Friday 14 June 2019

FAWZAN KO ADEEL PAGE 49-50

πŸ’„Fawzan ko Adeel?πŸ’  


Written by MSB✍🏻
Story by Maryam Sb (MSB) πŸ˜˜πŸ’•    

πŸ‘„πŸ’‹    


Page 49-50  


Gudu yake kamar zai tashi sama, dukan sitire yake kamar mahaukaci yana magana shi kadai.  “Oh shit!”  His face was red! Idanunsa sun kada sunyi jawur. Wayarshi ya dauko ya danna kira  “John any news?”  “No not yet, we’re still searching for them”  “I don’t want excuses John! Just bring them back to me, remember I said dead or alive I don’t care, I just want them back, understood!?”  “We’ll try our best...”  “No don’t try just do it!”  “O..kay sir”  “Good”  Jefar da wayar yayi karkashin seat yana cigaba da driving yana kalle kalle, amma ko masu kama dasu bai gani ba.  “Samha you little brat! How could you escape? I just have to find you no matter what! I see you’re clever hun? If I catch you I promise to teach a very valuable lesson!”   Haka ya cigaba da driving yana zagaye unguwar har dai ya fita daga unguwar gaba daya. Duk bayan second 30 sai ya kira John yaji yaya, amma sai John yace masa basu gansu ba, duk yabi ya rude kamar wani mahaukaci, yadda yake driving sai kayi tunanin titin zai 6alla. Har yana neman bige mutane...    ~~~~~~~~  A 6angaren su Samha kuwa tunda suka fito suke gudu, sunyi nisa sosai inda suka gaji har basu iya cigaba da gudun, zama sukayi shakaf kasa suna maida numfashi.  “Samha tashi kar su iso kinga ko titi bamu kai ba, mu karasa mu nemi taimakon lift”   Samha na maida numfashi tace  “Wallahi wannan gardawan suna bayanmu, am scared Saudat I think munyi saurin guduwa”  “Tunda mun riga da mun gudo tashi mu cigaba daga inda muka tsaya”  Tun kafin su tashi hadari ya soma haduwa, kafin kace me garin yayi bakikirin iska sai kadawa yakeyi, wani irin mugun iska ya tashi, nan Samha suka mike suka cigaba da tafiya iska na kada su kamar zai kada su kasa, sanyi sai ratsa su yakeyi kasancewar sun ma manta ko mayafi su dauko tsabar rudu dankwali ne kadai kansu, maqe hannu sukeyi suna kyarma sai kalle kalle sukeyi a tsorace, sai yanzu ta lura unguwar ba gidaje ya akayi ma aka kawo ta wannan unguwar haka?   Yayyafi aka soma yi nan suka fara gudu ruwa na sauka kansu kadan kadan, nan da nan aka 6alle da ruwan kamar da bakin kwarya, haka suka karasa titi kasancewar kowa sauri yakeyi bamai sauraren su koda sun tsaida neman taimako.  “Kinga Saudat mutanen nan bazasu tsaya ba daman kizo mu cigaba da gudun kawai”  “Samha sanyi nakeji!”  “Nima haka, mu daure kawai kar mutanen su iske mu”  Kokarin 6oye wayar Samha keyi inda Saudat ke boye camera din hannunta kar ruwa ya jikesu.   Gudu suka soma ba kakkautawa har takalmin Samha ya katse, wurgar dashi tayi ta cigaba da gudu kamar zasu tashi sama.  Sunyi nisa har basu san ina suke bama, suka juya sukaga sun bar kan titi sun shiga dokar daji.  “Samha nifa bansan kan garinnan ba ina muke ne?”  Samha ta zagaya da kwayar idonta ga duhu ga ruwa anayi sosai ta girgiza kanta alamun a’a  “A gaskiya ban gane ina muka shigo ba Saudat”  “Toh ay ba tsayawa zamuyi ba cigaba zamuyi”  “Nidai Saudat ko muyi surrender su kama mu kawai?”  “Inji waye? Ay tunda mun bar gidannan kar mu yarda mu koma, tashi kawai mu cigaba kila Allah yasa mu samu mai taimaka mana”  Tashi sukayi da kyar tsabar gajiya suka cigaba da gudu, kamar da wasa suka juyo kamar ana binsu, juyawa sukayi nan suka ga mutum biyu daga cikin guards din na biye dasu.  Kara wuta sukayi sun masu nisa sosai Samha ta saki kara, juyowa Saudat tayi a gigice ta ganta zaune dirshen rike da kafarta, dawowa tayi ta daga kafar nan taga jini na 6ul6ulowa.  “Subhanalillah! Kin taka kwalba Samha ina takalminki?”  “Ya katse shine na wurgar dashi wani wani”  “Samha ya zamuyi yanzu naga alamar suna kusa damu fa mutanen nan”  “Saudat jeki kawai ki karasa mission din, I know you will come back for me no matter what”  “No way Samha! Bazan tafi na barki nan ba, I can’t...”  Kamo hannunta tayi tana hawaye “You can Saudat, complete the mission for us, go to the police station direct narrate everything to them, every single detail don’t left out anything, take my phone and the camera, then come back for me, I cannot walk any further”  Girgiza kanta takeyi “No Samha ki hau bayana mana I can manage”  “Bazaki iya ba Saudat, zaki gaji ne, just hurry up and come back ok?”  Hugging Samha tayi tana kuka “I promise to come back, don’t go anywhere please”  “Idan kin dawo bani nan ki tabbatar sun tafi dani, and you know exactly where to find me right?”  “I know, be careful Samha, I will be right back ok?”  Rike kafan tayi cikin azabar ciwo tace “Be safe Saudat”  Saudat naji nagani ta dauki wayan da camera din tana waigen Samha tana kuka ta tafi da gudu.   Har tafi Samha ta kwala mata kira. Dasauri ta dawo  “Na manta this is my address gashi nan zan maki typing cikin wayana, idan kinje tell my parents everything da halin da muke ciki, I know they will do something about this ok?”  Girgiza kai tayi tana hawaye sannan ta juya da gudu ta tafi...   Rike kafan Samha tayi ta zare kwalban ihu ta sa saboda azaba ta kwanta nan tana maida numfashi ga ruwan saman dake dukanta. Skirt dinta ta yaga ta shiga daure kafan saboda jinin dake kwarara ko ya daina zuba, in banda zogi ba abinda kafan keyi gaba dayanta ciwo takeyi, runtse ido tayi tana jin ciwon kafar na ratsa ta.   Footsteps taji, take ta dinga jan jiki tana matsawa a hankali, maganganu ta dinga ji a kusa da ita.  “Are you sure nan suka yi?”  “Wallahi Sir I saw them ta nan suka bi”  “Keep looking why are you still standing here like a complete idiots!”  “Sorry sir!”  Nan suka shiga dubawa ita ko Samha ta cigaba da jan jiki, gajiya tayi kawai ta bari ta rufe ido saboda ciwon kafa.
Kamar daga sama Samha taji an kwala mata abu a kai, ihu tayi tana ganin kanta na juyi, Haidar ta gani tsaye kanta biyu biyu take ganinsa yana murmushi yana mata bye bye, take duhu ya mamaye ta...   ~~~~~~   A hankali ta bude idanunta, biji biji take gani kafin idon ya bude tas, kanta ya sara mata dubawa tayi ta ganta cikin wani irin daki marar haske mai datti, katifa ce kadai cikin dakin, kallon kanta tayi zaune take kan wata kujera duk an daddaure ta har hannunta a daure bata iya kwakkwaran motsi.  Bakinta an rufe mata dashi da wani kyalle ko A bata iya cewa, kokarin kwace kanta take daga daurin amma ta kasa. Magana takeson yi ba hali  Karar key taji daga waje Haidar ne ya shigo cikin shigar bakaken kaya, guard dinshi ya aje mashi kujera kusa da ita yana mata murmushin mugunta.   “Welcome back honey pie... how are you?”  Kallonshi tayi cike da tsana kamar ta rufe shi da duka.  Ya kyalkyale da dariya yana shafa gefen fuskarta, bakinshi yakai daidai saitin kunnenta yana mata magana cikin rada rada.  “How could you escape from your dearest Aliyu Haidar? Nida ke mutu karaba takalmin kaza my love”  Magana take sonyi cikin tsawa ta kasa.  “Relax baby, am here with you now don’t be scared” yace yana shafa kanta, da karfi ta matsar da kanta tare da runtse ido tana jin tsanar Haidar. Gashin kanta ya damqo da karfi, sannan ya yakice kyallen bakinta ya shiga kissing dinta kamar zai 6alla mata baki, cizo tasa masa da sauri ya matsa yana sosa wurin, bata tsaya nan ba ta watsa masa miyau a fuska, tana kallonsa cikin ido cike da tsana.  “How dare you!? I will teach you a lesson right now!”  Kallon guard din yayi dake tsaye ya masa signal da ido, fita kawai guarda din yayi ba’a juma ba ya dawo da bokiti hannunsa, dire bokitin yayi kasa take Samha taga duk kankara ke ciki manya manya.   Haidar ya duka ya debo ruwan sanyin nan ya daga daidai saitinta ya shiga kwara mata shi, kyarma ta farayi tana ihu, haka ya dinga zuba mata ruwan in banda ihu da kyarma ba abinda Samha keyi, kusan rabin bokitin ya watsa mata, sannan ya dakata, yana kallon yadda take shivering, bakinta ya matse da hannunshi sannan ya take mata kafarta mai ciwo.  Wani irin ihu tasa kamar zata fasa dakin da kara, take suka toshe kunnensu da sauri. Kuka takeyi cikin azabar ciwo tace  Haidar I promise you’ll pay for every single pain you caused me, I promise to destroy you Aliyu Haidar...”  Ya kyalkyale da dariyar mugunta “You say this more than ten times, but har yanzu you didn’t fulfill your promises sweetheart”  “Bazanyi alkawar a banza ba Haidar, I promise you I will...”  “Shafa mata kumatu yakeyi, sannan kuma ya faske ta da wani irin wawan mari. Marinta ya shiga yi amma ta dake tana kallonshi ko motsi batayi ba  “Hit me again! Come on! Hit me! Do it now! Hit me Aliyu Haidar! Now!!!”   Mari ya shiga kai mata hagu da dama amma ko gezau batay ba, sai daya gaji dan kansa ya bari, kyalkyalewa da dariya tayi  “Are you tired already? Come on hit me Aliyu Haidar! Kill me don’t hesitate! Do it now!!” Ta fada cikin mugun tsawa!  Tashi yayi ya fita daga dakin ya banko kofar tare da sa key....           God bless y’ll ❤️❤️❤️u

No comments: