, Allah dai ya shirye mu baki d'aya.
Ba'ayi mata wata kwalliya mai yawa ba, don Hanifah ba mai son kwalliya bace bata son wannan shafe shafen da ake yayi, aka d'auko mayafi aka lullu6e mata jikinta da shi kalar kayanta, y'an uwa da abokananta ma anko suka sanya kalar brown and cream, a lokacin da aka fiddo amarya an gama mata kwalliya kowa ya yaba kamar ba Hanifah ba.
Sai kusan takwas da rabi motocin d'iban mutane zuwa wurin dinner suka iso.
Khaleel na waje ya gama shirinsa cikin blue d'in shadda wadda ta yi masa kyau ba kad'an ba, kayan sun d'an kama shi haka ya k'ara fito k'arfi had'e da kumarinsa ta ko ina.
A yayin da Saif ke sanye cikin farar shadda sabuwa dal, cikin wad'anda Ammi ta d'inka masa.
Duk jama'ar wurin mutane ne daga garuruwa daban daban, inda yayi karatu ko yake da abokai da sauransu.
Wata daga cikin cousin d'in su Hanifah mai suna Surayya ta fito waje inda Khaleel da tawagarsa ke tsaye suna fira cike da nishad'i, gaishe su tayi tace.
"Ya Saif an gama shiri fa, mu taho a fara tafiya ne?"
Khaleel ya kalle ta yace
"Ina amaryar?"
Tayi murmushi tace
"Tana ciki itama an gama shirya ta"
Saif yace
"Ok ku fito na tafi da wasu a motata, sauran kuma wad'anda basu samu wuri ba, ga motaocin friends d'inmu nan sai su shiga"
Tace to, ta juya tayi ciki da sauri don kiransu.
Ba'a d'auki tsawon lokaci ba aka fara tafiya wajen dinner d'in, motar da aka shiga da ango da amarya babu kowa sai su kad'ai a ciki.
Khaleel ya kalli Hanifah yayi gyaran murya yace.
"Wannan kallon fa, yarinyar nan naga kamar kinfini zak'ewa ko?"
Ba shiri ta kalle shi, ta kuwa dank'ara masa harara ta kauda kanta. Ya rankwafo saitin kunnenta kamar yana mata rad'a yace.
"Gaskiya kin iya kallon love Hanifah, kinga yadda idanunki ke juyi kuwa"
Ta k'ule da maganganunsa wato yama raina mata hankali.
Haka suka isa wurin babu abinda Khaleel keyi sai tsokanar Hanifah, ita kuwa ko uhm ta dena cewa.
Wurin ya gauraye da hasken fitilu masu kyan gaske, motar da amarya da angon ke ciki ta tsaya, kafin su fito sai da suka yi minti biyu sannan Saif ya basu umarnin fitowa, tun daga bakin mota aka fara d'aukar su hoto da wayoyin flash, banda mai hoto da aka d'auko musamman domin d'aukar hotuna.
K'awaye masu anko suka fara shiga, sannan ango ya shigo shida amaryarsa cikin hall d'in.

Aka fara bud'e taron da addu'a, sannan Saif ya fito ya fara fad'in tarihin ango, kasancewar tsayin rayuwar Khaleel bashida wani aboki da zai kira da sunan amininsa sama da Saif, ya zayyano makarantar da yayi, tun daga nursery, primary da kuma secondary, da abinda ya karanta.
Ya gangaro da fad'in amarya da ango rainon gida ne, sannan shine mutum na farko da ta fara yi ma tumbud'i, aka k'yalk'yale da dariya.
Sam bai damu da dariyar ba ya cigaba da cewa.
"Akwai wata rana zamu tafi sallar juma'a ya d'auke ta yana mata wasa, kawai ta feso masa fitsari a fuska da jikinsa gaba d'aya, bata tsaya a nan ba kashi ya biyo baya, a wannan ranar sai da muka makara zuwa sallar juma'a don sai da ya sake wanka..."
Aka sake kwashewa da dariya.
Nan Saif ya cigaba da zayyano musu abubuwan da Hanifah tayi wa Khaleel d'in tana baby, Hanifah ta k'ule, kamar ta fashe.
Bayan ya kammala ya wuce ya samu wuri ya zauna, aka kira wata y'ar ajin su Hanifah a makaranta kuma k'awarta mai suna Sadiya, itama ta bada tarihin amarya da makarantar da tayi da sauransu. Ta kammala tayi addu'a ta koma mazauninta.
Bayan nan, aka fara ciye ciye da shaye shaye (abinci, drinks da sauransu), amarya da ango basuyi rawa ba sai y'an mata ne suka d'an taka, an dai kirasu akayi musu hotuna ba iyaka wanda za'a sanya a album.
Sai kusan sha biyun dare aka watse kowa ya nufi makwancinsa.
Ranar da k'yar Hanifah ta iya yin baccin kirki.


*******


Washe gari lahadi ba'ayi komai ba sai shirin d'aukar amarya da akeyi, jikin Hanifah duk yayi sanyi har wani zazza6i take ji, idonnan yayi jajir, ga anyi anyi taci abinci tak'i, Ammi har zare mata ido tayi amma tak'i cin komai, sai da Ammi ta had'o mata tea mai kauri ta shigo ta mi'ka mata tace.
"Tashi ki sha"
Ta d'ago daga kwance da take tace
"Na koshi Ammi..."
Ammi ta d'aure fuska ta fara fad'a
"Kar fa ki maida mu sakarkarin banza mana, don ma kinga ana lala6a kisha shine zaki fara yi mata mutane rainin hankali, aure kanki farau ne? Dama tun kafin kiga 6acin raina ki tashi kisha"
Hanifah ta fashe da kuka
Anty Ikilima (matar yayan Ammi) ta k'araso tace
"Don Allah kiyi mata a hankali, dama dole hankalinta ya tashi baki gani za'a raba ta da gida ne?"
Ammi tace
"To ita kad'ai ta ta6a yin aure a duniya?"
Anty Ikilima ta kalli Hanifah tace
"Y'ata tashi kisha kinji"
Ta'ki tashi ma k'ara tura kanta cikin pilo da tayi. Ammi ta kalli Anty Ikilima tace
"Kin dai gani ko? Yarinyar nan ta raina ma mutane hankali wallahi, ke kika sani idan kinga dama kar kisha ki zauna da yunwa, ai cikinki ne"
Daga haka tasa kai ta fice daga d'akin, Anty Ikilima ta kwanta da murya tayi ta lallashinta, da k'yar dai tasha rabin kofi, sannan kuma ta matsa matabdole ta tashi ta shiga wanka, a yayinda su Sadiya da sauran y'an uwa suka tashi suka fara harhad'a ma Hanifah sauran kayanta cikin akwati.


*******

Da yamma Ammi da kanta ta shirya Hanifah cikin atamfa d'inkin riga da skirt kalar green da dark pink, aka d'auko ALKYABBA aka sa sanya mata, a d'akinta Ammi tayi mata nasiha mai ratsa jini da zuciya, kuka kawai takeyi kamar ana zare mata rai.
K'arfe biyar daidai aka fito da ita daga d'akin Ammi wanda da k'yar aka 6an6are ta daga jikin Ammi, y'an rakiyar Amarya suka fito wad'anda mutane k'alilan ne sauran wad'anda basuje ba sai daga baya zasu je.
A mota ma kuka take sosai, Anty Ikilima sai Anty Hassan (itama matar brother d'in Ammi ce) suke gefen Hanifah suna aikin rarrashi har aka iso gidan.
Anty Hassana ce ta kamo hannunta ta fito da ita daga motar sannan ta sanya ta tayi bismillah, ta shiga gidan da k'afar dama...



MSB✍🏼