Friday 14 June 2019

FAWZAN KO ADEEL PAGE 71-72

πŸ’„Fawzan ko Adeel?πŸ’

Written by MSB✍🏻
Story by Maryam Sb (MSB) πŸ˜˜πŸ’•

πŸ‘„πŸ’‹


Page 71-72


Kallonshi take daga sama har kasa tace
“Daman na fada maka a baya, I said you’ll pay for all the pains you’ve caused me! Toh gashi nan am fulfilling my promises kamar yadda nace! And yes! Nice kalleni da kyau kagani, am fit and fine, kalleni ka kara kallona, Aliyu Haidar yau inaji duk duniya ba wanda ya kaini farin ciki, ganinka a nan kadai ya sanyaya mun rai, am damn happy! You’re either gonna rot in jail for the rest of your life, or die don haka ka tuba ka koma ga Allah ka fara izgifar tun yanzu, saboda kai kam karshenka yazo, so RIP in advance Aliyu Haidar this is just the beginning of your destruction! You’re  nothing but a monster, na tsaneka with a every fiber of my being, ka cuce ni ka cuci rayuwarta, ko da yake I don’t blame you at all, I blame myself for trusting you in the first place, I should have never trusted you Aliyu Haidar, but bakomai kaddara ce kuma na kar6a hannu biyu-biyu, yawan yan matan daka kashe, da kuma wadanda ka aura ka cuci rayuwarsu kasani Allah baya bacci kuma shi ba azzalumin bawa bane ba, tun a nan duniya zaka fara ganin sakayya kafin kaje ka iske na lahira....!”

Daka mata tsawa yayi gamida da bugun karfen cell din, idanunshi sun kada sunyi ja
“Samha! Ya ishe ki haka! Kar don kinganni a nan kiyi tunanin you won, ina nan dake a court zaki gani we will win and you’ll lose, Aliyu Haidar never loses not this time around”

“Karya kakeyi! You already lost muna nan dakai a court mu zamuyi wining case dinnan saboda mun rike gaskiya...”

“Mu zuba ni dake! Zaki sha mamaki”

“Aliyu Haidar yawan kudin da zaku kashe bai isa ya take gaskiya ba, Allah yana bayan mai gaskiya bawai makaryaci ba”

“Yafa ishe ki!”

“Bai isheni ba” tace sending him a deadly glare!

Shiru yayi yana kallonta kamar zai dake ta, tayi murmushi
“Am done with you insha Allah, na kuma fada maka abinda ke mind dina now I can have peace of mind! Allah ka dade tsare mu daga fadawa hannun irinku”
Tana gama fadin haka ta kama hanya ta fita ta bar shi yana cigaba da dukan karfen cell din.

“Am gonna kill you Samha! I swear!”

Daka mashi tsawa akayi
“Bafa gidanku kake ba don haka kayi wa mutane shiru a nan!”

*****

Wani katon shopping mall suka tsaya suka shiga ciki, mom ce ta umarci kowa ya dauki abinda yakeso while suka ke6e itada Amal tana fadi mata wani abu, gyada kai tayi tana murmushi, Samha na kallonta ta shiga lift ta dan juma can ta dawo hannunta niqi niqi da manyan ledoji, direct mota ta wuce ta ajiye, Mom ce tace ma Samha ta daukar ma Adeel
Kaya masu kyau da Shatu da Saudat, nan sukayita za6a da takalma, bayan sun gama suka wuce gida.

Tun daga waje Amal ta cire dankwalinta ta daure ma Samha idanu
“Meye haka?”
“Shushh” Amal tace tana kamo hannunta suka fito daga motar, dragging dinta upstairs tayi.
“Wai meke faruwa?... Amaaaal!”
“Ya Samha mana! Kiyi shiru kawai”
Suna shiga daki tayi dragging dinta bathroom ta rufe da key
“Kiyi wanka ina jiranki a nan!”
“Amal why? Ki bude kofannan! Idan na fito zaki sani ne”
“Naji” tace cikin dariya
Hilwa ce ta shigo dakin a gajiye ta dire ledoji kan gado, ta zauna tare da cire gyalenta
“Whew! Na gaji”
“Sannu” Amal tace tana fiddo makeup kit dinta tana budewa.
Knocking Samha tayi da karfi Amal ta bude mata.
“Oya shafa mai sharp sharp!”
Harara ta mata sannan ta shafa mai, tana gamawa Amal ta zaunar da ita kan stool tana facing dressing mirror.
“Amal badai makeup zaki mun ba? And you know me I hate makeup”
“Ya Samha Please, light makeup zan maki fa kawai...”
Folding hannuwanta tayi tana mai daure face tamau
“No”
“Don Allah fa nace”
Ajiyar zuciya tayi tana rolling eyes nata
“Alright very very light makeup...”
“Tam zan maki light makeup wallahi”
Ba yadda ta iya haka Amal ta cigaba da mata kwalliya, shafa wancan, goga wancan, goge wancan, har aka gama it takes forever takeji ta tsani kwalliya.
“Please na gaji Amal ya isa haka”
“Saura kadan, just wait a little while I promise yanzu zan gama”
Haka nan ta tsaya aka karasa, Amal tayi ihu
“Wow! Kalli kanki a mirror”
Bude ido tayi ta kalli kanta, ware ido tayi tace
“Who’s this Amal?”
Amal da Hilwa suka sa dariya
“It’s Khadija Ahmad, you look fabulous! Gorgeous! Stunning! No amount of words to describe how beautiful you look”
“What’s with all this makeup?”
Hilwa ta bude ledan tabdauko wata doguwar riga black and red mai matukar kyau.
“Wear this”
Ta kallesu da mamaki
“Why?”
“Omg! Just wear it pls! No more questions!”
Kimtsawa tayi ta saka, it was a beautiful silky gown sai jelar baya red color, wata danqareriyar flower ce red color a daidai saman gefen kafada, bude baki sukayi suna kallonta. Gashinta aka mata coiling da comb, red hular ribbon aka sa mata.
Ta kallesu with a confuse look
“Meke faruwa wai?”
“Shush” Hilwa tace ta zaunar da ita kan gado, tana kallo suka shiga shiryawa... Amal pink gown ta sa, While Hilwa ta sa wata blue maternity gown.
Kamo hannunta sukayi suka soma saukowa downstairs. Gidan decorating akayi da balloons ansaka /Welcome home/, music ke tashi a hankali. Tsayawa tayi tana kallon gidan tace
“Wow, all this for me?”
“Ya Samha mun hada maki wannan dan family get together ne just to show how happy we’re to have you back home with us...”
“Awwn, thank you, it means alot wallahi”
Saukowa sukayi downstairs, cousins dinsu ne maza sunyi group suna playing FIFA video game while yan matan suna zaune suna kallo. Kasa katon kwalin pizza ne suna ci suna playing games.
“Wow you all came? Am so happy!” Samha tace feeling happy, hango Adeel tayi zaune kasa yayi folding kafafunsa, sanye yake da red shirt da black jeans, ware ido tayi ganin yadda yayi shiga sai ka rantse bai ta6a zaman kauye ba, he looked exactly like Fawzan now, no wonder kayan da ta siyo masa ya sa, karasawa tayi ta zauna gefensa, juyowa yayi suka hada ido ya ware ido cike da mamaki, ta masa kyau sosai.
“No! Wallahi bazamu yarda ba!” Amna tace tana take kafafun Ayman (da dad da dad dinsu uwa daya uba daya suke) Yasir da Ayman ne ke playing two players, while Adeel na zaune kawai yana kallo yana cin pizza yana shan maltina.
“Yes you guys have been playing FIFA since morning! Gaskiya we wanna watch movie too” Siddiqa tace tana watsa ma Ayman da mugun kallo
“Me too” Hilwa tace tana gyara zamanta kan kujera
Nan hayaniya ta qaure mazan da matan suka fara gardama matan movie mazan ball.
“Agghhh!” Samha tace tare da toshe kunnuwanta da karfi sannan ta tashi da sauri ta bar parlor din.
“Wai sai yaushe zaki zo?” Amal tace tana waya
“Am on my way yanzu haka”
“Alright tohm”
Knocking akayi Amal ta bude pizzan da suka kara ordering ne aka kawo ta kar6a ta kai parlor.
Kitchen ta leka Sadiya ta gani tana fitar da cupcakes daga oven, while Shatu na gyara kitchen din da yayi kaca kaca, mom kuma tana shredding chicken cikin wani dan plate. Gaisawa sukayi da Sadiya ta masu sannu zata kama masu aikin Sadiya ta hana ta da sauri, nan suka fara jayayya da kyar ta hakura ta koma parlor inda suke game din, har yanzu basu bar gardamar ba, ba wanda ya lura da ita, komawa kitchen tayi ta shiga kai coolers dining tana arranging wurin.
Tana gamawa suka ji karar doorbell taje ta bude

“Yasmin!”
“Samha!”

Suka fadi a tare, take sukayi jumping tare da hugging juna

(Ya Allah I missed this naughty girl!)

Janyewa sukayi daga hugging din

Kamo hannunta Samha tayi
“Muje ciki”

“Not so soon...!”
Juyowa sukayi a tare, Samha ta tsaya tana kallonta baki sake can tace cike da mamaki
“Aliya...!?”
Tana kallonta daga sama har kasa. Matsatsun kaya ne jikinta wata peach fitted gown na silky material, sanye take da baqin glass, sai kanta tayi rolling karamin peach gyale bakinta chewing-gum ne tana tauna ji kake qas qas qas!
“Yes it’s me Aliya”
Samha ta qaqalo murmushin dole
“Toh shigo ciki Bismillah”
Daga mata hannu tayi
“Ba zama ya kawo ni ba, ina so ki shiga ciki ki kira mun Fawzan yanzu, naga kuna ta 6oye shi toh na ganshi dazu a shopping mall, please kice masa his cousin Aliya tana kiransa...”


Hahahaha! Who remember Aliya? Well she’s back πŸ˜‰ Who’s ready for this?

No comments: