Saturday 15 June 2019

FAWZAN KO ADEEL PAGE 101

πŸ’„Fawzan ko Adeel?πŸ’


  Written by MSB✍🏻
Story by Maryam Sb (MSB) πŸ˜˜πŸ’•    


πŸ‘„πŸ’‹  



   Page 101  



In banda kyarma ba abinda hannun Fawzan keyi bisa steering wheel a lokacin da yake speeding zuwa Ceder Crest Hospital, jikinshi har shaking yakeyi gaskiya tashin hankali baida dadi gashi Samha duk ta kara  ruda shi da kukanta wadda ta hada kai da gwiwa tana gunjin kuka. “Samha... Habibty ki daina kuka kinji? Just pray for her insha Allah komai zaizo da sauki” cikin kuka tace “Don’t talk! Just drive!” Kara wuta yayi sadda ya cije lips dinsa.  Suna isa asibitin yayi kwana yana neman wurin parking, ba tare da ya tsaya gaba daya ba Samha ta bude motar ta fita a guje cikin kofar entrance din. Gudu gudu ya bita shima ya samu receptionist din ya tambayeta ina zasuyi ta nuna masu hanyar waiting area. Hannun Samha ya damko wanda take numfashi sama sama tana hawaye hannunta duk zufa in banda kyarma babu abinda takeyi, fizge hannunta tayi sadda ta hango mom dinta, tana zuwa tayi hugging mom inda wurin ya dauka da koke koken mutane. Muskutawa Fawzan yayi  “Mom ina kwana?” Gyada kai tayi tana murmushi, kwayar idonta ta cika dam da hawaye idonta yayi ja ya kumbura har idanun sun kankance. Samha na kan kafadunta tana kuka, gefen Adnan mijin Hilwa ya koma ya zauna bisa wata kujerar shaking hannu sukayi Fawzan yace “Assalamu Alaikum” “Wa’alaikumusalam” “Ya mai jiki?” “Alhamdulillah” “Allah bata lafiya” “Ameen ameen”  Suna gama gaisawa Areef da matarsa suka shigo. Fawzan watched the family wept for Hilwa, in banda koke ba abinda ke tashi wurin, Amal kuwa ta raku6e bisa kujera tana ta kuka gashi ba abinda zai iya yi even for his Habibty. Hannunta yake kokarin kamowa ya maido kusa dashi taqi sai ma kukanta dake karuwa.  12:45pm   Yanzu anyi awa uku tunda aka sanar dasu Samha wannan bad news din.  Adnan, Fawzan da Areef ne suka dawo daga mosque, ba kowa wurin sai Samha da Amal suna zaune tare sunyi jugum jugum, yana zuwa ya kamo hannunta ta mike tsaye, can wata kujera nesa da su Amal suka koma ya kwantar da kanta bisa kafadarsa yana rike da hannunta.  “Kinyi sallah?” Ta gyada kai alamun eh “Fawzan I hope they will be ok?” Kara matse ta yayi a jikinsa “Insha Allah, just keep praying ok?” Ta gyada kai tana kara shigewa cikin jikinsa.  Fawzan ya kewaya da kwayar idonsa su kadai ne family a wurin, juyowa yayi ya kalli Samha gani yayi tana ta addu’a praying for her sister, mom tana mosque itada Sadiya, Amal tace tana hutun sallah while Samha ta riga kowa tashi tayi tata sallan.   Hours past and there’s no sign of any doctor,  Samha da Amal suna bacci da alamar kukan da sukayi ne ya bugar dasu, sallama driver dinsu Samha yayi ya ajiye masu baskets din abinci, ya masu ya mai jiki Sannan ya fita.  A hankali yake tashin Samha ta mitsika ido tana kalle kalle “Zakici abinci?” Ta girgiza kai “I don’t have any appetite” “You need to eat something please Samha” Ta zum6uro baki “Ok I want kebab and milkshake” He nodded “Anyone else need anything?” “I want a kebab too” Amal tace tana tashi zaune Nan kowa ya fadi abinda yake so Fawzan ya tashi yana murmushi, wajen asibitin yaji muryar Samha “Fawzan wait!” Ya dakata yana kallonta tana karasowa  “Pick me!”  Murmushi yayi tare da wrapping hannunsa around her waist ya daga ta sama yana kallon cikin idonta. “Allah ya tsare Habiby” tace tana kissing kumatunsa Dan murmushi yayi yana direta kasa “Insha Allah Habibty” Juyawa tayi ta tsaya bakin kofa tana kallonaa har sai da ya fita daga gate sannan ta koma cikin asibitin. Wuraren 5:30 ya dawo hannunsa dauke da ledoji kala kala yanayin wurin was still sad, ajiye kayan yayi kasa gefen Samha ya gaida mom da Amal da Samha da suka saka a tsakiya ko wace ta dora kanta bisa kafardarta daya. “Mom ina wuni? Ya mai jiki?” “Ahh Fawzan, lafiya lau Alhamdulillah” “May Allah grant her Shifaa” “Ameen ya Allah” “Tashi yayi ya koma wata kujerar dan nesa ya zauna “Samha tashi ki koma wurin mijinki” Mom ce tace ma Samha Tashi tayi a kunyace ta koma inda Fawzan yake ta zauna ya kamo hannu yana murzawa a hankali “How are you?”  “Am ok, you?”  “Am good... I forgot to tell you the decision Abba made, I mean hukuncin da yanke ma Aliyah da Shatu” Ta gyara zama da sauri “Ya akayi ya sani? Kai ka fada masa?” “Nooo, kinsan bayan na sauke ki school na biya ta gida to greeted him na fito zan tafi gida naji tana waya da Shatu, that’s when na shiga dakin and dealt with her shi kuma Abba I think yaji hayaniya ne yazo while ta haka yasani, then ya yanke masu hukuncin auren Friend dinsa wani Alhaji Buba, kuma tare za’ayi masu auren I mean zasu auri miji daya” “Wow! I think hukuncin nan ya masu daidai, I will tell my mom Allah ya kyauta gaba” “Ameen” Hango Adnan sukayi gaban kofa at the far end, sai yanzu ma suka lura da jinin dake jikinsa Inaga while picking her up ne, gaba daya suka mike suka nufa inda yake Samha tace “How’s she?” “Tana under operation yanzu”  “Kana gidan abin ya faru ne?” Fawzan ya tambaya “Yes naje kai mata wasu kaya gida, sai taje ta kai kayan sama ni kuma ina jiranta kawai tana dawowa sai dai naji ihunta ashe tayi tumbling ta fado kasa she was wet in blood, nan su mom suka fito while I picked her up muka nufi asibiti, she was unconscious da muka kawo ta” “Me doctors din sukace about the baby?” Mom ta tambaya “Daman abinda nazo sanar daku kenan”  Gabansu ya yanke ya fadi, zufa ta keto masu addu’a suke Allah yasa they will both be ok. “Alhamdulillah! Hilwa and I are proud parents of two handsome boys!” Take wurin ya kaure da murna da hayaniya as everyone gets happy and excited.  “Wait.... two? You means twins!? Amma meyasa baku fada mana ba?” “We wanted it to be a surprise” yayi murmushi Hugging Amal Samha tayi as they all thank Allah. Adnan ya koma ciki can ya dawo ya sanar dasu an fiddo ta daga theatre and she was fine alhamdulillah with only a broken arm and ciwo a goshinta.  “Time to go meet my nephews Anty Samha!” Ta fada tana murmushi as they walk to where the babies are.             God bless y’ll! πŸ’•

No comments: