Monday 20 February 2017

KHALELL Page 25&26

πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€

           πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️
   ♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€♥️πŸŒ€





©PERFECT WRITERS FORUM
              (P.W.F)❤️

           
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
                  *KHALEEL*
               πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€


Written by Maryam S bello {MSB}✍🏻


http://MaryamSBello.blogspot.com


 February 2017πŸ’Ž


              PAGE


✍🏻✍🏻25&26✍🏻✍🏻


Kai kawo yakeyi tsakanin dakinsa, abokinsa dake tsaye mai suna Fahad yace masa.
"Wai lafiya Deen? Meye haka?"
Ya dan dakata, sannan ya dunk'ule hannunsa ya naushi dayan yace.
"Ina yarinyar dana baka labari kwanaki?"
Fahad yace
"Wa kenan?"
Deen yace
"Yarinyar nan mana me sunanta ma?"
Ya dan tsaya kamar mai tunani, can kuma da sauri yace
"Hanifah!"
Fahad yace
"Oh! Nagane ta budurwarka da yayanta yayi maka duka saboda ka..."
Deen na huci yace
"Ya isa! Kar ka tuna min da mutumin nan, kasan me naji?"
Yace
"A'ah"
Deen yace
"Aure zatayi mana, yarinyar nan ni ta yaudara haka? Lallai batasan ko waye Zaharadeen ba"
Fahad yayi saurin katse sa.
"Yaudara kuma? Kana da bakin kiran wasu mayaudara, indai haka ne to kai me za'a kira ka kenan? Mata nawa ka yaudara? Mata nawa ka nuna kana sonsu daga baya ka yaudare su? Wallahi Deen kaji tsoron Allah, nasha fada maka hakan da kake bashida kyau..."
Deen yayi saurin daga masa hannu
"Da Allah dakata Fahad! Sheyasa ban cika sanya ka cikin harkoki na ba, da an fara magana sai ka sanyo min wa'azi, to dama kai nake tsoro ne da zakace min naji tsoron Allah, sheyasa nakeson Tboy da yana nan da ya bani shawara mai kyau, amma ba irin taka ba..."
Ya karasa yana huci da ka ganshi kaga tantirin dan duniya!
Fahad yayi murmushi mai ciwo yace
"Allah sarki! Ay daman nasan zakace haka, to kasani tunda ina tare da kai dole idan kayi ba daidai ba na fada maka gaskiya komai nacinta kana jina ko?"
Deen yace
"To baza'a dauki gaskiyar ba, idan ka isa ka sani naji, kuma wallahi kaj na rantse ko? To Sai na koya ma Hanifah hankali, da na fara nasara da cin ma burina akanta, amma lokaci guda 'dan iskan mijin da zata aura ya wargaza min plan dina"
Fahad abin ma ya bashi dariya saboda inda sabo sun saba haka dashi, indai akan gaskiya ne to Deen baji yake ba, amma tunda yana so Deen din ya shiryu sheyasa yake jure duk wani wulak'anci da zeyi masa. Don haka sai ya dafa Deen 'din yace
"Deen ka rabu da Hanifah, tunda dama bada niyyar aurenta ka fara nemanta ba, inda ma aurenta zakayi da sauki, wanda yake son aurenta zai aureta, it's high time ka nutsu, kaifa ba k'aramin yaro bane ba, yau da ace Abbanka nada rai da nasan bazaka dinga yin irin wadannan abubuwan ba..."
Deen ya furzar da iska da k'arfi yace.
"Fahad ya isa haka mana! Naji keep your wa'azi with you, am not interested, zan je na nemi Tboy shi ka'dai ne yasan shawarar da zai bani, amma kai kam banida lokacinka"
Daga haka ya fice tare da banko k'ofar dakin garam!
Fahad yayi murmushi yace
"Bazan gaji ba, insha Allah zaka dawo hanya madaidaiciya, Allah kabani ikon k'ara jurewa"
Yana fa'din haka ya fice daga d'akin yabi bayan Deen.



********


Wata ranar asabar da daddare duk suna zaune a palo ana kallo, Ammi ta mi'ke don ta fara jin bacci tace musu zata shiga d'aki ta kwanta.
Wurin ya rage daga Hanifah sai Khaleel, Khaleel ya kalli Hanifah yace
"Ya kamata ki rubuto abubuwan da kike buk'ata na hidimar biki ki bani, kinga lokacin sai matsowa yakeyi"
Tayi shiru, yace
"Wai badake nake magana?"
Tace
"Uhm"
Yace
"Ki ansa ni ba uhm ba"
Tace
"Ai naji kuma zan rubuto"
Yace
"Better, kiyi da wuri don ina so na fara rage abubuwa"
Ta kauda kanta zuwa kallon da takeyi. Cikin ranta tace
~<<"kai hidimar biki ta shafa sai wani rawar kai kakeyi">>~
Yayi murmushi yace
"Hanifah bani ruwa nasha please"
Wayyo kamar ta k'wala ihu takeji, mutumin nan ya takura mata a rayuwa.
Ya tamke fuska yace
"Dake fa nake"
Ta mike tana k'unk'uni, ta hade fuska kamar bata ta6a dariya ba, ta fice daga palon. Kitchen taje ta dauko masa ruwan roba na Swan da kofin glass, tana zuwa ta dire masa tayi hanyar waje sai wani cika take tana batsewa, k'iris ya rage ta fashe.
Sunanta ya kira, bata juyo ba amma ta dakata alamun taji kenan. Yayi dariya k'asa k'asa, sai kuma yayi saurin d'aure fuska yace.
"Dawo ki zuba min"
Tayi shiru still tana tsayen da take. Ya ce da dan k'arfi
"Ki dawo nace ki zuba min...!"
Ta dawo ta durk'kusa ta shiga bude ruwan. Kallonta yayi yanda idanunta suka kawo ruwa, sai kuma ta basa tausayi a ransa yace
"I'm sorry Hanifah, but i really have to do this, idan ba haka ba bazamu daidaita ba"
Saukar wani abu yaji a fiskansa daidai wurin hancinsa, ya runtse idanunsa, sai kuma ya bu'de, Hanifah ce tsaye tana 'kyal'kyaltar dariya. A razane yace
"Meye haka kika watsa min a fuska Hanifah?"
Ta dan 'daure tace
"Miyau na mana, wannan shine tukuicin k'aunar ka a gareni, wannan yana daga cikin abubuwan dana tanadar maka muddin ka bari mukayi aure, zaka wahala ne"
Yayi dariya
"Kina tunanin don kin sa min miyanki shine zanji haushi? Never Hanifah"
Sai kuma ya mi'ke tsaye yana fuskantarta.
"Son da nake miki bazai ta6a sa inji k'yamar miyanki ba baby, na gode da kika sa min ya k'ara min son da nake miki fiye da baya, kuma hakan ya k'ara min k'warin gwiwar cigaba da jiran ranar da zan mallake ki baby na"
Ta d'aure fuska a ranta tace
~<<"Maye kawai, naso yaji haushi gashi banyi nasara ba"~>>
Yayi murmushi yace
"Bari kiga wani abin mamaki"
Ya juya yayi dariya sanann ya juyo tare da watsa mata miyau a fuska, ita nata daidai bakinta, ta fasa ihu, ta shiga gogewa iya k'arfinta, ya kalle ta yace
"Gudumuwata ce nima, i love you so much Hanifah"
Yana gama fa'dan haka ya wuce yana murmushi yana fa'din.
"Hanifah kenan"
Ita kuwa da gudu tayi da'kinta tana kuka, toilet ta fad'a ta shiga wanke fuskarta ta soaps masu k'amshin dadi, a ranar da k'yar ta ta kasa bacci, data rufe ido sai ta tuna, wani irin haushi da tsanar Khaleel suka k'ara dirar mata lokaci daya, sannan kuma ta hau tunanin next move d'inta, ta mi'ke zaune daga kwancen da take tace
"Wallahi sai na rama don bazakaci bulus ba, sai na maka wanda yafi nawa!"


Kuyi hak'uri da wannan banda charge sai kuma anjima insha Allah....!❤️😌

MSB✍🏼

No comments: