Friday 14 June 2019

FAWZAN KO ADEEL PAGE 21-22

πŸ’„Fawzan ko Adeel?πŸ’

Written by MSB✍🏻
Story by Maryam Sb (MSB) πŸ˜˜πŸ’•

πŸ‘„πŸ’‹

Page 21-22

Oh my God! Don Allah ki tashi Samha bakiso mu gama da wuri ne kam?”
Ta fada tana nade gyalen bakar abayar data sa.

“Uhm?” Tace tana kara jawo bargo zata koma bacci, take Yasmin ta bude mata bargon gaba daya.
Cike da masifa ta mike zata fara magana, Yasmin tace

“Save it for later, but now jekiyi wanka mu tafi registration naji ana cewa akwai lectures karfe 2”

“What the? Karfe nawa yanzu?”

Rolling eyes Yasmin tayi
“9:54”

Salati ta shiga yi sannan ta mike a zabure ta fada toilet, cikin minti goma ta fito da sauri ta shiga shiri, cikin black trouser and black top sai ta dora long soldiers jacket, black gyale tayi rolling kanta dashi ta feshe turare a jikinta, tayi grabbing jakanta.

“Samha we’re going to be late fa” Yasmin tace tana sa takalmanta.

“I can’t go out without eating join me” tace tana cin dankalin dasu Yasmin suka soya.
Girgiza kanta Yasmin tayi ta zauna suka fara cin abincin.

Da sauri sauri sukeci, suna gamawa suka sha ruwa, bincike Samha ta shiga yi cikin akwatinta

“I can’t find dayan earring dina”

“Ki barshi ay ba’a ganin kunnenki” Yasmin tace almost pushing Samha out of the room tare da rufewa da key.

Tsaki Samha taja tati gaba abinta.

Papers na registration suka ciccike suka tafi signing, sun gama saura Deen Samha ta kalli Yasmin

“Ina ne office din Deen din?”

“I don’t know let’s ask”

Wani student suka tambaya nan ya shiga nuna masu. Bama nisa daga inda suke a hankali suke takawa office din nasa.
Knocking sukayi.

“Yes come in”

Tura kofar sukayi
“Assalamu Alaikum”

Ras ras! Gabansa ya fadi, she’s the one ya fada cikin ransa mamaki gami da farin ciki bayyane saman fuskansa, dakewa yayi yace

“How may I help you?”

“Em, good morning sir, we came for signing” Yasmin tace kanta kasa

“New students?”

“Yes Sir”

Karba yayi bayan ya gama yace, make a copy and submit it here

“Yes sir, thanks”

Tunda suka shiga har suka fita Samha bata dago da kanta ba bare ma tayi magana.

Suna fita ya dauki wayansa cike da farin ciki ya kira Sultan
“Am so happy today!”

“Why? What happened?”

“Guess” yace yana mai farin ciki

“You know am not good at this stuffs just say it”

“I saw her again can you believe it!?”

“You mean she? The girl you....?”

“Yes!” Yace almost jumping of happiness

“Wow, ikon Allah kenan, masha Allah congratulations, is she a student here?”

“Yes...! She is... she is coming back to
Submit her papers ”

“What’s your next step then?”

“Zan bi komai a sannu har sai nayi nasara, hope she accepts me”

“She will you are handsome after all”

“I hope so, bye will talk later, regards to my cutie”

“Insha Allah”

Nan ya cigaba da aikinsa cike da farin ciki har suka dawo da sallama. Amsa sallaman yayi, suka shigo. Miko mashi Yasmin tayi ya shiga bi yana duddubawa ko ta hada komai, da ya tabbatar ta hada ya sa mata a file ya ajiye.

“Kawo naki”

Dagowa tayi suka hada ido, take tayi saurin sauke nata, a hankali ta taka wurin table din ta mika masa, adjusting glass dinsa yayi ya shiga dubawa, sunanta ya gani KHADIJA AHMAD. Sunan ya birge shi harda dan murmusawa. Ya dade yana dubawa wanda rabi hankalinsa na kanta.

“Yayi, you can go”

Tafiya sukayi ya bita da kallo har ta fice take ya sauke ajiyar zuciya.

“Kinga abinda nagani?”

“A’ah”

“He’s been staring at you tunda muka shiga”

“Mtss! Please bana son maganar nan, I don’t even believe you Yasmin”

“Am serious ina kallonsa”

Gaba tayi cikin takaici ta bar Yasmin na kwala mata kira...

***

2pm

________

3 hours later...

“Seriously this man isn’t going out? It’s 5 minutes after five” cewar Yasmin a gajiye, 2 hours ya kamata suyi amma har biyar ta wuce

Murmushi Samha tayi ta cigaba da jotting abinda lecturer din ke dictation.

“Sir it’s almost 6” cewar wani student

“God bless him” cewar Yasmin

“You can leave if you want to” lecturer din yace yana cigaba da bayaninsa.

“Yunwa nakeji, thank God munyi breakfast”

“Ai da sauri kikeyi sai da nace ki tsaya muci ba” Samha tace tana rolling eyes.

Tsaki taja kadan ta ciro wayanta ta boye kasan table tana cigaba da chatting dinta.

***

One week later...

“Na shiga uku gardi ya ganni” Zee ce ta shigo da gudu daga ita sai daurin gaba na zani.

“Wayace ki fita half naked?” Cewar Samha tana lalube cikin jakar makarantar Samha

“Me kike nema?”

“Ina wannan geography text book din da kika dauko library?”

“Oh ask Murja”

“Samha mana”

“Check my wardrobe, me xakiyi dashi?”

“Zubarwa zanyi a dustbin” Yasmin tace tana bude wardrobe din Samha

“Eh lallai zaki dawo ki samu naki waje kema”

Tayi rolling eyes dinta, yanzu dai ki tafi kiyi submitting assignment dinki tun kafin Dr Haidar ya hadu dake a class”

“Zo ki rakani mana Yasmin”

“Wa? Sadda mukayi submitting a class meya hanaki?”

“Haba mana Yasmin you know am on my period and having cramps”

“Gaskiya jeki wallahi note zanyi copying kinsan halin dr Gambo and gobe munada class dashi and bayada sauki”

“Ok na tafi amma zan rama wallahi”

“Whatever” tace tana mata gwalo

Samha went straight to his office ba don taso ba, knocking tayi

“Yes come in” yace yana tattara wasu papers wuri daya cikin files.

Sallama tayi cikin yar siririyar muryarta, dago ido yayi ya kalle ta, cak ya tsaya da abinda yakeyi yana kallota....

Thanks for reading πŸ˜‰

No comments: